TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 14

 👭❤ *'YAN UWA NA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____14💎



 Wani irin sarawa yaji kansa yayi saboda munin maganar da yaji mom d'insa tayi, dafe kan nasa yai na kusan minti biyar kafin can muryar ta dake faman masifa tadawo dashi duniyar tunanin daya shiga.


"Nifa nagaji da wannan zaman motar in zaka kaini inda nafad'a maka ka kaini idan kuma ba zakaje ba sai infita in hau napep, kabi duk kawani b'ata rai sai kace karasa wani naka"


"Mom kiji tsoron Allah kidena fad'an mugayen maganganu akan Ummi, wlh Ummi mutuniyar kirki ce batada wata mummunar manufa akanki" 


"To ubana yimun wa'azi!, bari kaji tunkan ahaifeka nake zaune da ita, shin kasan ko saunawa ta salwantar mani da 'ya'ya?, don haka in kasake shiga maganganu na sai ranka ya b'aci"


"Ya salam! Mom duk duniya fa idan tataru bazata iya cutar dakai komai ba sai abunda Allah ya nufa akanka, ina da tabbaci akan Ummi bazata iya salwantar da yaranki ba Allah ne yayi cewa su ba rayayyu bane kuma wannan bazai zamo hujja agareki ba kice zaki salwantar da tata rayuwarta data zuriarta, yin hakan kuskure ne agareki" tsananin b'acin ran abunda yake fad'a yasa ta fita cikin motar had'e da bugo gambun motar da k'arfi, napep tafara k'ok'arin tara tana sabbatu


"Ya zama dole in d'au mataki akanki Aisha, yama za'ayi ace d'ana dana haifa ke k'ok'arin juyamun tunani akanki, inaaa doleni kisan cewa kinyi k'ok'arin shiga gonata" da sauri ya qaraso wajen cikin girmamawa yace


"Kiyi hak'uri mom, idan bakyaso in koma magana shikenan nayi shiru amma kiyi hak'uri ki koma cikin mota lokaci na qurewa" sai da yayi ta mata magiya kafin ya samu ta koma cikin motar tana huci kamar damisa.


'Daya daga cikin gidajen dady dake unguwar igala ya kaita, gida ne mai matuk'ar kyau da tsaruwa, kallon gidan mom tayi sannan ta maida kallonta ga Mahmud dake k'ok'arin bud'e marfin motar ya fita


"Kai a ina ne nan ka kawoni" 


"Gidan dady ne daya gama ginawa las two month ago"


"To sai akayi me?"


"Eh to, dama na kawoki nanne kizauna kafin dady ya sauko daga fushin da yayi"


"Kutumar ubancan! Sai aka cemaka ni banida gidan iyaye, wlh Mahmud kashiga taitayinka"


"Don Allah mom kirufa mana asiri kizauna warki anan, nasan yanda dady yake da sanyin rai bazai wuce kwana d'aya ko biyu ba zai nemi ki koma, kinga daga nan ma sai ki dawo warki nan gaba d'aya tunda dama kin buk'aci araba maku gida ke da Ummi"


"Kaji na rantse maka bazan zauna a wannan gidan ba, wan can gidan dai nake da buk'ata tunda yafi girma kuma ni nake da 'ya'ya masu yawa, idan ma zaka kaini gidan ubana ka kaini don yafi maka"


"Innalillahi wa Inna ilaihirrajiun, wannan wace irin sabuwar rigimar ce kike shirin d'au kowa mom?, kefa kika nemi araba maku gida ba zaki zauna da ita ba, to taya za'ayi kuma kice ita zata fita tabar maki gidan, don Allah mom kicire son kai da yawa"


"Aikin banza, dalla malam ni wuce muje, bazan zauna anan d'in ba"


Shiru yayi kafin ya tayar da motar cikin b'acin rai, da gudu yabar wajen yanajin tamkar ya kurma ihu,


"Eyyeee.. Lallai ka girma da yawa Mahmud, ai sai kayi maza ka kasheni tunda na fad'i son raina" ba tare daya kalli mom d'in ta saba ya rage gudun da yakeyi har suka isa gidan papi wato mahaifin mom.


Tunda suka fita ba wanda ya cewa wani k'anzil, murmushi dady yayi had'e da kallon Ummi data juyar da kanta gefen glass, hannunsa ya d'ora akan nata dake saman cinyarta yana d'an matsawa ahankali, juyowa tayi tana kallon fuskarsa dake fitar da wani annuri saboda murmushin da yakeyi, a hankali ta lumshe idanuwanta, juyar da kanta tasakeyi tana kallon yanda motoci ke wucewa d'aya bayan d'aya, a hankali tafara motsa bakinta lokacin da taji ya sake rumk'e mata hannu sosai


"Maganar gaskiya dadyn yara inajin ba dad'i araina, bana son ganin Babanah a yanayin da na ganesa hakan na matuk'ar tab'a mani zuciya sosai"


A daidai nan dady ya shigo da kan motarsa cikin asibitin, sai da ya daidai ta tsayuwar motarsa sannan ya kalli Ummi


"Rabba'atul bait mun iso" juyowa tayi fuskarta ba walwala


"Wlh bana jin dad'in wannan shurun naka, kanaji nake magana ka shareni"


"To ya kike so nace?, Kiyi hak'uri zamuyi magana anjima kinji ko?" Gad'a masa kai tayi sannan ta bud'e marfin gambun motar tafito, aminity ward ya nufa tana biye dashi har suka iso room 5 in da aka kwantar da Bilkisu... Kwance Ummi ta hango ta bisa gadon jinyar marasa lafiya har lokacin bacci takeyi hankali kwance duk da da zaran ka kalleta zaka gano tana jin jiki sosai,


Da gudu Bilal dake rik'e a hannun ummi ya nufi gadon, Aunty Billy, Aunty Billy kitashi, Aunty Billy me yasa mekine, dady ne ya rik'o hannunsa dake neman ya rik'o hannun Bilkisu,


"Zo nan autana, Auntyn ka bata lpy ne, kayi mata addua kaji" gyad'a kansa yayi had'e da cewa


"Allah yaba Aunty Billy lpy dady, kullum abunda take cemun shine ina Bilal muso juna karka yadda kabarni, dady kace ta tashi nima bana so tabarni" dafa kansa dady yayi had'e da cewa


"Bazata barka ba kuna atare in sha Allah" ahankali Ummi ke shafa kan Bilkisu tana tofa mata addu'ar samun sauk'in rad'ad'in ciwo


 _BISMILLAHI ARK'IK', WALLAHU YASHFIK, MIN KULLI DA'IN MAUDU'I, WAMIN KULLI AINI AU ANI HATIM ALLAHU YASFIK, ALLAHUMMA RABBAN NAS, ASHFI BIL BA'AS, WASHFI ANTASH SHAFI'I LAA SHIFAA'A ILLA SHIFAA'UKA, SHIFA'ALLAHU LAA YUGADIRUSSAK'AMA, AS'ALALLAHUL AZHIM, RABBIL ARSHIL AZHIM AN YASH FIKA/KI_


Sosai Ummi ke maimaita wannan addu'ar tana tofamata, cikin Ikon Allah sai gashi tafara bud'e idanuwanta ahankali, 


"Ummi" ta furta ahankali, murmushi Ummi tayi sannan tace


"Sannu Bilkisu, Allah yabaki lpy" maida idanuwanta tayi ta rufe sannan ta sake bud'e su ahankali hawaye na zubowa daga ciki, k'ok'arin tashi tayi da sauri ta koma had'e da dafe kanta dake d'aure da bandage,


"Washhh..."


"Yi a hankali" Ummi tafad'a tana k'ok'arin gyara mata kwancinta, d'ayan hannunta ta mik'awa Bilal tana yimasa alama da kai da yazo, hannunsa dady ya saki 


Da gudu ya k'ara wajen ta "sannu Aunty Billy, bazaki barni ba ko?" A hankali ta d'aga masa kai hawaye na zubar mata, 


"Eyyee..alhmdulillah my lil sis ta farfad'o" idanunta ta d'ago tana kallon Mahmud dake a bakin k'ofar d'akin yana murmushi, k'arasowa yayi daga ciki tare da jaye Bilal dake rik'e da hannunta


"Jaye daga nan autan Ummi inga lil sis d'ina" kallon dady yayi cikin farincikin ganin 'yar uwarsa ta tashi yace




Post a Comment

0 Comments