TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 24

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_

 

_Jinjina had'e da gaisuwa ta musamman ga dukkanin members d'in *MUSHA KARATU NA..YBK GROUP* hak'ik'a zuciyata na alfahari da kasan cewata atare daku domin kud'in mutane ne masu tsananin karamci da halaccin dake samar da nishad'i atare da ita, fatana Allah ya tsarkake dukkanin gabb'anku ya kuma albarkaci ahalinku, ina so kusani cewa aduk bugun zuciya d'aya nawa d'auke yake da miliyoyin k'aunar ku fisabilillahi❤💘_



💎Page_____24💎



  Zaro idanuwa mom tayi tana mai kallon hajia kilishi sannan ta kwashe da dariya


"Ke 'yar uwa da gaske kikeyi?"


"Hmmm kina wasa wallahi ba itaba hatta shi kansa sai ya zame maki tamkar raqumi da akala, kedai kawai kisha kuruminki, kina zaunenki zakiga aiki da cikawa ba boka ba malam"


"Haka nake so domin naci alwashin salwantar da rayuwar Aisha da zuri'arta saboda na tsaneta fiye da yanda natsani shed'an"


"Hhhh kai k'awata shed'an fa kikace!" hajia kilishi tafad'a had'e da jefa cingum abakinta tana tauna, hannunta tasaka acikin jakarta tafiddo wata 'yar k'aramar kwalba kamar ta turare tamik'awa mom "ungo wannan ruwane aciki da basu wuce 3 drop ba amma sunada tsananin k'arfi, zakiyi amfani dasu kamar sau uku bayan sallar isha'i, zaki samu kad'a kid'an dangalo ruwan kad'an sai kiyi inserting acikin jikinki har na tsawon kwana uku amma ki tabbatar ranar alhajinki zai kusanceki, azahiri wannan kayan ni'imar matane ga duk wanda ya gani amma abad'ini sirrin mallakane mai k'arfi, ina tabbatar maki da cewa matuk'ar kikayi amfani dasu kuma alhajinki ya kusanceki to tabbas babu wata macce da zai koma kallo a matsayin macce aduniya idan ba keba" sake d'auko wata gumba tayi cike da k'aramin d'an bokiti fari irin wanda ake saka turarukkan wuta aciki ta mik'awa mom tace


"Ita kuma wannan gaba d'aya zaki dame kishanyeta, da kanki zaki bani bayanin kyautar da zaki karb'a a wurinsa don duk abunda kikace ya baki to wlh sai ya mallaka makishi"


Zaro idanuwa tayi had'e da cewa "kai dagaske kikeyi?"


"Sosai kuwa kigwada kigani"


"To amma ni k'awata har yanzu banji kintab'o abunda nafi buk'ata ba, matarnan fa tazamo mani tamkar ciwon ido" 


"Kash matsalata dake Hussaina gaggawa, ai kifara mallakar mijin tayanda duk wani tuggu da makirci da zaki had'a mata zai yadda dashi"


"Nifa nafison ayita tak'are, bana son ganinta gaba d'aya agidan" dafa kafad'arta tayi tana dariya


"Kai k'awata wai wannan tsana da kike yimata dame tayi kama? Ki kwantar da hankalinki abu komai a sannu kada garin gaggawa k'aik'ayi yi koma kan mashek'iya, abunda yakamata yanzu kiyi shine kisan yanda zaki jawo hankalin mijinki kibashi hak'uri in yakama har kuka kiyi masa ya maisheki d'akin ki hakan zai taimaka mana wajen yin aikinmu yanda ya kamata, amma kina nan azaune gida bana tunanin aikinmu zai yuyu kin fahimta" Shiru mom tayi tna nazarin magani ganunta sannan tace 


"To shikenan, yanzu kitashi ki watsa ruwa kafin hajia ta k'wallo maki kira"


Basmah kuwa Ummi na shiga d'aki ta kira wata k'awarta awaya, suna gama magana tafita abunta batare da kowa ya sani ba,


A b'angaren Ummi kuwa  bayan ta kammala abincin rana ita da 'yan biyunta wato Batool da Billy ta umurcesu dasu tafi part d'in mom su dubo mata Basmah idan tana can don tunda tagama yimata fad'a tabarta afalo zaune bata sake ganin taba ta d'auka tana d'akinsu kwance amma ga mamakinta koda taduba d'akin bata gane taba gashi har k'arfe biyu ta wuce, tafe suke suna firar breakfast d'in Basmah suna dariya har suka iso part d'in mom nan ma bata ciki saboda part d'inma akulle yake ba kowa aciki nan suka shiga dudduba ta tako ina gefe gefen gidan basu ganeta ba, wajen Ummi suka koma suka fad'a mata bata can, nan take hankalinta yatashi tafita tana duba ko ina a compound d'in gidan ba Basmah ba labarinta, innalillahi wa inna ilaihirrajiun ta dinga fad'a in tayi nan tayi can, wajen maigadi tanufa tana tambayarsa shin ko yaga fitar Basmah, shiru yayi ya kalli yanda hankalin Ummi ya tashi, cike da tausayinta yace


"Tuba nake uwar d'akina banso nafad'a makiba saboda har kud'i aka bani na toshiyar baki, amma ganin yanda kika tada hankalinki zan fad'a maki gaskiya, d'azu ina  anan zaune saiga wata k'awarta tazo ita da wani acikin mota, basu cemun k'alaba ni kuma ban cemasu ba naga ta fiddo wayarta tayi kira, ba'a jima ba saiga  Basmah tafito, shine har ta shiga motar sai tafito ta mik'o mani d'ari biyar tace ko antambayeni naga lokacin data fita ince a'a ya k'are maganar had'e da nunawa Ummi d'ari biyar d'in, ki gafarceni hajia nasan konayi yunk'urin hanata walak'anci zata yimani shiyasa nayi shiru, hawayene suka zubo a idanuwanta da sauri tasa hannu ta shafo bakinta daya kasa furta komai sannan tajuya takoma cikin gida, wayarta tajawo takira Mahmud cike da damuwa tafad'a masa halin da ake ciki, saida ya kwantar mata da hankali sannan ya kashe wayar.


Lambar Basmah ya shiga lalubowa ajerin contact d'insa had'e da danna mata kira, Basmah naganin kiransa amma tak'i d'agawa har sau uku, ganin haka yasa yafita batun kiran yaja motarsa da yake yana wajen abokansa yabar wajen aguje cikin matsananciyar damuwa.


Ita kuwa Basmah dake zaune bisa wata katifa ita da suby k'awarta tayi dariya tana nuna mata gaban wayarta kafin tace


"Kinganshi ko? Sai wani faman kirana yake don ya takuramun, gaba d'aya gidan sun tsaneni, mom d'inmu kad'ai ke sona yanzu kuma bata gidan dadynah ma baidamu dani ba agabansa za'ayi tayi mani fad'a akan d'an k'aramin laifi idan nayi amma bazayace komai ba, hatta k'anwata dake bimun tagujeni taya kike zaton zansamu farinciki agidan?" Murmushi suby tayi sannan tace " ki kwantar da hankalinki anan zaki samu farinciki kawai abunda nake so dake kiyarda dani"


"Taya zan yarda dake suby bacin bakida maganin matsalolina" wata kwalba suby tafiddo ta mik'awa Basmah


"Karb'i wannan kisha da kinsha shi zakiji gaba d'aya matsalolin ki suntafi koba haka ba bab's" tak'are zancen tana kallon saura yin dake gefe yana zuk'ar shisha" cikin maye Bab's yace


"Tabbas haka yake suby, idan kuma bata buk'atar sa, to tasha wannan don yafi k'arfi sosai" ya mik'o mata wata kwalbar dake ajiye acikin kwalaben da suka daza agabansu.


Karb'a Basmah tayi tana yatsina fuska


"Meye wannan Bab's"


"Hhhh Basmah Basmah kenan, wannan shi ake kira da sabuwar duniya kawai kisha zaki tabbatar da abunda nake nufi" har tad'aga kwalbar zata sha  saiga kiran Ummi ya shigo a wayarta, bataso d'aga wayar ba amma saboda tanason yiwa Ummi fitsara tad'aga 


"To kuma meye? Ko fad'anne kika kirani kik'ara yimun" da wuri Ummi tagoge hawayen daya zubo mata a idanu'


"A'a Basmah, kiyi hak'uri kidawo gida, ina kika shigane, kuma waye ya d'aukeki amota?"


"Meye damuwarki aciki, kawai ki ajiye waya"



"Basmah kiji tsoron Allah a duk inda kike kidawo gida, kada kiruguza rayuwarki abanza, kib'ata tarihinki na har abada" tuni kalaman Ummi suka tunzura Basmah ta d'aga kwalbar dake hannunta tashanye abunda keciki tas sannan ta bubbuga kanta da hannu tace  


"Kikace me? To koma mezai faru ai rayuwatace babu abunda ya shafeki aciki don haka sai anjima"  Ummi kuwa tanajin zata katse wayar takama fad'in "hello hello Basmah, Basmah" amma ina tuni takashe wayar tana kallon suby tace


"Kinji 'yar rainin wayon matar nan ko?"


"Kawai ki manta da ita Basmah yanzune zaki samu farincikinki da 'yancin kanki" saida tayi dariya sannan taci gaba dacewa welcome to the new world"




Post a Comment

0 Comments