TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Zazzafan so page 17

 


📄 *17*




*Tunani* ya hanata sakat, da k'yar ta samu bacci ya d'auketa.

Da asuba tatashi tayi sallah, amma ta kasa komawa bacci. Tana kwance kawai shiru har yanzu takasa samun mafita akan al,amarin.

Hajiya dai bata kuma yi mata maganar Yusuf ba.

Da la,asar ta hau shiri. Hajiyah ta kalleta "To Yanzu Hafsah sai yaushe kenan?" k'ak'alo 'yar dariya. 

"Hajiyah sai an kwana biyu dai"

"To shikenan, sai na ganki"

Bayan ta gama shiryawa ta d'auki jakar ta.

"To Hajiyah zan tafi. To shikenan ki gaida mutanen gidan"

Kyautar atamfa da turare Hajiyar tayi mata.

Bayan taje gida ma tunanin ne ya dameta, ta kira Basma amma wayar ta bata shiga ba.

Gashi yar yanzu Yusuf bai kirata ba, ita kuma tsoron kiranshi take, bata san abinda zai ce mata ba. Ahankali hawaye yake bin kan kumatunta, wani zafi zuciyar ta ke mata.

Kwance take bisa filo akan gadonta.ta d'aga kanta sama..

Zancen Jamila ta tuna *"Hafsah baki so bane shiyasa*

Tabbas lokacin hakane, shiyasa taji haushin Jamila alokacin don taga tana kuka akan _rashin-masoyi..._

Ta shafa kumatunta taji hawaye wato dai da gaske kuka take akan wani..?

Ahankali ta mik'a hannu ta d'akko wayarta, text ta rubuta mishi kamar haka:

*I have committed a sin to make you sad,*

*and am realizing that am very bad,*

*so, plz forgive me* *to lessen the grief,*

*ur forgiveness will led to a relief,*

*So plz forgive me*

Ta tura mishi, sai lokacin tayi ajiyar zuciya.

Bashir ya shigo cikin d'aki nata.

"Yaya kizo Abba ya dawo yace ina kike."

Tilas ta mik'e ta nufi hanyar toilet d'inta,

Bashir gani nan"

Fuskantarta ta wanko sannan ta fito ta zari dankwalinta bayan ta b'oye wayar ta ta fita.

"Yaya. Abba ya kirata bayan ta zauna. Ta d'ago ta kalleshi.

"Na,am ta amsa a k'asan mok'oshi.

Baki da lafiya ne? Ta girgiza kai "A,a"

"To ya kika baro min Hajiyata.

"Tana nan Lpia tace tana gaidaku"

"Gobe in sha Allah zanje in gaidata, kwana na uku kenan ban je ba" 

Ya fad'a yana kallon mama.

"Ai shiyasa na tura Hafsan saboda an dad'e ba,a je mata ba." 

Inji mama.

"Ai kin kyauta"

Ya Kalli Hafsah cike da kulawa. 

"Ko dai baki so baro gidan Hajiya ba ne?

Ta d'anyi murmushi "A,a Abba"

"Kinga yaya katin DSTV d'innmu ya k'are kinga babu kallo yau, ki karanta mana wannan kinji.

Ya fad'a yana mik'a mata littafin 'Magana Jari ce' (Na Marigayi abubakar Imam)

Ta sa hannu biyu ta k'arbi littafin.

"Abba wanne za,a karanta?

"Ki Karanta mana mai dad'i,ko wanne ma."

Mufida tace "Abba ni ma zan karanta."

Bashir ya harareta "sai kace iyawa zatayi.

Abba yai murmushi "Wa yace maka mamana ba zata iya ba? "

Labarin 'HASSADA GA MAI RABO TAKI'

Shi ta fara karanta musu, tanayi abba nayi mata gyaran hausa saboda Hausar irin ta da ce me sarqaqiya.

Labarin nada tsaho da kyar ta k'arasa.

Ko babu komai Hafsah ta d'an manta damuwarta zama cikin 'Familynta' ya d'ebe mata kewa da kuma damuwa.

Abba ya d'anyi musu sharhi akan labarin, Mufida ta dameshi da tambaya

"Abba Menene 'kusumbi'?

Abba yayi dariya kije ku kwanta da safe zan fad'a miki.

Yasan idan ya fad'amata sai ta k'ara k'irk'iro mishi wata tambayar.

Suka mik'e suka nufi d'akinsu.

"Ayi addu,a dai, inji Abbah.

"To Abba" Mufida ta fad'a.

Babu laifi Hafsah ta sami nutsuwar zuciya, damuwarta ta d'an ragu game da Yusuf. Yanzu ta juya akalar tunaninta izuwa nema musu 'Mafita'

akan al,amarin.

Meyasa Yusuf yake haka ne?? wai dama haka halinshi yake ko kuwa jiya ne kawai yai mata haka?.. 

Ko dai dama bata fahimci halayyarshi bane?

Duk wani saurayi na k'warai mai yin so tsakani da Allah ba zai tab'a yunk'urin zubar da kimar wacce yake so ba, zai iya jure komai saboda ita. Amma shi kodai manufar soyayyarshi ita ce 'Neman wani abu daga gareta'??

Tayi saurin korar wannan tunanin daga cikin zuciyarta.

*'So hana ganin laifi'* 😇

Wani b'angare na zuciyarta ya k'alubalanci zarginta akan Yusuf.

Hafsah biki yiwa Yusuf adalci ba. Shekara d'aya yana jiranki, da haka yake nema daga gareki ke kad'ai ce mace a duniya? Amma haka ya zauna jiranki... Kuma kirasa shaidar da zaki masa sai wannan? Saboda ansami 'Akasi' na lokaci d'aya??

Hafsah ki tuna waye Yusuf, murmushinshi, kalamanshi, soyayyarshi gareki.. Bakya tunanin idan kin rasashi kin tafka 'asara'?

Zuciyarta ta cigaba da karanto mata,hakan ya tilasta mata d'akko laifukan kacokan ta d'ora su akanta...

Meyasa take yi mishi kwalliya?

Meyasa ma jiyan tasashi kallon cikin idanuwanta, tabbas itace ta jawo koma menene. Ai kowanene ma dole ya sami rauni, balle kuma da tasiri soyayarta. 

Dole ne ta chanja tsarin mu,amalarsu...

Wannan ne matakin farko da Hafsah ta d'auka duk don tsoron kada Yusuf ya tsere wa samunta.

Bata samu bacci da wuri ba.

Da asuba Abba ya shigo tashinta, bayan ta yi sallah ta koma ta kwanta, cikin sa,a ta samu bacci mai nauyi.

Bashir ne ya shigo d'akin yana dukan filon (pillow) da take kwance.

"Yaya wai mama tace, ki tashi munyi late wai ko baki da lafiya ne?

"A,a yanxu zan shirya."

"Ok Yaufa har 7:00am tayi."

"Ok Kujira ni."

Agurguje ta shirya ta fito.

Amakarantar babu laifi ta d'an saki jiki, tunda a ganinta ta samo maganin matsalar, sai dai damuwarta d'aya ce 'bai kirata ba' sai kuma tunanin, ya zatayi ta dawo da mu,amalar su kamar da, don tasan Yusuf da tsawaita fushi..

Tana cikin Aji bata fita break ba. Tayi shiru taji an daki bayanta.

"Shegiya H. Hamid wa ya had'a miki tension? Ta fad'a lokacin da take zagayowa kujerar kusa da Hafsah ta zauna.

Hafsah, ta d'ago da sauri jin muryar Basma yunus.

"Au dama kinzo yau najiki shiru a class"

Tai dariya cikin muryarta mai karad'i tace,

"Wallahi nazo.

Kin san in dai 'Gajere' na class ba,a jin kaina."

Hafsah tayi 'yar dariya.

"Hah Basma Yunus baki bar kowa ba"

"Wallahi kuwa har Daddy"

Hafsah ta bud'e baki zatayi magana sai kuma ta fasa, abin ya fi k'arfinta.

Basma ta d'ana mata duka a cinya.

"Ke wai me ya dameki ne?.. Jiya fa naga mutuminki a wajen wani party har mun gaisa"

Gaban Hafsah yai wani irin bugawa tace 

"Yusuf d'in.?

"Yes"

"Hmm i'm telling you, ai yaro ne tsadadde biki ga 'yan mata First Class ba, yadda suke rububinshi.

Hafash dai jinta kawai ta ke amma tunaninta na can wani waje.

'Wanne irin party ne haka?

Ta daure tace

"Ke me ya kaiki partyn meye?

Basma tayi dariya.

"You know, ina da wani friend Ahmad. So shine yai inviting ena na graduation en wani abokinshi, so ashe abokin Yusuf ne ke graduation en"

"Wallahi Yusuf ya iya rawa biki ga ba, kinyi dace k'awata. Ina ma kaina 'wishing' in samu kamar Yusuf."

Ran Hafsah ya d'an sosu taji kishi ya d'arsu a zuciyarta.

Tai ajiyar zuciya kawai.

Ta bud'e jakarta ta d'akko musu snacks da lemo, 

"Muci ni yunwa nakeji."

"Akwai abinda ke damunki fa"

Cewar Basma.

Hafsah tace 

"Hmm ke dai bari. "Munsami misunderstanding ne da shi"..

"What, Meya had'aku.?

Hafsah sai taji ta kasa fad'a wa Basma.

"OK, tunda bazaki fad'a ba.

"Kinzo da waya.?

Hafash ta girgiza kai.

Basma ta ciro wayarta.

"Am bari mu kirashi saka number en. Banyi serving ba.

Hafsah tasa number tana cewa "Sai dai ki mishi magana idan yaji nice ba zai d'aga ba."

"Ok"

Yana d'agawa Basma ta kashe murya.

"Hallo,Basma ce k'awar Hafsah."

"Ok how are you"

"Very fine" 

"Am mene ya had'aku da Hafsah ne?

"Hmm, Basma your friend dont' care about me" 

"Bata damu dani ba ne"

"No,ba haka bane meya faru?

"K'awanki bata sona, tana guduna ne she disgraced me! " she dn't allow me to touch even her hands, not talk about kissing.."

Ya fada bbu ko kunya.

""Hmm, I get an opportunity"💃🏼

Basma ta fad'a aranta.

A fili kuma cewa tayi, "Am sorry, this is not a problem to worry about."

"What? Me kina nufi? "

"Calm down kasan yanayin ba da'ya ba, So I think my friend don't have interest about it"

"Hmm ok" Thank you"

"Kayi hak'uri fa"

No I know how to deal with her.

"Ok Gata to"

No ki rabu da ita.

"A,a dai"

"Ok"

Ta mik'a mata wayar.

"Hello,

"Hum, Hafsh me yasa kike min haka ne? 

"Am sorry please I don't mean to hurt you my dear"

"Hmm, ok zamu yi waya to night."

"Bye"

Hafsah ta rungume "Basma thank you my friend"

"Me ya ce miki ne? kinsan wayar ba a hands-free take ba."

"No, ki share tunda yace komai ya wuce.

"Ok"

Hafsah dai wasai take jinta,sun shirya da Yusuf d'inta.

ina sonka Yusuf d'ina Allah ya tsaremin kai!!

Basma ta bita da kallo..

To da yamma bayan abba ya dawo daga wajen aiki gidan Hajiya ya wuce, bayan sun gaisa tasa aka kawo mishi abinci.

Yana gamawa akayi kiran sallar magariba yai al,wala, 

"To Hajiyah daga can zan wuce."

A,a ka dawo dai"

"To Hajiyah.

Bayan ya dawo ya zauna a k'asa, yana fuskantarta, yasan da akwai maganar da zasuyi.

"Na dawo Hajiya"

"To madallah."

Dama cewa nayi shi wancan yaron da yake zuwa wajen Hafsah an daidaita ne?

Abba yaji abin banbarakwai,

"Wanne ake magana Hajiyah?

"Au to ,baku kirashi ba kenan."

"Wani yaro ne haka Mara k'iba. Shekaranjiya ya kirata a salularta (waya) ya zo ma nan sun gaisa."

Kan Abba ya kulle amma gudun kada Hajiya ta gane yace

" Oh to, eh saboda bata gama Makaranta, bane shi yasa"

"To yadai dace a tuntubeshi aji idan da gaske yazo."

"To za,ayi hakan Hajiya."

Yayi mamaki da Hajiya ta ambaci waya, amma don ya sake tabbatarwa sai yace.

"A wayarta kenan ya kira, sannan yazo Koh?

Hajiyah tace,

"Eh mana, kasan zamani cigaba yazo, da ya iso ma kiranta yayi ta fita."

"To Hajiyah ni zan koma."

"To ka gaida mutanen gidan."

"Allah ya kiyayeku Allah ya tsareku, daga mugun ji da mugun gani. Allah yai muku albarka."

"Amin Hajiya, Amin".

"Sai da safe"

"Allah ya tashe mu lafiya"

"Amin"

Abbah tuk'i yake amma gabadaya ranshi ab'ace yake, ya kasa yarda da abinda Hajiya ta fad'a mishi, yama za,ayi ayi haka? 'yarsa?..Hafsah?.. Ta mallaki waya bai sani ba? Ta dinga zance da saurayi wai duk bai sani ba?

Yasan tabbas da sanin mamanta.

Lallai zai nuna mata b'acin rai in dai haka ya tabbata.. 

Abin ya bashi madaukakin mamaki fa, inda badon hajiya ce ta fada ba zai taba yarda ba.

Wanne irin sakaci yayi har haka ke faruwa a gidansa??

Huci yake sosai da ya isa gidan. Mama na ganin yanayinshi tasha jinin jikinta...




Post a Comment

0 Comments