TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 9

 👭❤ *'YAN UWA NANE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____9💎



 My son ya jikin naka? hope kasamu sauk'i?


"Alhmdulillah dady it's just a little worry dake damuna"


"Being patient my son, in sha Allah komai zai wuce, abunda nakeso dakai shine kaje ka gyaro zamu fita da kai da kuma k'annenka"


"OK dady bari nashiryo" part d'insa ya wuce shi kuma dady yanufi part d'in Small mom, yana shiga ya tadda batool zaune Small mom na gyara mata gashinta shi kuma bassam yana kallon k'wallo gyaran murya yayi bayan ya shigo, cikin gadara Small mom tad'ago kanta tace


"Alhaji kaji tsoron Allah, yanzu abunda kakeyi daidai ne?, ka dubi tun lokacin da kabar part d'innan kanufi part d'in waccan algungumar munafuka ace sai

 yanzu zama fito kusan awa d'ayafa kenan kana can kabiyewa k'ananan yara kuna faman dariya sai kace mahaukata, wlh alhaji baka kyautawa"


Batare da dady ya kalli inda takeba ya k'wallawa basmah kira, da sauri tafito daga cikin bedroom d'inta daga ita sai bes da mini siket kanta babu d'an kwali, dady na kallonta ya d'auke kansa sannan yace


"Ki gyara keda qannenki zamu fita"


"Dady ina zamuje ne?" Kallon ta ya sakeyi cikin jin haushin shigar da take ciki yace


"Idan baza kujeba kwa iyayin zaunenku, shashashar yarinya, bassam maza jeka gyara kafin in fito"


"Dady ban iya gyarawaba momy ke gyarani" bassam ne ya fad'i haka har lokacin hankalinsa na akan TV da yake kallo, tsananin takaici yasa dady juyawa yabar part d'in, dariya basmah tayi had'e da cewa


"Cab wlh mom dady ya iya fitina yanzu, daga tambaya shikenan sai ya rufeni da fad'a, shin waima ina zamu jene?"


"Kema dai kyafad'a basmah! ai kune abokanan fad'ansa amma kar kiso kiji yanda yake k'yak'yata dariya da wud'an can jinin mayu" da sauri batool tace


"Cikamun kai nidai mom, wlh Allah idan bamu gyara da wuriba dady tafiyarsa zaiyi kuma munaji muna gani zai fita dasu billy yabarmu gida kuma nikam da haka tafaru k'ara shegen gashin can na yayyah basmah ya tsittsinke" cikin zafin rai basmah tanufo batool tare da finciko gashin kanta


"Bari nafara tsinke naki gashin kafin nawan da kikeyiwa fatan tsinkewa ya tsinke, muguwar yarinya kawai" nan fa suka kacame da rigima suna faman zagin junansu, ana haka saiga Mahmud ya shigo rik'e da hannun bilal, da gudu bilal yanufi wurin bassam yayinda shi kuma Mahmud ya nufi wajen dasu batool ke rigima yana fad'in


"Ke, ke me kuke yine haka, mom dube su kigani sai kace kaji kuma kinsa masu ido, wlh basmah idan baki cikataba saina zazzaneki agidan nan, wannan wane irin rashin mutuncine, kizauna kina fad'a da k'anwarki?" Turo baki tayi tana fitar da lumfashi dakyar kamar wacce tayi wasar athletic s competition 


"Yaya aradu wannan yarinyar batada kirki, wai ni take yiwa fatan gashina ya tsittsinke don tana marar kunya"


"Keep quite, stupid girl nizan ida cika fatan da take yimaki tunda bakyason zama da head tied, banda iskanci dubi yanda jikinki yake amma har kya iya fitowa ahaka wlh mom gab nake da b'ab'b'alla yarinyar nan, zaku wucene ku shirya ko sai na b'ata maku rai" gwalo batool tayiwa basmah had'e da dariya sannan kowace ta nufi d'akinta har sun wuce ya jawo batool ta baya yace


"Ke ko? idan na rik'aki zaki game kurenki tunda kin zama marar kunya" soko ya sakar mata had'e da tureta da kad'an ta fad'awa mom, da gudu tabar falon shi kuma mom ta jefo masa harara cikin b'acin rai


"My son kamaida hankalinka, wai meyasa kafiye son takurawa Yaran nan, shikenan kai kullum bakada aiki sai cin zalinsu" a hankali ya tako har inda take zaune shima ya zauna tare da rik'o hannunta


"Mom ya kamata kifahimci cewa su 'YAN UWA NANE ina matuk'ar sonsu shiyasa  nake yimasu haka, duk wannan abun da nake yimasu inayine saboda in daidaita rayuwarsu badon in takura masu ba"



"Shikenan naji amma meyasa baka lallaahinsu idan sunyi laifi kamar yanda kake yiwa waccan ma...." Da sauri yarufe mata baki saboda bayason kalmar da zata fad'a mararsa dad'i akan qanwarsa Bilkisu


"Kiyi hak'uri mom in sha Allah suma zan dinga lallashinsu matuk'ar sun gyara in kuma sukak'i dukane zai rabani dasu" kunnensa mom ta murd'e yayi saurin cewa 



"Washhh...mom harkin manta da yaronki ba lafiya shine kike neman ciremun kunne?" Sai a lokacin mom ta tuna da rashin lafiyarsa saboda abunda yafaru d'azu data tafito wajen ganinsa ba k'aramin b'ata mata rai yayi ba.


"Ayya sorry my son, ya jikin naka?"


"Am ok mom, nasamu sauk'i alhmdulillah, zamu fita da dady kuma tuwon alkama nake son ci"


"To ku tsaya a restaurant kaci mana kafin kudawo don bazan iya dafashi ba, kannen kama ka nema masu abunda zasuci ni bacci nakeji" 


"Pls mom kitaimaka kinsan bazan iya cin abincin waje inba dole ba"


"Haba my son baccifa nace maka zanyi, ko kana son takura nine?"


"Noo..shikenan mom bari mutafi" rai ab'ace yabar falon har yana cin karo da Billy dake k'ok'arin shigowa da gudu


"Washhh.." Tafad'a tana k'ok'arin fad'uwa, da sauri ya tarota 



"Sannu lil sis, meyasa kike son gudune ko nauyin jikinki bakyaji, nakusa fara dukanki idan baki dena wannan d'abi'ar ba"


"Sorry dady ne yace in kiraka" tana rufe baki suka had'a ido da mom dake bakin k'ofa rik'e da hannun bilal tana shirin ingizo k'eyarsa waje, sunkuyar da kanta tayi yayinda mom tayi kamar batasan da itaba tace



"Maza wuce kabar nan munafukin yaro, shine zakaje ka tsaresa kuna kallo don bak'in hali bacin kaga ba'a shirya masa ba ga dadynku najiransa" baki abud'e Mahmud ke kallon mom kafin yaje yakamo hannun bilal subar wajen,


Cike da tsana mom ta sake dallawa Billy hararar datasa tabar wajen itama da sauri


Kusan mintuna ashirin su dady sukayi suna jiran fitowar su basmah, can Mahmud ya hangosu tafe basmah saye da wata pitet street gown an tsaga rigar tabaya gashi ta matseta tako ina sannan ta yafo wani siririn mayafin da ko wuyanta bai ida rufewa ba ita kuma batool, a tsorace dady ya kalleta sannan ya maido kallonsa ga Mahmud fuskarsa d'auke da ayar tambaya. Duk'ar da kai Mahmud yayi sannan yafito cikin mortar ransa ab'ace ya nufi inda suke, batool da bassam na ganin haka suka rugo suka shiga cikin mota yayinda basmah taci gaba da tafiyarta cikin hankali kwance duk da zuciyarta cike take da tsoron yanayin da tagansa amma saboda yanayin rigar dake jikinta kotaso tayi gudu hakan bazai yuyuba shi yasa taci gaba da tafiyarta, kafin ta k'araso taga yafara ciro belt d'in dake jikinsa da baya da baya tafara ja amma ina kafin ta ankara har ya cimmata, dukanta yakeyi har saida tafad'i k'asa tana ihu, mom ce tafito aguje tana fad'in.....




Post a Comment

0 Comments