TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Hauwa kulu book 2

        ‘YAR CIKIN BADALA

     (HAUWA-KULU)

    2



                                    



SUMAYYAH ABDULKADIR babbangoro2015@yahoo.com

     07030137870

      (whtsp only)

    PAID BOOK

          SADAUKARWA

SADAUKARWA NE GA DUK MAKARANTA LITTATAFAINA ‘YAN CIKIN BADALAR KANON DABO.










               HAUWA-KULU-2

M

ota na tsayawa agaban su ta ce masa “Kurna”. Ba don ta san kowa a Kurnan ba, sai don ta san tayi nisa dai da cikin gari, ta tafi can wajen fita garin Kano, shi kuma mai mota ya ce naira biyar, duk da Inna ta san zuka musu kudin yayi don ya gansu hajaran majaran amma bata ko nemi ragi ba, ta kama hannun Hauwa suka shige da katon bakkon kayan su.

Aka zo Kurna, sai ta rasa inda zata ce ya sauke su, shi kuma ya gaji da yawo dasu a Kurna sai yace ko tasha zan kai ku in gari zaku bari? Inna ta samu kanta da cewa “eh”, sai ya kai su tsohuwar tashar nan wato Tashar Kuka ya ajiye su.

Inna ta kama hannun Hauwa duk sun yi wujiga-wujiga da gajiya da yunwa, suka je rumfar wani mai shayi, a daidai lokacin hantsi ya dubi ludayi, ta zaunar da Hauwa a bencin da babu kowa, mai shayi ya zo wajen su yace “Iya lafiya? Ba’a bara a kan benci na, na sana’a ne”.

     Hauwa ta fiddo manyan idanun ta tana sama tana kasa da su, wai dai ya san hararar sa take yi, don ba abinda ta tsana a ambata mata irin a dangantata da kalmar “BARA” don tana makauniya mara ido, ba don Inna ta koyar da ita kyakkyawar tarbiyyar rashin saka baki a maganar manya ba, da ta zage shi, mai shayi ya ce,

     “bayin Allah ku kara gaba don Allah, kada ku kashe min kasuwa da wannan daurin bakkon naku duk warin tsummokara”. 

    Inna ta daure ta ce “don Allah zuba mata shayin ta sha, zan biya ka, nawa ne kofi daya? Ka yanka mata biredi”.

    Nan ne Hauwa ta kasa daurewa, ta ce “Inna ko wannnan shi ya saura shayi a duniya, ko yunwa zata kashe ni, ba zan sha ba, tun da ya ce mana mabarata” ta fashe da kuka, sannan ta mike tana laluba bakkon su, ta dauka ta dora akan ta, Inna ta mike ta kama hannun ta suka tafi, yana cewa “Umma ta gaida ashsha, dama makafi akwai fadin rai, da zuciyar tsiya kamar kutare, ni bana son harkar mabarata da nakasassu”.

Inna ta hango rumfar wata mata mai saida abinci, ba yawan mutane a wajen, sai ta ja Hauwa suka nufi wajen, matar tana ta kai kawo da masu sayen abinci uku dake kan tebur, da ganin ta ka ga ‘yar Kano-Jeddah, Inna tayi mata sallama, da mutuntawa ta amsa ta ce “Iya sannu ko? Abinci zaku saya?” Inna tace “eh, zuba mata ta ci ta koshi kisa mata yankan nama, nawa ne kwanon shinkafa da miya?” Matar ta ce “naira bakwai”, haka ta zuba ma Hauwa abinci mai rai da motsi ta shigar da ita rumfar da babu mutane sosai ta bata ruwa ta wanke hannu. 

    Inna tana zaune tana sakawa da kwancewa, ko yunwar ita bata ji saboda duhun zuciya da bakin cikin abinda Zakari yayi musu. Tana matukar son gidan ta, duk wani tarihin ta da mijin ta da ‘ya’yan ta, duk wata dabdalar gidan aure, dama jin dadin rayuwar ta ya ta’allaka ne a cikin gidan nan na bayan BADALA. Amma ace yau rana daya….??? Ta sa gefen zaninta ta share hawaye tayi sharbe, wanda Hauwa ta ji shi. 

    Tadago gululun manyan idanun ta zuwa sashen da taji sharben Inna “Inna ke bazaki ci ba ke?” “Ci Kulu ki rabu da ni kinji, ba zan iya kai ko ruwa baki na ba yau”.

     Sai itama ta tsame hannunta, ta koma jikin bangon wurin ta jingina itama, kamar yadda Inna tayi, ta hade jikin ta cikin hannayenta ta takure kai a cikin kafafunta, ta ce “to shikenan nima ba zan ci ba, tunda kema Inna ba zaki ci ba”.

     Inna ta ce “Kulu yunwar ce bana ji sam”. Hauwa ta ce “na san bacin rai ya hana ki ci, amma abu daya nake so ki tuna Inna, idan Kawu Zakari ya rushe gidan mu, ya kwace ta karfin tsiya saboda iya zaluncinsa ai Allah ba azzalumin bawanSa bane, kuma baya yafe hakkin wanda aka zalunta. 

    Ba kuma zan gushe a cikin sujjadar salloli na biyar na farillah ba face ina mai kai karar sa wurin Ubangiji.

    Inna ki manta da Baba Zakari, mu fuskanci wadda zata fishshe mu. Son samu Inna mu fara sana’ar abinci muma a tashar nan, tunda na lura akwai kudi a jikin ki”.

     Inna ta ce “eh da kudi, wadanda yaronnan Jamilu ya bani kan ya tafi, amma Hauwa ai baka fara sana’a farat daya baka zauna a wajen ka fuskanci yanayin wajen dana mutanen wajen ba, da irin zaman da ake yi a wajen, dabi’un su da yanayin mu’amalar su. 

    Ta yaya zamu zauna a Tasha bayan matattara ce ta rashin arziki ga ‘ya’ya mata? Ki dai bari mu kara gaba, in ya so ko a masallaci sai mu dinga kwana”.

    Duk hirar nan da suke yi a kunnen Hajiya Ladi mai abinci, tana kirga kudin cinikin ta tana sauraron su da kunne daya, don ta gama da girkin safe, zata fidda riba ta dora na rana. 

    Ta ji tausayin Inna ta kuma ji Hauwa ta burge ta, wadannan idanu na ta da alama basa gani, amma duk da haka zuciyar ta bata mutu ba, ba ta ce tunda gasu a tasha su yi bara ba, don ita makauniya ce zata zamewa uwarta hajar samu, gata budurwa son kowa, sai ma cewa uwarta take su kama sana’a.

     Hajiya Ladi ta matso inda suke ta zauna, tace “naji duk abinda kuka tattauna a junan ku, duk da ban san daga inda kuke ba zan baku masauki a gidan da nake zaune, in kuma dinga baku aikin abinci kuna taimaka min, sai mu dinga zuwa nan tare kullum in mun sayar mu koma gida tare, ni kuma zan dinga baku abinci sau uku a rana. 

    Ban yi karyar biyan ku ko sisi ba, abincin da zaku dinga ci da wajen kwanan da zan baku shine ladan aikinku, in ya so in kika gane yadda ake sayar da abinci a nan tashar kina iya kafa naki tebirin daga baya.

    Baiwar Allah muma da Allah ya rubuta mana samun na abinci a Tasha, ba zabin mu bane ba, da gaske akwai bata gari, kuma matattara aikin ashsha kala-kala, amma yaya zakayi da abinda Allah ya rubuta cewa anan samunka yake?”.

     Inna da Hauwa suka hau godiya ga Hajiya Ladi mai abinci, kuma tun daga ranar ta basu daki guda a gidan ta wanda ke nan unguwar Rijiyar Lemo, ta kwashe shirgi tace su dinga kwanciya a dakin. Amma da wuri zasu ke tashi su tafi tasha a dora mata abincin safe, zuwa karfe hudu sun saida na rana sais u dawo gidanta tare.

Ta koyawa Inna kalolin irin girke-girken da take yi, ga mamakin ta sai ta samu Innar Hauwa kwararriya ce a fannin girki har ta fita kwarewa. Gata da tsaftar jiki data muhalli, tuni ta kara rike Inna da kyau.

  Tun daga ranar suka soma yi wa Haj Ladi aiki, Hauwa ma ba’a barta bata aikin komai ba, ita ke wanke wanke na kwanukan da aka bata, tsaf take wanke su ta dauraye ta kife a kwando.

     Kafin sati ya zagayo sun kware da aikin abincin Haj. Ladi, sun saba da sauran ma’aikatan Hajiya Ladi biyu Zulai da Amuna.

Hajiya Ladi na da ciwon Asma duk ranar da ta motsa mata bata iya tabuka komai, sai kwanciya sai tari, sai ta danka komai a hannun Inna, ganin ita babba ce ta girmi su Amuna kuma ta fi su hankali da kula, wannan ya fusata Zulai ta bar aikin, don a ganin ta an fifita bakin zuwa a kanta.

    Ya zama saura Amuna da Hauwa kadai ke yin sauran ayyukan, har aikin da baka tsammanin mara ido zai iya Hauwa ta iya, su yankan alayyahu da yankan salak, kuma ba tare data yanke hannun ta ba, haka duk wani aiki da za’a iya yi daga zaune, ita Inna ke baiwa tayi.

****              ****               ****


    Ciwon asma mai tsanani ya kwantar da Hajiya Ladi sosai, baiwar Allahnnan sai ta soma tsoron kada ta mutu ba’a san kowa nata ba, yanzu kam tayi nadamar rayuwarta da kuruciyarta data karar a Kano-to-Jeddah, harta soma tunanin iyayenta ko suna raye yanzu?

    Haj Ladi ta soma istigfari daga kwance, rannan cikin dare ta tashi, ta kuma tashi Innar Hauwa, tana kuka ta soma gaya wa Inna ita asalinta. Tace ita ‘yar kauyen Billiri ce, Billiri ta Gombe, ita ‘yar mai garin Billiri na lokacin ce, tace abinda ya fiddo ta daga gida auren dole ne suka samu uwar daki ta haure da su Makkah suka jima cikin rayuwa ta Kano-Jidda, daga baya aka kamo su aka watso Najeriya, shine fa ta kama sana’a don tana tsoron karuwanci a Kano, sabida shari’ar musulunci da aka kafa lokacin, har yau bata iya ta koma gida ba.

     Tace “idan ta Allah ta kasance a kaina, na bar miki shagon nan ki cigaba da hayar sa saboda rikon amanar ki, bamu jima tare ba, amma na yarda da halayen ki na kwarai, inaso ki cigaba da sana’a ta amma ki tattara komai nawa ki kaiwa mahaifi na, ki roka min gafarar sa, zan kara jan hankalin ki kan ki kula da mutuncin makauniyar ‘yar ki a rayuwar tashar nan, don akwai bata gari, gashi ta cika ido ta kai munzali, Allah ya taya ki kula da ita.

Jikin Inna yayi sanyi ta ce “Hajiya Ladi tafi da kan ki nemi gafarar mahaifin ki, tunda da sauran karfin ki, ciwo ba mutuwa bane, iyaye sun wuce komai kuma ba zaki taba samun kwanciyar hankali ba in baki samu albarkar su ba. lokaci bai kure miki ba Hajiya Ladi”. 

    Inna da Hajiya Ladi sun yi wannan maganar da kwanaki biyu Inna ta wayi gari da asubah don yin sallah sai ta fahimci Haj. Ladi bata tashi sallahr asubah kamar yadda suke yi kullum ba, tun tana tunanin jikin ne ya motsa mata ta makara har garin Allah ya waye Haj. Ladi bata tashi ba, sai ta matso ta duba ta, anan ta fahimci Hajiya Ladi, babu. Wato rai yayi halin sa.

****                 ****                   ****


Inna ta tsaya tsayin daka aka kai gawar Hajiya Ladi gidan mahaifin ta wato gidan Maigarin Billiri, ta kuma isar da wasiyyar Hajiyar ta hanyar damka masa dukkan kudaden ta na cikin lalitar ta, ya sakawa Inna albarka yafi cikin kwando, ya tambayeta ko ita ‘yar ina ce? Don bata yi masa kama da ‘yan Kano Jiddan ba ita, Inna ta gaya masa daga cikin Badalar Kano suka fito, neman abin rufin asirin rayuwa, sakamakon batan maigidan ta, shine suka hadu da Haj. Ladi gun sana’arta, ta kuma taimaka musu a lokacin da basu da mataimaki sai Allah, ta gaya masa sun yi zaman amana tare. Ta kwashe duk irin taimakon da Haj. Ladi tayi musu ta fada masa, shi kuma ya ce albarkacin ta da mutuncin ta ya yafe wa Ladi duniya da lahira. Zai taya ta rokkon gafarar Ubangiji.

Ta fada masa Hajiya Ladi ta bar mata shagon abincinta ta ce ta kama ta cigaba da yi, tana da jari, don haka zasu koma Kano, yayi mata fatan alkhairi da godiya, bayan sadakar ukun Hajiya Ladi suka koma gidan da take haya inda suke zaune, kasancewar kudin shekara data biya bai kai ko rabi ba.

    Inna ta fiddo ajiyarta ta kudin da ta ke ta ajiye da su tayi cefanen abinci yadda suka saba lokacin Haj. Ladi, daga ranar ta cigaba da sayar da abinci, ba maraba da Haj. Ladi na raye.

Ciniki sosai suke yi da tsofaffin kwastomomin Haj. Ladi, a kullum ranar Allah sai ta dafa shinkafa tiya uku, suka tara kudi masu dan yawa, daga nan Hauwa ta kawo shawarar su canza gida mai dan kyau, abinda suka tara zai ishe su kama gidan haya tunda kudin Haj. Ladi ya kare, Hauwa tace su kama gida a nan cikin Kurna ko dai wani waje kusa da tashar kukan.

    Hakan kuwa aka yi. Inna ta kama dan mitsitsin gida mai tsafta fiyeda na Haj. Ladi, mai dakuna biyu da bayi da madafi a wani lungu cikin unguwar Kurna.

     Sana’ar abincin Inna na kara bunkasa, don duk tashar kuka babu mai abinci mai kyau kamar nasu, har ta kai Inna ta dauki ma’aikata biyu a karkashin ta da suke tafiya tun asubah su dora abinci kafin ta iso, Saude da Hajara zawarawa ne, ita kuma sai gari ya fara haske tayi sallar walha take tadda su, galiban zata tarar har sun dafa sun kwashe, sai ta zauna ta fara sayarwa da kanta. 

    Basu jima a Kurna ba Hauwa ganin hankalin su ya kwanta, kuma samun su ya ninka na baya ta tada kayar bayan komawa makarantar su, ga shekarar na neman wuce ta, za’a zana qualifayin, tunda dai yanzu suna samun kudi daidai gwargwado Inna bazata kasa daukar nauyin zuwan ta makaranta ba, dama jakar makarantar ta da komai na makarantar ta na nan har lokacin bata rabu da goyon ta ba, hatta uniform da [photochromic Glass] dinta da takalminta suna nan cikin jakar. 

    Inna ta ce Hauwa daga nan Kurna zuwa makarantar ku akwai nisa fa, kuma bazan iya kai ki kullum da kaina in dawo dake ba, da girkin abinci da muka dogara da shi zan ji ko da kai ki makaranta da dauko ki?” 

    Hauwa ta ce “Inna me zai hana mu samu mai Achaba wanda ya kasance dan unguwar nan da aka san gidan su da komai nasa, ku tsadance, kullum ya kaini ya dauko ni, in yaso a dinga biyan sa duk karshen wata”.

     Shawarar Kulu ta samu karbuwa gun Inna, dama tasan dai Hauwa-Kulunta ba daga nan ba wajen kaifin basira. Hakan kuwa akayi.

Hauwa ta samu komawa makarantar su special school ta Kano a ranar wata litinin, daga malamanta har dalibai ‘yan uwan ta sun yi farin ciki da dawowar Hauwa Bilyaminu, bayan kwashe watanni shidda rabon ta da makaranta.

Amma duk da haka saboda kokarin Hauwa malaman su basu yi mata rifitin ba, sun tabbatar bada jimawa ba zata kamo duk abinda ya tsere mata. 

    Wani kabila dan bautar kasa mai suna Teacher Amos Hedimasta yasa yake yi mata lesson fisabilillah, saboda kokarin ta, kullum na awa daya bayan tashi daga makaranta. Wannan ya taimaka mata kwarai tayi saurin kamo ‘yan ajin nasu, ya zama da an fara sabon darasi Hauwa zata cafke, musamman da yake akwai kishin abun a ranta da kulafucinsa, hadi da tsoronta na zama MABARACIYA saboda rashin ido.

     Hauwa ta jajirce, ko barci bata yi kullum ta dawo zaka samu tana karatu da Braille, har sai Inna ta kwace littatafan ta, ta kashe fitila, ko ta ce, “karatun ya isa haka, dare mahutar bawa ne”.

 

    Ba jimawa da komawar ta makaranta aka yi jarrabawar kwalifayin, aka yi hutu, wanda in sun koma su Hauwa zasu shiga aji shidda na sakandire.

     Sakamakon jarrabawar qualifayin din ta lokacin da ya fito, yafi na kowa a makarantar kyau, yafi na kowa daraja, komai nata daga ‘A’ sai ‘B’. A lokacin kam makerin budurci ya gama kera Hauwa Bilyaminu, da ka ganta kaga kyakkyawar bakanuwar budurwa, mai samun kulawar Uwa da tsaftar jiki da abinci mai gina jiki, yadda ya kamata. 

Kafin su Hauwa su koma hutun da zata fara aji shidda suka bar sayar da abinci a tashar kuka, suka dawo sayarwa a tashar Kano-Line, ba don komai ba sai don yafi kusa da makarantar Hauwa kuma samarin tasha sun fara son matsawa Hauwa a can tashar Kukan, da cewa suna son ta har da masu neman ta da sakarci, duk da idon uwar ta kuwa. 

    Wannan ya tadawa Inna hankali ba kadan ba, ta ga dole su bar tashar kuka zuwa inda basu saba da kowa ba. In yaso ta hakura da ko me take samu a tashar don kare mutuncin Hauwa. Don da yawa suna amfani da sabo da mutuncin dake tsakanin su da Innar ne, su soko mata zancen suna son Hauwa, sabida kirkin Inna da yadda ta ke sakarwa kowanne kwastomanta fuska yasa take da jama’a, yawanci matafiya da masu shigowa Kano ta tashar tasu da direbobi dake cin abinci wajen ta. Ga ita Hauwar kam! Ai duk iya rashin kunyar mai zuwa cin abinci teburin su, bai ma isa ya tunkare ta da wata magana wadda ba ta sayen abinci ba, don babu fuska sam. Zata iya wuni bata yi koda murmushi ba. abinda Kawu Zakari yayi musu yayi mata illah a zuciya sosai ya rage mata walwala. “Hauwa-Kulun–Majadun” kenan.

Duk da cewa bayan sun dawo tashar Kano-line sun kama gida a unguwa uku shima mai daki biyu ne, amma sun fi ciniki sosai a tashar kuka, wani ko ba don Allah ba zai sayi abincin Inna a tashar kuka saboda daukar hankalin sa da makauniyar ‘yar nan tata tayi, wadda ke taya Innar ta aikin abincin da sayar da shi wa masu bukata da zarar ta dawo makaranta. 

    A wancan lokacin Hauwa ta gama isa aure har ta na neman wucewa don gab take da zana jarrabawar fita sakandire wato SSCE, ta samu damar da ‘yammata da yawa a zamanin basu samu ba, saboda da sun fara makarantar ake cire su ayi musu auren wuri, amma Inna bata bada fuskar da wani zai zo mata da zancen son Hauwa ba kwata-kwata, itama Hauwan ba fuska ko kadan. Don kullun Inna na gaya mata “da tun farko baki baiwa Jamilu fuskar zuwa inda kike da sunan neman aure ba, da har yanzu muna zaune gidan mu cikin sutturah, rufin asiri da kwanciyar hankali, da yanzu bamu zama masu sayar da abincin tasha ba”.

Sai Hauwa ta cuno baki gaba tace cikin kunkuni “to Inna Yaya jamilu ba dan uwana bane? Duk kin bi kin tsani Yaya Jamilu, kamar shine Baba Zakari, ina laifin sa? Halinsa daban na uban sa daban”.

     Inna ta kama baki, ta bude shi ta mayar ta sake rufewa cikin al’ajabi, wai ta san soyayya, ta ce “hakane, dan uwan ki ne, na jini ma kuwa, amma wallahi ki sani ko shi ya saura da namiji a duniya, kema kika saura diya mace a duk fadin duniyar nan in dai ni SAFIYA ni na haife ki, kuma ina raye, to baza ku yi aure ba, ke ko ina gargarar mutuwa zan bar wasiyya ga duk wanda na samu cewa ba zuri’a ta babu ta Zakari”.

Hauwa aka kumburo baki sai ka ce zumbutu ta ce cikin wani sabon kunkunin “to ai ni dama ban sa aka ba, in dai maganar aure ne Inna, kawai na san ba’a raba hanta da jini, Yaya Jamilu dan uwana ne dana ke kauna tunda ba wani jini na da ya taba nuna min kauna bayan shi, kogobe na kara ganin sa In sha Allahu zan kula shi, zan tsugunna har kasa in gaida shi don bana manta alkhairin da yayi min, kuma bani da masoyi duk duniya bayan ke irin sa”. 

     Inna ta harzuka, yau akan Jamilu tana fade Hauwa na mayar mata? Tace “hantar taku sai in ba’a saka mata soson karfe da farin omo da sabulun dan jangabo ba, tuni in taji karta jinin zai rabu da ita koda zata kukkuje ta karce, wawuya kawai, mara kunyar wofi.

     Ke na bi zumuncin naku da soyayyar taku da gudu na tattake su ba takalmi a kafata!”. 

Hauwa sai ta kama dariya ta ce “tsakani da Allah Inna ban san ki da dorawa mutum laifin da ba nasa ba, duk da haka Inna Allah ya huci zuciyar ki, ni ba bakuwar zafi bace a kan Yaya Jamilu, ina ni ina wani aure alhalin ba ido? 

    Kawai ina son Yaya Jamilu a rai na, kasancewar duk cikin ‘ya’yan Baba Zakari wa ya taba nuna min zumunci da kauna ta fisabilillahi idan bashi ba? Kiyi tunani Inna, ki rage kin Yaya Jamilu, laifin Baban sa ne ya shafe shi, yasa kike ganin bakin sa. Shiyasa kome zai yi bazai burge ki ba, tunda Baba Zakari ya riga ya shafa masa, amma ko kadan bashi da laifi”.

Haushi ya ishi Inna, tayi mata shiru ta rabu da ita ta kaiwa banza ajiyarta, don ta dade da sanin in za’a kwana ana kushe Jamilu, to kuwa Hauwa bazata gaji da kwana a hanya tana kare shi ba.

    Rayuwa ta mikawa Hauwa da Innar ta cikin rufin asirin Allah a tashar Kano-Line, inda suke gudanar da sana’ar su. Har gashi yau Hauwa sun fara zana jarrabawar WAEC wadda aka fi sani da SSCE a wannan watan da muke ciki. 

    Wadda da zarar sun kammala ta, Hauwa tayi sallama da makarantar kwalejin ilmi na musamman. Tunanin Hauwa kullum a yanzu shine, shin ko yaya rayuwa zata kasance mata bayan kammala sakandire? 

    Tunda dai Innarta ta ce bazata taba yi mata aure kamar kowacce mace ba wanda shi tafi bukata a wannan matakin? Ta sani ba don komai Inna take wannan kaffa-kaffan da ita ba, sai don kare mata martaba da mutuncin ta, har ma da tattalin kwanciyar hankalin ta, Inna tana bata kariya ne daga shiga matsalar gidan aure alhalin tana fama da wannan nakasar mai girma. Har ila yau, Inna tana guje mata shiga jami’a ne domin bata kariya daga fadawa ga soyayyar duk wani namiji da zata wahalar da ita a matsayin ta na karamar yarinya kuma mai raunin halitta na nakasar idanu, wadda har yau bata kai ga cika shekaru ashirin da haihuwa ba. 

     A wannan gabar da Inna ta san aure ne kadai ya ragewa Hauwa-Kulu, kuma ta fahimci tana ra’ayin yin sa da dan uwanta Jamilu ko bata furta ba, to bazata taba bari Hauwa ta kai kanta ga kowacce matsala ba.

     Da dukkan karfin ta zata kare Hauwa-Kulun ta daga duk wata soyayyar da bazata yi mata amfani ba.

    Inna tayi wa kanta alkawarin bazata bar Hauwa-Kulu taje jami’a ba, koda tana da ido kamar kowa, balle kuma BABU! Bazata lamunci shigar Hauwa jami’a bane don kada a gurbata mata tunani, ko kuma wani da yafi Jamilu iyawa ya hilace ta ya hure mata kunne, a karshe ya saka ta a matsalar da bazata iya fiddata ba.

     Tana da yaqinin yadda Ubangiji Subhana ya nufe ta da yin ilmin sakandire ba tareda dabararta ba, ya kuma tsara mata yin rayuwa cikin nakasa ba tare da ta tagayyara ko ta tozarta a dalilin nakasar ba, (kamar yadda dan uwan mahaifinta ya so su wulakanta), sannan rashin mahaifinta tare da ita duka bai sa sun kasa numfashi da motsi cikin kudurar sa cikin duniya ba, ta tabbata shi din dai sarkin wannan kudura da iradar wato (Ubangiji Subhana) bai manta da it aba, shi zai cigaba da tsara mata sauran rayuwarta ta can gaba, kamar yadda ya tsara ta baya ta hanyar da bata taba tunani ko tsarawa kanta ba, tunda shi dai Ubangijin KOWA. In tace KOWA tana nufin KOWA, har da ita HAUWA-KULU!

     Abin nufi anan, daga mai lafiya har mai nakasa duka nasa ne. shi ya halicci abunda yadda ya ga dama wato “Fa’alun lima Yureed ne”. Shi din, (Ubangijinmu), mai yawan hikima ne ga rayuwar duka bayinSa.

     Bai kuma halicci wani a mai nakasa wani a mai cikar lafiya don baya son dayan ba, ko don ya kaskantar da shi cikin bil adama, ko don ya saka shi cikin bakin cikin rayuwa mara yankewa, kamar yadda ya dade da fada mata ne;

     “Nakasa ba komai bace face jarrabawar Imani ga wasu daidaikun bayin Allah - (LIKITA SARHAM)”.

     

Idan haka ne kuwa zata tsaya tsayin daka wajen ganin cewa ta cinye wannan babbar jarrabawa da DR. SARHAM ya kwadaitar da ita muhimmancin cinyeta da TAUHIDI da IKHLASI (ta bakinsa), daga yau ta daina fito na fito da Innarta akan Yaya Jamilu, daga yau zata yi wa mahaifiyarta biyayya irin wadda wani da bai taba yi wa Uwarsa ba (koda ya san abun da take so din ba daidai bane), ita HAUWA_KULU zata yiwa Inna biyayya kan jiki kan karfi, akan duk abinda take so da ita da rayuwar ta, musamman hakura da rayuwar aure domin tserar da kwanciyar hankalin su.

    Ta san Inna tana yi ne don amfanin ita Hauwan ba don nata amfanin ba.  

    Hauwa-Kulu ta cigaba da gayawa kanta daga yau ta cirewa ranta burin yin aure kamar kowacce mace mai lafiyar yinsa, ta barwa Allah ikonsa a kanta, ta daina yarda zuciyarta na kwadaita mata Yaya Jamilu, kai dama duk wani Da namiji bayan shi da zai biyo hanyarta, ta yarda da nakasarta babban gibi ce da zata hanata jin dadin rayuwa ta wani bangaren, ta kuma karbeta hannu bibbiyu, ta yarda nakasar ido bazata bata damar yin abinda ke kira “MARITAL LIFE” da “MOTHERHOOD” ba, wadanda sune ginshikin rayuwar kowacce diya mace, kuma su suka fi komai dadi da muhimmanci ga rayuwar kowanne dan adam.


****                        ****                         ****

      (A GIDAJEN MALAMAI NA SABUWAR JAMI’AR BAYERO).

G

idan Prof. Abbas Shanono ya kacame da hayaniya a tsakanin jama’ar gidan da kawayen ‘ya’yansu da jama’ar mahaifiyar su da aka gayyato domin taya Surayyah Shanono, murnar kammala digirin ta na farko, bayan dawowar su daga filin ‘convocation’ na cikin jami’ar Bayero.

  Anan cikin gida bayan kawayen Surayyah sun gama dabdalar su sun tafi, Mama ta hada musu (get together party) su’I’su, domin kwarai tayi alfahari da sakamakon Surayyah, koda yake abin kamar a jinin ‘ya’yan ta ne, in dai ta fannin karatun boko dana addini ne basu da na biyu. 

    ‘Get together party’ din da Mama Mai Shari’ah Haj. Maimuna ta shirya na abu biyu ne; bayan taya Surayyah murnar kammala karatunta da kyakkyawan sakamako (first class degree) ya kuma kunshi sallama da auta Sumayyah, wadda ita kuma zata tafi Jeddah nan da kwana uku domin fara nata karatun, can a jami’ar da Abba Prof. yayi mata alkawari tutuni, wato Sumayyah zata tafi inda Bhaiyanta (SARHAM) yake itama a cikin satin nan da yardar Ubangiji.

    Tsananin kaunar juna irin na wannan family, da yadda basa yin wani abu babu sanin dayan su, yasa sun kasa cika farin cikin ranar yau ba tare da shi ba, musamman da ya kasance a lokacin wayar zamani ta tafi da gidan ka ta fara yawa a Najeriya (amma dai ba a kowanne gida ba), to shima dai Abba Prof. kamar sauran manyan ma’aikatan gwamnati a Kano ya mallaki tasa, har yana arawa iyalin sa lokaci-lokaci su kira dan uwan su dake nesa su gaisa.

    To yau ma hakan ce ta kasance. Sumayya ta ce “Abba ka kira mana Bhaiya ayi komai ‘live’ a kunnen sa”. Abba yace “kin manta Sarhamu jarrabawa yake yi?” 

    Sumayyah ta hau roko “Abbah don Allah, ko na minti biyu ne, bazan ja shi da surutu ba”. Surayyah kuma ta ce “Abbah ni zan biya ka kudin da zamu cinye maka a wayar”. Abba Prof. yace “da can dana ke baku aron wayar kuyi wayar da shi biyana kuke yi?” Suka hada baki wajen cewa “tuba muke Abbanmu! Abbanmu like no other Babanmu maganin kukan mu”.

    Prof. yayi dan murmushi kafin ya danna masa kira, ba jimawa Sarham ya amsa masa da cikakkiyar amsa sallama, da muryarsa dusassa, wadda a kullum yanayinta kamar na mai fama da mura. Sarham yace (cikin hausar shi wadda yanzu ta daina fita sosai yadda ya kamata).

     “Daga bangarena ina kokarin kiran ku ne fa Abba, naka kiran ya shiga nawa shiga, in ban manta ba yau ne graduation din ‘Surry Darling”. 

    Surayya ta saki dariyar farin-ciki jin yau wai Bhaiya ya kira ta da ‘Darling’ tana fadin “yau kuma?” Shima daga nasa bangaren dariyar yayi, yace “Surry rigima, Surry masifa Surry mathematician, Surry Darling!”. Duk falon aka kwashe da dariya da alama yau dukkansu cikin nishadi suke, abinda basu sani ba ya fi su nishadin wannan ranar, domin tayi daidai da ranar zagayowar haihuwar sa, kuma a daidai lokacin wani babban abun farin ciki ya same shi, wanda daga shi sai Allah suka san shi, wato wani ‘gift’ ne na musamman na taya murnar zagayowar ranar haihuwa Madinah ta kawo masa...

    Don haka don yau ya kira abokiyar fadansa da ‘darling’ bai ji faduwa ba ko kankani, karewa ma, har shirin fita ‘outing’ (picnic) na musamman ya yi niyyar shirya mata shima idan yazo, ko a TIGA DAM ko a DAMBATTA DAM, inda suka saba zuwa don ‘celebrating’ wasu ranaku masu muhimmanci da suka shafi dayan su.

    Sannan kuma gashi yana shirin ‘surprising’ dinsu su duka, domin a lokacin ya riga ya yanki tikitin tahowa gida kwatakwata, ba tare da ya gayawa kowannen su ba, tuni kuma yayi ‘booking’ din jirgin dare, bayan kwashe shekaru uku yana zullewa Mamansa Haj. maimuna, a kan dai maganar aure. 

    Yanzu kam da kwarin guiwar sa zai iso gida, kuma da abinda ya tabbatar zai baiwa kowa a gidansu kwanciyar hankali, abinda ya tabbata zai faranta ran Mama, ya kuma wanke bacin ranta da shi, wato maganar auren sa. Shi yasan inda abinda iyayensa ke so su ji a yanzu to bai wuce yayi aure hakanan ba, iyayen sa sun matukar daga hankalin su a kan rashin auren sa a wannan dan tsakanin ya rasa meyasa, ya manta shekaru talatin da biyu a wancan lokacin har ya wuce matakin samartaka, ya shiga na tuzuranci a al’adance, har hakan na neman ya shafi zaman lafiyar sa da su, don Mama ta dade da daina kiran sa a waya tace yayi abinda yake so tunda ya badawa idon sa toka ya ki auren diyar aminiyar ta Barr. Hannatu wato Sadiya Maijama’a, har wani ma sa’ar yayi wuf da ita (ya aure ta). 

    A yanzu kam Dr. Sarham Abbas yana cikin wani farin ciki maras misaltuwa. At last, at very long last, he found his first and true love, bama mai kama da ita ba, ba mai irin kokarin ta ko kamanninta ba (kamar yadda Mama tai masa fata), a’ah, ita din ce da kanta ba sako ba, wato (his ex) Madinah Attahiru ba wata ba! Kuma har sun daidaita sabanin dake tsakanin su, duk tsayin wannan lokacin na komawarsa Jeddah suna tare da Madina Attahirusun sake hadewa acan jami’ar sarki Abdul Azeez (KAU) Jeddah.

      ****                    *****                  ****

    

    WAIWAYE ADON TAFIYA (1)

      (DR. SARHAM SHANONO A JEDDAH) 

                      

    Abinda ya faru shekaru ukun baya shine tun saukar sa a birnin Jeddah cikin wani ikon Allah suka hade shi da ‘ex’ dinsa Madinah Sorondiki a cikin asibitin koyarwa na ‘KING ABDUL’AZEEZ’, inda duk a can ne dukkansu suke kara zurfafa karatu. 

    Ba zai manta ba kwanansa uku da zuwa ranar nan ya zo wucewa, kamar daga sama ya hangi Madina Attahiru tana shiga wata farar mota kirar ‘Audi’ don fita daga asibitin. Sarham ya mutstsika idon sa, don da farko ya dauka gizo idon nasa yayi masa, irin wanda dare da rana ya saba yi masa a kan ta, har saida ya dinga neman taimakon Ubangiji da sallolin dare kafin ya samu Madinah ta daina yi masa gizo a kowacce kusurwa ta dakin sa.

     A ranar da yayi mata wannan ganin a asibitin kusan karamin hauka yayi, bai iya yayi barci a daren ranar ba ko na minti daya, ‘fade memories’ na komai nasu a can baya ya dawo masa sabo, ya dawo da tsohuwar Madinah sabuwa a ran sa. 

    Amma a washegari da ya sake ganin ta, sai ya kuma tabbatarwa ba gizo idon sa ke masa ba, Madinah ce. Har yau bayan rabuwar shekaru bakwai, tana nan a Madinah ‘yar gayun ta. Fara, doguwar nan sambaleliya da ya sani hamshakiyar ‘yar hutu. Madinah siririya mai yalwar gashin ido dana gira, ta kara tsayi da cikar halitta, ga sabon aji na musamman data kara a kan wanda ya santa da shi a baya, ko dama can Madina classique lady ce balle yanzu da ta ke kusan shekaru Talatin. Tana takunta akan kasa cikin rangaji da rangwada tamkar basarakiya, tabon sallahr nan har yau yana nan a kan goshin ta, ya kara fitowa radau, shi ya kara tabbatar masa har gobe tana nan a “Madinah” mai yawan ibada.

     Madinah (Munawwararsa da ya sani) tuntuni mai aji ce, iyayenta sun wadatata da komai na bukatar rayuwa, balle yanzu da ya san ko yaya ta zama babbar likita tana aikin kanta kuma kallo daya zaka yi mata ka san hankalin ta a kwance yake, tana neman cika shekaru talatin. 

    Abinda bai sani ba shine tana da aure ko bata da shi? 

    Wannan tunanin, da kuma sanin halin mahaifinta da yayi, su suka sa yayi maza ya shiga taitayinsa, ya soma yaki da fade memories masu neman dawowa muhallinsu saboda ganinta. Sosai ya kama kan sa, bai bari ma ta san ya gan ta ba har bayan sati guda da ganin da yayi matan.

    Amma wani coincidence din, ashe ajin su daya a wannan karon ma, itama ta zo yin irin kwas din da yazo yi, duk a specialization nasu na ‘ophthalmology’. Bayan kwashe shekaru biyu tana practicing aiki a Dr. Siddiqah Hospital anan Jeddah.

    Ranar da yi mata gani na biyu da yamma ne, ya je shan Gahwah (coffee) a wani Mud’am dake cikin asibitin koyarwar nasu na Sarki Abdulazeez, bayan ya gama sha, ya tashi ya nufi kantar biyan kudi, ya zaro khamsoona riyals dinsa daga aljihu zai biya, kawai ya ji cashier din ya ce ai an biya kudin gahwar da ya sha.

     Ya juya cikin tsanaki da mamaki, nan yayi ido hudu da Madinah Attahiru, his ex Madinah Sorondinki, tana masa kallon ashe kana duniya? 

    Zuciyar sa ta harba. Makwallaton wuyan sa ya motsa, amma ya kasa hadiyar miyau. Donhaka wani abu ya tokare a wuyansa. Madinah muguwa ce ta karshe ya sani in dai akan soyayyah ne, idan ta samu dama zata iya kisa, har lahira kuwa, don haka nisa da ita shi ya fi wa bawa kamarsa kwanciyar hankali.

     Juyawa Dr. Sarham yayi cikin daure fuska kamar bai san ta ba, ya soma takawa don barin mud’am (restaurant) din gabadaya. 

    Madinah ta saki malalacin murmushinta, ta riga ta san halin kayanta bashi da jarumta in dai a kanta ne, tanada yaqinin bazata sha wuya ba wajen dawo da shi ruwa tsundum cikin soyayyah. Ba da sanin sa ba Madinah har sujjadah ta fadi ta yi a nan inda take zaune, (for the second phase) na rayuwarta ta sake haduwa da Sarham Shanono, a muhallin da ta fara haduwa da shi a can baya.

    Ta tako cikin kasaitar ta har inda yake tsaye yana shirin barin wurin shan coffee din, ba tare da ko an gode yace ba, daga abinda aka biya masa. Madinah ta sha gaban sa, ta kashe shi da murmushin nan nata kamar na koren furen fulawa, da ya dade da daina gani, zuciyar sa kuma bata bar mararin ganin murmushin ba all those years, Madinah ta ce,

     “ai in da alkawari zai zamanto cewa ko gaisuwar musulunci ce akwai a tsakanin mu Dr. Sarham, idan ta SO da KAUNA ta gushe ko tayi fading, a matsayin mu na dalibai duka, sannan ‘yan kasa daya kuma ‘yan aji guda, dana tabbatar abinda nazo yi shi ka zo yi, ba laifi bane don hanya ta hada mu mun tsaya mun yi gaisuwar musulunci”. 

    Wannan karon ma bai yi niyyar bata amsa ba yasa kai zai wuce abinsa, a ran sa yana fadin “Allah ya shiga tsakanina da ke Madinah!

     Mumini na kwarai sau daya maciji yake saran sa a rami guda”. Amma sai Madinah bata yi fushi ba, ta sake shan gaban sa. Ta ce, 

    “Assalamu alaykum warahmatullah wa barakatuhu!”

    Kamar yadda ta dade da sani, Sarham Abbas nada wani hali daga halaye masu kyau, wato baya iya maida gaisuwar musulunci a kwandon shara, ta hanyar kin amsata, wato duk inda ya ji ta sai ya amsa koda ba da shi ake ba, ba don komai ba sai don cika sunnar Manzo SAW. 

    To yau ma hakan ce ta faru kuma yanzun ma. Sarham ya kasa kin amsawa don cika umarnin addinin musulunci, sai ya ce kasa-kasa kamar yaci madaci,

    “wa alaykumus salam warahmatullah wa barakatuhu”.

    Daga wannan sai aka shiga kallon-kallo, koko in ce ‘kallon kuda’ kallon debe shakku ko debe tsammanin gizo ido ke yi, kallo ake babu ko kiftawa haka babu kakkautawa tsakanin SARHAM DA MADINAH. Suka yi wa juna kiriii da ido.

     Kallon da ya dawo masa da duk abinda ya faru cikin shekarun soyayyar kurciyar su kan idon sa, koko ince, kan idon kowannen su, komai da ya gabata (in the past) ya zo yana gilmawa a idanun kowannen su, tamkar yadda sinasinai ke wulgawa a majigi, suna tariyo kan su, suka kuma shiga warware tsohon kullin dake zuciyar Sarham akan Madina, tamkar ana tariyo tsohon kaset na faifan bidiyo. 

    A hakikanin gaskiya Sarham na kullace da Madinah kullata mai yawa, wadda ta janyo ya maida kansa ba namiji ba, ta hanyar daina sha’awar soyayya da sha’anin mata gabadayansu.

     Madinah tasa ya hada su itada sauran matan duniya yayi musu kudin goro da cewa dukkansu maciya amanar kauna ne, kuma basu san darajar soyayya ba, mata irin Madinah in ka bari ka fada komarsu zasu iya kashe ka har lahira akan soyayya.

     Yana tuhumarta ne da rashin alkawari da cin amanar kaunar da suka yi wa juna. 

    Son data ke ikirarin tana yi masa yayi ittifakin ko kusa bai kai rabin nasa ba, shiyasa ta iya bari har aka raba su cikin matukar sauki haka, kamar kwace goriba a hannun kuturu.

     Abu daya ya sani kuma yake da tabbacin sa; Madinah Attahiru, bata taba raina shi ba, wai don shekaru biyu ko uku kawai ya bata a haife, Madinah bata taba raina arzikin mahaifin sa ba, wai don bai tara dukiya kamar nata mahaifin ba, baya ga kasancewar sa malamin makaranta/malamin jami’a.

     Yana son Madinah har gobe, domin ta hada duk wasu halaye na kwarai da nagarta da kyawun sura dake sawa a so mace, a yi mata So na musamman. Duk wasu ‘attributes’ da yake so a matar aurensa Madinah ce ta hadasu ita kadai ranta.

     Ya ci buri mai yawa a kan Madinah Attahiru, haka ya sha wahala lokacin da ya rasa ta farat daya. Haduwar su ba zato a yanzu, karo na biyu cikin shekarun girmansu, a lokacin da suke da cikakken hankalin su bata nufin komai sai fami a kan gyambon da riga ya warke.

    Kafin wannan lokacin sun yi alkawarirrika masu dimbin yawa shi da ita, kai har yawan adadin ‘ya’yan da suke burin haifa ra’ayin su ya zo daya, wato ba masu yawa ba, shi da Madinah kamar Lailah da Majnoun ne. Daga cikin manyan alkawuran su na can baya, har da na yin aure daga zarar sun kammala MBBS, koda basu samu ayyukan yi ba a Jeddah, sun ajiye a ransu zasu yi ko ayyukan philanthropy ne a private clinics na Jeddah don rufa asirin juna indai zasu rayu tare. 

    Rana daya Madinah bai san ya aka yi ba, bai san me ya faru ba Madinah ta yarda mahaifin ta ya ci zarafin sa, ya kuma canza mata makaranta, duk dai don ya raba su, ya rasa mai yasa Baban Madinah ya ki jinin sa ya kuma raina arzikin su shida iyayensa har haka, tunda daidai gwargwado iyayensa nada abin yin su, da rufin asirin su basa nema a hannun kowa, ko da yake ya taba gaya masa fuska da fuska;

     “me na sama ya ci bare ya baiwa na kasa? Kuma yayi yarinta da auren ‘yarsa a lokacin” Shine kawai hujjarsa.

     Babban laifin da Madinah ta yi masa shine, bayan an canza mata makarantar, bai kara ji daga gareta ba, Madinah bata kara waiwayarsa ba, bata kara neman sa ba, koda da gaisuwar zumunci ne. Ai yasan Madinah nada email adireshinsa, da adireshin sa na gidan wasika, da lambar talfon din gidan su, amma ko sau daya, bata taba tunanin gwada neman sa ba, wanda ke nufin ta datse duk wata alaqar soyayya da sanayya dake tsakanin su.

     Koda ba don maganar alkawarin aurensu ba, ai ta nemi inda yake ta ji yana raye ko ya zarce ta dalilin kisan gillar soyayar da suka taru suka yi masa itada mahaifin ta, tunda dai ta kwana da sanin irin son da yake mata, ba irin wanda zai gushe farad daya bane.

     Wannan shine babban laifin da Madina tayi masa da ba zai yafe shi ba wato kin neman sa ko sau daya cikin shekaru bakwai da rabuwarsu, tun bayan komawar ta Yamboa inda a can tayi nata consultancy din, tsayin shekaru biyar, da komawar sa shima zuwa gida Najeriya na dan wani lokaci, inda daga baya ya dawo shima yayi consultancy dinsa ya sake komawa gida.

     Wanda ya yi shi ne da kyar da sudin ludayi shikadai a [KAU] a dalilin rashin Madinah tare da shi.

     Saboda tunda suka fara MBBS suke tare, har zuwa karshen sa. Karatun dukkansa, da aikin gida (assignment) da halartar lacca duk tare suke yin komai. A lokutan jarrabawa kuwa duk zaka same su tare a library, sun dukufa basa komai sai fatan isa ga ‘goal’ din rayuwarsu. Don haka shekaru goma kenan ya kwashe a cikin hidimar dakon son Madinah Sorondinki, idan har lissafin sa daidai ne; yayi shekaru biyar tare da ita cikin fafutukar hada MBBS, shekaru biyar kuma cikin jinyar soyayyar ta, lokacin da yake consultancy, tun bai san so ba akan Madina ya koye shi, wato tun farkon tashen balagar sa da soyayyar Madinah ya budi idanu. 

    

    Wannan shine tarihin soyayyar su shi da Madinah wanda ya tuna a wannan ‘yan dakikan da suke kallon debe tsammani shi da ita.

    ****               ****                 ****

    

    Da tunanin sa ya zo nan, sai ya dauke kai daga kallon kudar da suke yi wa juna, ya juya da zummar cigaba da tafiya ya bar ta a wurin, ba tare da ya kara tankawa ba. 

    Madinah bata yi fushi ba, ta hakurkurtar da ranta da cewa fushin fari ba nata bane, Allah na nufin su da wani al’aamri maigirma da ya sake hada su (at appropriate time), ta sake biyo bayan sa jiki babu karsashi, yana saka kafa tana mayas da tata duk inda ya cire tasa, cewa tayi cikin muryar dake raurawa.

     “Sarham, yaya bayan rabo?” 

    Cikin dakiya da tsare gida yace “bayan rabo kuma? Sai tarin alkhairi” “Kamar baka gane ni ba?” Madina ta fada kamar zata fashe da kuka wannan karon, idanun ta na kallon kasa, sun kasa rike hawayen yanzu, suna cigaba da tafiya zuwa dakin karatu, hawaye na tsirgo mata. Sarham yace.

     “Madinah kenan, ni kuwa na gane ki, ko ba Madinah Attahiru diyar masu Bankin Musulunci na Duniya bace? Idan na gane ki sai me hakan zai kare ni da shi, ni Sarham dan yaku-bayi?”

     Madinah tana hawaye tace “zaka iya fadin komai a kaina ba tare da na ga laifin ka ba Sarhm, laifi kan laifi na san na yi maka amma ina da DALILI na. 

    Abu daya nake so ka gane yanzu, Daddyna daka sani a da can, to bashi bane yanzu. Wannan sabon Attahiru SoronDinki ne, wanda duniya ta biyar dashi, yanzu ya gane cewa rayuwar kanta da dan adam kansa komai mukami da mulkin sa, da dukiyar da yake tinkaho duka ba a bakin komai suke ba.

To cut it short, Daddyna ya dade yana neman ka ido rufe domin ya nemi afuwar ka, ya kuma baka damar da ya dade yana hana ka”.

    Murmushin da Dr. Sarham Shanono yayi irin wanda yafi kama da a kira,

     “na dade da baiwa wannan tatsuniyar baya” ne. 

    A fili kuma yace “Madinah Soron Dinki, takamaimai me kike so da ni yanzu a takaice, da yasa kike min wannan binbinin haka?”

     Ai jin haka Madinah ta tabbatar yanzu kam Sarham ya gama da babin ta, yau ita Sarham ke cewa tana masa binbini! Wannan ba Sarham din data sani a baya bane halinsa duk ya canza, wancan jovial ne mai saukin kai da dadin sha’ani, ko dai wani ne mai tsananin kama da shi da irin sautin sa ta gamu da shi saboda yadda ta saka shi a ranta???

     Sai kawai Madinah ta durkushe anan inda take tsaye, cikin korran grass carpet (ciyayi) ta saki kuka mai cin rai.

    A can zamanin baya Sarham ba abinda ke daga masa hankali irin damuwar Madinah Attahiru, amma wallahi yanzu bai ji ko gezau ba wai an tsikari kakkausa, ya yi kuka har fiye da wannan da take yi yau akan rashin Madinah, da kuma wulakancin da mahaifin ta yayi masa ranar da yace “ba zai taba baiwa dan almajirin gwamnati (dan malamin makaranta) ‘yar sa ba”.

     Ita nata kukan kuwa a yanzu ai na jin dadi ne, abinda bai sani ba, kukan Madina yau ya kunshi abubuwa masu dimbin yawa, har da wadanda tunanin sa da tsinkayen sa bai bashi ba. 

    Bata taba daina son sa ba, a duka wadannan shekarun daidai da rana daya, ta yanke alaqar su ne domin ta samu damar yin biyayya ga mahaifin ta, wanda ba abinda bai yi mata a duniya ba, ya kuma fifita soyayyar ta akan ta ‘yan uwanta maza bakidaya kasancewar ita kenan masa diya mace, kuma auta a cikin ‘yan maza bakwai. Wannan shine dalilin nata.

Sarham bai tsaya Madinah ta gama kukan bay a cika bujensa da iska ya bar wurin, sai dagowa tayi bayan ta share hawaye ta neme shi a filin wajen ta rasa.

A lokacin ta cigaba da tuno rayuwarta ta baya tare da Sarham, abinda ya faru shekaru bakwai da suka gabata, ta tuno asalin ta, haduwar su, lokutan su tare a campus, da abubuwan da suka faru da ita bayan rabuwar tasu…….

              ****               *****        ****



     WAIWAYE ADON TAFIYA! (2)

      DR. MADINAH ATTAHIRU                    

A

salin mahaifin ta Bakano ne dan asalin Soron Dinki, Soron Dinki wata karamar unguwa ce mai tsohon tarihi a jihar Kano, wadda ta haifi fitattun malamai da alkalai a tarihin jihar. Tana nan dab da gidan Sarki (Emir’s Palace). 

    Mahaifin Attahiru wato Kakan su Madina tsohon Alkalin Alkalai ne na jihar Kano kuma fitaccen mutum akan sha’anin shari’ah a Kano. Tun a tsakiyar shekarun 80’s Attahiru Habibu Sorondinki ya tafi Jeddah kan wani kwas na aikin Banki, tare da matar sa Hajjah Ramlah da manyan ‘ya’yan sa maza uku a lokacin, Abubakar da Omar, da Osman inda daga wancan lokacin ya fara aiki da wani tsohon bankin kasar ta Saudi-Arabia.

    Da tafiya tayi tafiya, zamani na garawa da shi a harkar aikin banki a can, har zuwa lokacin da aka bude ISDB wato (Islamic Development Bank) Allah kuma ya zabe shi ya kai shi ISDB a babbar ‘headquater’ din su dake birnin Jeddah. Ya rike kananan mukamai da dama a cikin ta, kafin ya iso wannan matakin na yanzu. Domin kuwa a halin yanzu mahaifin na Madinah Alhaji Dr. Attahiru Soron Dinki yana rike da matsayin (Chief Financial Officer) na ISDB. Alh. Attahiru na auren Hajjah Ramlah, wadda ta kasance ‘cousin’ a gare shi, ta cika masa gida da kyawawan ‘ya’ya maza har su hudu, Abubakar, Omar, Osman da Aliyu, a Kano ta haifi manyan su uku, wato Abubakar, Omar da Osman. Da suka zo Jeddah ba jimawa ta haifi Madinah da Aliyu anan.

     Akwai ratar haihuwa sosai tsakaninta da Osman kafin su samu haihuwar auta “Madinah”. Daga Abubakar har Umar har Aliyu da Usman ma’aikatan bankuna ne a kasar Saudi-Arabia, saboda mahaifin su dake da wuka da nama a harkar aikin banki.

An haifi Madinah ne a garin Madinatul-Munawwarah lokacin sun je aikin omrah duk gidan, shi yasa Baban ta ya kira ta da suna Madinah.

Madinah ta ga gata tun daga haihuwar ta har girman ta, Madinah bata taba sanin wahala ko babu a rayuwar ta ba, ta tashi a gida na ilmi da tarin dukiya, wanda ya sa koda ta shiga jami’a maza ke rububin ta, da yawa ko don su rabi alfarmar ISDB, da yawa kuma saboda kyawun ta ne. 

    Amma wani ikon Allah babu wanda tasu ta zo daya irin coursemate dinta Sarham Abbas Shanono, wani siririn sardidin yaro, dan ajinsu, wanda ta fahimci yafi kowa a ajin su kokari, kamun kai da kula da abinda ya kawo shi, shima kuma ya fahimci Madinah Attahiru tafi duk matan ajin su kokari, ga aji ga kasaita kamar wadda ta hada jini da sarauta, amma shi bata yi masa ko daya sai ma wani ‘special respect’ da take bashi, sai suka hade daga haka, suka zama abokan karatun juna, daga abotar karatu da karawa juna sani abin nasu ya fara, kafin ba da jimawa ba ya rikide zuwa zazzafar soyayyah wadda ta isa a bada labarin ta a ko’ina, amma irin soyayyar nan ta sa’annin juna. Wadda bata fiya ‘actualizing’ ba. Domin kuwa shekaru uku kacal Sarham ya baiwa Madinah Attahiru.

Duk da kasancewar Madinah irin mutanen nan da basa so ka shiga harkarsu, masu halin da kai tsaye za’a ce na nasara ne kamar ba tashin Saudi Arabia ba, amma duk da wannan hali nata bata da wulakanci da raina mutane. Personality dinta kawai za’a ce na nasara ne (musulma mai halin nasara), tanada wani zazzafan hali na kada ka sake ka shiga harkar ta, itama kuma bata shiga harkar kowa, saboda mugun jan ajin ta, ta kasance mace ‘yar I don’t care attitude. 

    A hali iri na Madinah ko kai waye wajen isa, ko wane irin laifi kayi mata, ko wane irin aibu kake da shi, Madinah bazata zauna tana gulmar ka da wani ba, tafi karfin haka, saboda she is frank, bata iya boye me take ji akan mutum, zata tare ka ne gaba da gaba ta gaya maka, da dai ta zauna tana zunden ka da wani.

     Wato dai a takaice Madinah bata iya munafurci ba, sannan bata so a yi mata. 

    Wadannan halaye nata sun taimaka kwarai wajen ribato zuciyar kyakkyawan Bakanon matashin Sarham Shanono a kan ta, babban jigon son da ya samu kan sa da yi mata shine yadda gatan data ke da shi bai hanata tsayawa tsayin daka wajen yin karatun da zai amfani al’umma ba.

Sarham Abbas da Madinah Attahiru duk abokanan karatun su na MBBS sun san su tare, ko’ina tare suke zuwa, soyayyarsu mai tsafta, mai ban sha’awa ta ‘yan bokon da, ba irin ta wannan gurbataccen zamanin ba, Madinah kullum kawo ta ake a kuma zo a dauketa a motar gidan su, shikuwa a nan kusa da makaranta ya kama hayar gida mai daki biyu (flat).

Sun tsayar cewa da zarar sun yi bikin kammala karatu zasu yi aure, Madinah ta yarda zata bi Sarham Najeriya ta zauna cikin iyayen sa da kannen sa duk da cewa itada kasar Kano sai da ziyarar dangin su kawai su kan shigo ta, ita dinma sai suyi shekara hudu-biyar basu zo ba.

    A wani dan tsakani da ya kasance sun kusa zana jarrabawar karshe a MBBS Madina ta baiwa Sarham iznin fara zuwa zance gidan su, ba don komai ba sai don iyayenta su san da zaman sa, kasancewar soyayyar tasu iya makaranta suke yin ta ba wanda ya san shi a gidan su har zuwa lokacin banda Yayan ta Osman dake zuwa kawota da daukan ta. 

Zuwa na farko, na biyu dana uku Alhaji Attahiru ya fahimci akwai mai zuwa wajen Madinahr sa, Hajjah Ramlah ma ta gaya masa wani ya fito neman auren Madinah amma bata san ko waye ba, saidai ga dukkan alamu Madinah tana yi da shi, ko daga girke-girken da take faman yi masa in zai zo.

    Daddy ya umarci Madinah data turo masa yaron dake zuwa wajen ta yana so zai yi magana ta gemu da shi, ba tare da tunanin komai ba a washegari Madinah ta gabatar da Sarham a tankareren falon mahaifin ta, daga nan ta basu wuri don su gana.

Sarham yayi wani kuskure zai ce ko katobara, koda yake a wurin sa is normal, wato yawo da farar jallabiyya ta larabawa a garin Jeddah, maimakon da zai je gun siriki yayi shiga ta cika ido da kima sai yasa jallabiyyar sa abinsa wadda taji wanki da guga da turaren sa na Oud Abyad. Kallo na farko da Alhaji Attahiru yayi masa yaga yarintar sa da rashin cika ido, sannan kuma babu tantama dan talakawa ne ko daga sittirar jikinsa amma duk da haka bai yanke hukunci daga abinda ya ganar da kansa ba, sai da ya tambayi Sarham.

“Yaro kai dan ina ne?”

“Kano”

“wane gari a Kano?”

“Shanono”

“Waye mahaifin ka?”

“Prof. Abbas Shanono”

“daga jin Farfesa malamin Jami’a ne kenan?” 

“Eh!”

“to kai kuma meye taka sana’ar?”

“dalibi ne ni”

“Dalibi dan Farfesa, ilmi na dukan ilmi, amma dame ka shirya rike min ‘ya ta yaro da kai haka? Ko bata fada maka daga gidan data fito ba?”

    Sarham ya kasa hadiyar miyau, don bai zaci wadannan kalaman marasa kan gado daga babban mutum mai ilmi kamar sa ba, Daddyn Madinah ya cigaba da cewa “yaran zamani in zaku yi abu sam sam ba kwa tunani, yo me na sama ya ci bare ya baiwa na kasa?

     Yaushe zan ajiye ‘ya ta zaman jiran girman ka da yin arzikin ka kafin inyi mata aure?

     Ai kawai yaro kaje ka nemi daidai kai diyar malaman makaranta”.

    Sarham hatta jijiyoyin kansa saida suka mimmike, suka fito rada-rada, tun kafin ya tashi a wajen ya gayawa ran sa ya hakura da Madinah ko itace autar mata, don mai taba Abban sa ya zauna lafiya a hannun sa sai dukan ruwan sama. Shima don ba zai iya rike shi daga taba jikinsa bane.

Duk da haka wannan tsohon baturen zai ce ko tsohon nasara ya ci arzikin Madinah-Munauwarah. Amma da ba haka ba?! Da yayi masa raddi daidai da nasa. Ya girgiza kai ya mike. A kullum Madinah na cin alfarmomin sunan ta a wurin sa, wato, yana son garin Madinah sosai, duk sati biyu yake ziyara Masjid Nabawy daga Jeddah, don haka ko cikin hira yana gaya mata cewa tana cin albarkacin sunan ta na Madinah garin Manzo, garin da ya zamewa Ma’aiki (SAW) mafaka (refege) kuma wajen yin hijira daga inda yayi masa kunci, don haka sau tari ya kan ce da ita, ko sunyi aure ta bata masa rai komai girman laifin zai iya yafe mata shi saboda sunanta, zata cigaba da cin albarkar city of Madinah, za kuma ta cigaba da samun wannan alfarmar har gobe a wurin sa.

Don haka bai ce komai ba baya ga godiya ga mahaifin Madinah da barin gidan su ba tareda ya tsaya Madinah ta ga yanayin sa na lokacin ba.

    Shi uban da kansa ya gaya mata ya sallami wannan yaron, in bata da hankali shi da hankalin sa, ba daga turu aka fito da shi ba, kuma ta sani daga yau ta bar King Abdul Azeez University kenan, don ya fahimci irin ‘ya’yan talakawan nan ne masu hurewa ‘ya’yan manya kunne da ‘I love you’, su dau advantage na iyayen su don su samu abin yi mai maiko, in sun kama kasa su auro daidai su, ‘ya’yansu su koma na ladan noma.

Madinah couldn’t control her tears, ta bi bayan Sarham da gudu amma bata cimmasa ba. A washegari kuma Babanta bai barta ta koma [KAU] ba, yasa Abubakar ya karba mata ‘transfer’ zuwa Yamboa ya kuma je ya kaita da kan sa, yace in ta kara neman wannan yaron ko a waya kota wata kafar sadarwa kowacce iri ce zai saba mata ko ya bar kasar bakidaya da ita.

Madinah na matukar son birnin Jeddah don anan aka haife ta, amma haka Baban ta ya raba ta da shi saboda Sarham zuwa Yamboa.

    Madinah na matukar son Sarham, so irin wanda bazai misaltu ba, amma haka ta hakura da shi saboda ta yiwa mahaifin ta biyayyah.

    Madinah na matukar son mahaifin ta shiyasa ta zabi farin cikin sa a kan nata, wato ta zabe shi akan soyayyar dake zuciyar ta, ta kuma bi umarnin sa.

    Wannan kadai ya nuna Madinah mai biyayyar iyaye ce ta kuma ci ribar biyayyar tun a lokacin, domin duk da zuciyar ta tafi dare duhu, amma haka mahaifin ta yayi ta saka mata albarka, yana ankarar da ita illar auren ‘ya’yan talakawa gasu yara masu gata kuma ‘ya’yan manya kamar ta, yace basu da alkawari ‘yan taking advantage ne kuma basa juyuwa ta sauki ga matan su, taurin kansu kadai dafadin rai ga matayensu sai ta gwammace kida da karatu, sannan basa taba zama da mata daya.

Duk Madinah tayi biyayyah ko a fuska bata taba nunawa mahaifin ta har lokacin Sarham yana ranta ba. ta kuma san duk abinda ya fada akan Sarham ba haka bane, Sarham akasin duka wadannan expectations dinne.

Sai ta tattara komai ta fauwalawa Allah ta maida hankali ga fuskantar karatunta a jami’ar Yamboa, ta manta da komai, a shekara daya da Sarham ya gama nasa karatun itama a shekarar ta fita daga Yamboa University, ta fita da flying colours a specialization nata, ta zama cikakkiyar likitar fidar ido (ophthalmic surgeon) mai lasisin yin aiki a kasar Saudi-Arabia. 

    Shima Sarham ya fiddo nasa kwalin daga (KAU), ba tare da sanin me kowannen su yake ciki ba. Daga nan ya tattara ya koma gida. Inda ya kama aiki a karkashin gwamnatin jiharsu.

A lokacin ne AVM Adamu Alkali ya fito neman auren ta.

Ba kuma ta kanta ya bi ba, ya tafi ne kai tsaye ta kan mahaifinta, shikuma a sanin irin biyayyar da Madinah keda ita bai bata lokaci wajen neman yardarta ba, saboda wannan shine daidai da ra’ayin sa, irin mijin da yake mata fata yake mata addu’a, gashi Allah ya bata a lokacin da ya dace tayi aure, miji wanda bazai yi kaico da aura masa ita ba, wato na saman da ya ci ya hantse yake watsowa na kasan sa, dama duk wadanda ke jikin sa koda sun kasance suma masu wadatar ne.

Don haka Daddy bai ja lokaci mai yawa ba wajen sanya auren Madina da AVM (Air Vice Marshall A. Alkali), wanda shima dan Kano ne gaba da baya, amma mazaunin jihar Lagos, inda a can yake aikin sojan saman sa.

         ****                *****                   ****


L

okacin da mahaifin ta yayi mata bushara da hakan, wato ya gaya mata da bakinsa ya saka auren ta da AVM Alkali, Madinah ko tada kai bata yi ba balle ta ce a’ah, saidai bayan maganar da kwana biyu ta kwanta zazzabi mai zafi, wanda har ya kai ta da kwanciya a asibiti.

     AVM yayi amfani da wannan damar ya zo duba Madinah, ranar ne ma ta fara ganin sa a gadon asibiti, ba wani kallon kurilla tayi masa ba amma ta fahimci babba ne sosai, ba za dai tace sa’an baban ta bane amma hakika ya manyanta don zai girmi babban Yayansu wato Yaya Abubakar, babu mamaki ya aje diyar data kusa giramanta.

Madinah ta dauke kai daga duban sa, yayi mata sannu da jiki ta amsa fuska ba yabo ba fallasa, babu wata fuska da zai neme ta da zance, dole ya gabatar da kan sa ya tafi. A washegari manya suka tsayar da ranar daurin aure.

Sadakin Madinah kawai da aka kawo dankunne ne da sarka na ‘Emerald’ wato koren yaqutu, sannan AVM ya yi alkawarin ‘launching’ sabon asibitin ido nata na kanta da zai bude mata a jihar Lagos inda zata zauna da zarar ta sauka a kasar Najeriya.

Iyaye nata shirye-shirye ta kowanne bangare ka’in da na’in, haka ta fannin matar AVM wato Hajiya Juwaira itama tana ta shirin zuwan amarya don ta saba da shiga ta fitar su shiyasa bata ko damuwa idan yace zai kara aure. Amaryar kuwa a lokacin duk da shekarun nan masu dama da suka gabata zuciyar ta na ga Sarham.

     Tarihi ba zai manta da soyayyar su ba, amma babu tantama da zuciya daya yau ta hakura da Sarham da aka damka sadakinta, ta yarda zata auri zabin mahaifin ta. 

    Aka daura auren DR. MADINAH ATTAHIRU da AVM A. Alkali a wata ranar juma’ah, a masallacin Haraam, bayan saukowa sallar Juma’ah, iyaye da dangi aka shiga shirin biki na garari da kasaita kafin lokacin da za’a mika amarya nanjeriya.

Daddy yace ma AVM shi da kan sa yazo ya tafi da amaryar sa bayan kammala biki kenan, bai yarda da mata su rakata zuwa kai amarya Lagos ba irin yadda ake yi a al’adar Kanawa.

Air Vice Marshall Adamu Alkali Sambo, ya biyo jirgin su na sojin sama zuwa birnin Jeddah, irin jirgin su na helicopter, jirgin ya fadi a wani tsibiri/tsauni. A cewar wasu kuma ‘yan uwan sa sojojin sama ne suka harbo jirgin nashi bisa wata matsalar aiki da suke ciki da shi da su kadai ta shafa kuma su suka santa. 

    Koma dai yaya ne an tabbatar babu wanda ya fita da rai a wannan hadarin jirgin saman daga shi har staff dinsa guda hudu da matukin jirgin na biyar.

    ****                      ****                    ****

    

“Innalillahi wa’inna ilaihirajioun…”.

In ji Daddy, kafin ya saki kan wayar a kasa ya durkushe akan kafafun sa, Hajjah Ramlah na tambayar ba’asi amma ya kasa gaya mata mijin Madinah yayi hadarin jirgi akan hanyarsa ta zuwa daukan ta.

     Madinah wadda aka gama shiryawa cikin ‘SARI’ na ainahin matan indiyawa, hatta bular nan ta dankunne a hanci an yi mata da karfen zinare, ta zama kamar ba’indiyar gaske, dama tana da irin suffar su, isowar AVM kawai ake jira su daga Najeriya, sai ga Baban ta ya shigo dakin afujajan, yace mata “Madinah kiyi tawakkali”, Dady ya nisa kafin ya sake cewa “Ya ke ‘ya ta mai albarka, Allah ya karbi AVM”.


Albarkar da har gobe ta tabbatar tana bibiyar ta, domin watanni goma bayan rasuwar AVM A. Alkali, ba tare da ta yi masa ko gani na uku ba, mahaifin nata da kansa ya kira ta, har zuwa lokacin bai gama fita daga ‘shock’ da firgicin mutuwar AVM ba, wanda har ciwo ya kwantar da shi, ya kuma maida shi salihin bawa akan yadda ya dauki duniya a baya. 

    Ita kuwa Madina duk da taji mutuwar, tofa bata kara saka wani tunani na daban akan rasuwar sa ba, bayan na tunanin zuwa karo zurfin ilmin ta a KAU, don har zuwa lokacin ruhin ta bai bar makarantar nan tasu ta baya ba. 

    A yau da Daddy ya kirata dakin sa domin su yi magana ‘heart to heart’ irin ta Da da mahaifi shi da ita, ta zauna tankwashe da kafafu a gaban sa.

Ya fara da neman gafarar ta, kafin yace “na so in yi abu na son zuciya ta, gashi duk yadda naso faruwar sa Allah bai kaddara gidan ki bane ba.

     Gashi ya yanke hukuncin da ya san yafi daidai da rayuwarki. 

    Na sani Madina biyayya kawai kike yi min, amma zuciyar ki naga wancan yaron, don haka yau bisa umarnina, na amince ki nemo wannan yaron Sarham a duk inda yake, in har yanzu yanada niyyar auren ki ya zo zan bashi. Bana neman ko kwandalar sa”.

     Madinah ta girgiza kai ta ce “Daddy! Ai ni tuni na hakura da Sarham, na dade da mantawa da shi, kai ma ina rokonka ka manta da shi, ka sake yi min duk mijin da kaga dama, da yardar Ubangiji wannan karon ma bazan baka kunya ba”.

    Shi kuma ya dage Sarham zata nemo, bas hi ba kara yi mata auren dole, auren soyayya yake son tayi wannan karon, da wanda zuciyarta ta aminta da shi, ba auren biyayyar sa ba.

    Madina ta yi masa rantsuwa kan bata ma san inda Sarham yake ba a yanzu, don haka tana rokonsa alfarmar ya barta ta koma karo karatu a King Abdulazeez University. 

          Shikuma babu ja’inja ya lamunce mata, yana mai saka mata albarka.

    Mafarin dawowarta KAU kenan, sai gashi ko sati bata yi ba ta hange shi a zaune a mashayar coffee, yana jira a hada a miko masa. Madinah ta mike ta je ta biya kudin coffee din tun kafin ya gama sha ya tashi.

    

    “SARHAM!!!”

     

    Madinah ta fada a hankali, bayan gushewar shekaru bakwai yau ta sake sanyashi a idanun ta, duk da canzawar halittar sa bazata taba kasa gane shi ba.

    Wannan sirantakar da rashin kumarin, yanzu duk sun hade da tsoka da muscles, ta bada surar kakkarfan matashi lafiyayye mai wadatar jini a jika. 

    Wanda zuwa yanzu zamu iya cewa ya gama samun rayuwa daidai da burin sa, hankalin sa a kwance yake, saboda tsarin rayuwar sa ta masu tsantseni da gudun duniya ce tun sanin data yi masa, ba wai irin ta tara yaki halal yaki haram ba, sun tsaya ga iya gumin su, sun tsaya ga cin halal da moriyar ilmin su kadai.

    Yayi jiki daidai misali wanda ya karawa tsayin nasa haiba, ya tashi daga siririn yaron nan zuwa (handsome man), son kowa, kin wadda ta san ba zata samu ba.

Madinah (couldn’t control her tears) wadanda (emotion na radadin soyayya) yayi sanadin zubowar su, a lokacin da zai bar wurin ne ta bi bayanshi shine ya yi mata wannan yarfawar. Shin meye laifin ta a duka wannan tsarin da Ubangiji ya yiwa rayuwar ta? Me tayi ma Sarham da yayi zafin da gaisuwar musulunci ma sai da kyar zai amsata tsakaninsu?

    Ba mai bata wannan amsar sai SARHAM din. Ta sani bai dace ta bi shi har gidan sa ba, kai baima dace ba mace kamar ta ta dinga bin namiji komai tinkahon sa yana yarfata irin haka, balle ita Madinah Attahiru, da bayan aji har ajujuwa gare ta. Amma haka ta take PRIDE din nata, da kafarta ta taka zuwa gidan da ta san acan yake da zama, bata da tabbacin har yanzu acan din yake, ko kuma ya canza gida, amma dai tace bari ta fara duba can din ko zata dace. Ubangiji da kan sa yace “SULHU ALKHAIRI NE!” 

     

     To gata ta zo neman sulhun abin kaunar ta yau da kafafunta, kamar yadda tasan tana cin alfarmar sunan ta kullum a wurin sa, haka yau ma take da wannan kyakkyawan fatan, tana da yaqinin wannan karon ma zata ci wannan alfarmar daga gareshi, wadda tafi ta koyaushe girma a wurin sa, wato ya sauke fushinsa ya tsaya ya saurareta ko na minti biyu ne albarkacin sunanta da yake girmamawa na MADINATUL MUNAWWARAH… Madinah garin Manzo, Madinah mafaka ga dukkan musulmi, duk da tabbas ta san an bata masa, kuma laifi kan laifi ta san ta yi masa. Ko tace sun taru sun yi masa itada Daddy dinta.

Ilai kuwa tana tura karamin gate din ta hange shi daga can saman bene, tsaye a jikin balcony, ya harde hannayen sa a kirjin sa ya juya bayan sa daga kofar shigowa, don haka bai ga shigowar ta ba, da alama yayi zurfi a cikin tunani.

     Madinah tana tura kofar cikin sa’a ta taddata a bude, don haka kai tsaye ta sa kai, ta kuma haura ta matattakalar benen ta cimmasa har inda yake. 

Kamar cikin mafarki, kamar kuma irin gizon da ta saba yi masa cikin ido biyu, haka ya ga Madinah Attahiru tsaye a gaban sa, (for the second phase) na rayuwar su. Tana sanye da shudiyar abaya kirar Dubai da mayafin ta, ya sha mamakin biyoshin data yi, a irin sanin da yayi mata wajen tsare mutuncin ta da tsare ajin ta, wato tun saninsa da ita… maintaining self-esteem dinta yana sama da komai a gareta, a kuma irin yarfawar da yayi mata dazunnan.

     

    Wadannan, dama wasu dalilan, su suka sa ya kasa wofintar da ita, ko bar mata wajen kamar yadda yayi niyya da farko. Musamman ganin kyawawan idanun ta sun cika taf da kwallah, gab suke da ballewa bisa sassalkan kundukukinta, tace cikin rishin kuka.

    “Yau ma in ci albarkar garin MADINAH……Madinah garin Manzo, in ci albarkar kasancewa ta MADINAH AL-MUNAWWARAH, mafaka ga kuncin dukkan musulmi, a lokacin da suka shiga cikin matsin mushrikai, da abokan gaba, suke neman inda zasu samu tsaro da kwanciyar hankali, Madinah ta zamo mafaka ga Manzonmu (SAW), don haka nake rokon albarkacin ta ka saurare ni, ka bani mafaka daga kuncin zuciyar dana ke ciki a cikin kirjina”.   

Bai ce komai ba, amma a fuskarsa wannan karon akwai sassauci, a idanun sa wannan karon akwai rahma, kai har da wani boyayyen sirrin da baya so ta ankara da shi. Yace.

     “Me zan saurara daga gareki Madinah? Kada ki manta ni Sarham ba kowa bane, ba kuma dan kowa ba, dan Malaman makaranta ne, wadanda basu aje ba, basu kuma ba wani ajiya ba,” Madinah ta runtse ido kalamansa na mata zafi, tace “ka saurare ni ko na minti biyar ne, in labarta maka duk abubuwan da suka faru dani a lokacin”. Sarham yace “abu daya zan saurara daga bakin ki shine, meye DALILIN KI na kin nema na duk tsayin wannnan lokacin?”

     Madinah ta ce “ban da dalili, bani da hujjar kare kaina” “then why are you here?” Tace “saboda in baka hakuri, in kuma kai ka gaban Daddyn nawa, don ya dade yana neman ka, ya gana da kai”. Sarham yace “ai in baki sani ba, duk wani mumini sau daya maciji yake saran sa a rami guda bisa kuskure ko kaddara, amma sara na biyu, saidai idan shi ya kai kansa da kansa”. 

    Madinah ta ce “duk da haka Sarham, na kuma yarda da kai. Wancan lokacin haka nazo na daukeka na kaika gabansa ba tare da sanin zai ci mutuncin ka da zarafinka ba, to yau ma hakan, at the same time, wannan lokacin ma ban san meyasa yake neman naka ba. But do me this favour, ko da itace alfarma ta karshe da zaka yi min a rayuwarka!”.

    Daga wannan Dr. Sarham bai san meyasa bai kara musawa ba, ya samu kansa da bin bayan Madinah zuwa motar ta tamkar rakumi da akala.

    ****         ****           ****

    

    SULHU

S

un zauna shi da Daddyn Madinah a falon ganawa da bakin sa, Alhaji Attahiru yace “Sarhamu ba wani abune dalilinta ba, wanda ya hanata nemanka all this while, face BIYAYYAR IYAYE, ina fatan hujjarta wadda ta isa hujja a takaice, ta samu karbuwa a wurin ka, tunda kaima kana burin naka ‘ya’yan watarana su yi maka biyayya irin wadda Madinah take yi min. 

    Autata Madinah mai gudun zuciyar iyaye ce da son gamawa dasu lafiya, shiyasa bata daga ido akan duk wani umarninmu zuwa gareta, ba don ta daina son ka bane taki neman ka, a duka shekarun nan tana dakon soyayyar ka ne, ni da bata fadawa hakan ba amma nine shaidar hakan, amma a haka na rufe ido nayi mata aure da wanda hankali na ya kwanta da shi.

    Wani irin dago kai Sarham yayi cikin slow motion, jin furucin Baban Madina na karshe, Alhajin bai damu da reaction dinsa ba ya cigaba da bayani,

     “kafin Allah ya nuna min ayar sa a kan ku, wato kafin in kai ta gidan mijin ya dauke abin sa, a hanyar sa ta zuwa daukan ta zuwa gidan sa, ta sanadin hadarin jirgin sama.

    Idan nace maka I was extremely shocked da mutuwar AVM as at that time, kaima ka san yayi kadan ya bayyana dimuwar tawa.

    Da albarka ta yau nake cewa idan har yanzu kana ra’ayin auren Madinah to kaje ka turomin mahaifan ka su karba maka auren ta, bana bukatar komai sai sadaki”.


Duk da haka, duk da wannan ban hakurin da dattaku da Daddyn Madinah ya nuna a yanzu, da cewa da yayi yayi nadamar abinda yayi masa, ya kuma ce baya bukatar komai na auren Madinah daga gareshi sai sadaki, bai wanke zuciyarsa ba. Madinah ta sha matukar wahala kafin Sarham ya sauko, wato kafin ta samu ta shawo kansa ya sakar mata fuska ma kadai, domin wata ‘yar karamar zautuwa ce ta same shi akan maganar auren ta da marigayi AVM.

     Duk da maganar ta zo masa bagatatan, amma bai yi mamakin jin ta ba, sabida shi kansa ya san Madinah ba matar bari bace ga maza ‘yan uwansa, ya kasa sake mata fuska in ya tuna wai har aure aka daura mata, shi bai yarda bama wai bata je gidan mijin ba, watakila Daddynta ya fada ne don ya rage masa zautuwa, amma dai ko yaya Madinah take Madinah ce a wurin sa, ya sani ba zai iya daina son ta ba, ko da kuwa ‘ya’ya goma ta haifawa AVM din, yaki yarda sam ya koma mata ‘jovial Sarhamun sa’, duk wani annuri ya kau daga kyakkyawar fuskarsa.

     Rabuwar su ta wadannan shekarun da maganar daura mata aure da mahaifin ta ya sanar da shi sun sa ya canza da yawa daga halayen sa data sani na sakin fuska dayawan walwala, ko ace ita Madinah ta canza shi, ta mayar dashi tattaura, mai tsauri, kuma mai wuyar sha’ani. Duk da haka yana nan a ‘jovial’ Sarham din sa, wato mai far’a da faram-faram da mutane amma banda ga ita Madinah, sau tari sai yayi ra’ayi zata ga hasken hakoransa, ko inda wasu mutane daban yake tare. Duk Madinah ta jure wannan punishment din da bata da laifi, ta san wuyarta kawai su yi aure kawai komai zai zama labari. 

     Wani irin kishi ke cin ransa akan maganar auren Madinah da wanin sa, kuma taki su magantu akai sam, da ya kawo zancen zata bata rai, ta ki tankawa. In ya takura da tambayarta wani abu akan aurenta da AVM ko makamancin haka sai kawai ta saka masa kuka. Ko yaki ko yaso dole ya bar zancen.

    Ba kamar can baya ba da kullum zaka tadda fararen hakoran sa (in yana gaban Madinah) a warwaje, ya kasa rufesu, kamar na mai tallan makilin dinnan ‘colgate’. 

    Yanzu kam saidai ka ganshi bay abo ba kuma fallasa, fuskar ta koma kadaran-kadahan a gaban Madinah. Itama dole yasa saida ta rage nata far’an gareshi, ayi mutum kamar mutanen farko ba yafiya ba afuwa ba manta abinda ya shige? Aka koma kadaran-kadahan din ita da shi, amma dai suna tare koyaushe a cikin asibiti ko a cikin campus, ko a gidansu a weekend, haka suka kasance har zuwa ranar da Surayyah ta gaya masa ‘graduation’ din ta daga BUK.

     A ranar ne kuma Daddy, wato Alhajin su Madinah ya tabbatar masa ya bashi auren Madinah halak-malak, yaje ya zo masa da iyayen sa a tsayar da magana kawai.

Ko yaki ko yaso, hakika yaji farin cikin hakan maras misaltuwa akan wannan albishir din na Alhajin kamar yanzu ya fara jinsa, komai pretending dinsa kuwa, musamman da Daddyn da kansa ya kira shi a waya ya gaya masa da bakin sa da nasa, don haka ya ajiye maganar kishin matacce a gefe, yana cewa da sannu zai rama ne. Madinah bazata ci sadakin maza biyu abanza ba dole ta gane shima yanada ajinsa in ta shigo gidan sa, sai ta gaya masa ko sau nawa AVM ya samu alfarmarta, kafin ya yarda su yi rayuwar farin ciki irin wadda ya dade da yi musu tanadi.

     Da wannan shawarar da yayi da zuciyarsa ya ajiye kishi a gefe ya koma na shirin tahowa gida, domin ya kammala kwas din da ya kaishi Jeddah gabadaya, a ranar yayi booking, zai taso a washegari, suka yi sallama da Madinah a asibitin Sarki AbdulAzeez, yau kam taga ‘yar walwalar Sarham, domin da zai tafi har yake ce mata duk ta yi baki ta rame, ina dalili? 

Madinah taji wani irin sanyi a ranta sai ga hawaye sun digo. Shi bai san yadda canza matan da yayi completely da yadda yake treating dinta yanzu ne wai don ta auri wani kafin shi bisa rubutacciyar kaddarar ta ya ramar da itan ba, ya kuma maida ita bakar ba?

    A lokacin sai bata bashi amsa ba, maimakon hakan, sai ta mika masa kyakkyawan kwalin dake sunke a hannun ta, mai dauke da kyawawan furanni da katon HAPPY BIRTHDAY card mai zanen zuciya. Sai a lokacin Sarham ya saki dariya don shi ya manta ma wai yau ne ya cika shekaru talatin da uku a duniya.


    Tunda ya hawo jirgi yake tunani, Allah dai yasa Surayyah na kaiwa su Inna kudin da yake aikowa ta account din ta da yace ta dinga baiwa Sumayyah tana kai musu, ta san gidan, don sun taba zuwa tare, ya san dai Innar Hauwa jarumar uwa ce, cikin kowanne hali zata kula da kanta, kuma zata kula da Hauwa-Kulunta, ba zata bari ta zama (drop out from school) ba. 

    Dan abinda yake tura musu duk wata ya san zai ishe su cin abinci har wata ya zagayo, duk da ya san Inna bazata zauna haka babu sana’a ba, Allah yasa Sumayyahn kuma tana jure kai musu, kodayake Sumayyahn sa ba daga nan ba, wajen aikin zumunci da taya shi son duk abinda yake so, balle wadannan bayin Allah data fahimci sun mamaye rabin zuciyar sa!

Jirgin su ya taso daga Jeddah a washegari bayan sun yi sallama emotionally shi da Madinah a filin jirgi, yanata kissima abubuwa daban daban a ransa, wadanda zai je ya tarar a Kano, akan dai Inna da Hauwa, da rayuwar da suka samu kan su a bayan babu shi. Sarham ya sa a ransa ba zai koma Jeddah dauko matar sa Madinah ba wannnan karon sai ya mallakawa Inna wayar tafi da gidan ka komai kankantar ta, don dai ya dinga jin lafiyar su kai tsaye, ba tare da ya saka ‘third party’ a tsakanin su ba.


    ****               ****               ****

      

 

T

axi din da Dr. Sarham ya dauko shata daga filin jirgi bata sauke shi a ko’ina ba sai a kofar gidan su. Wanda ke cikin rukunin gidajen malamai na sabuwar jami’ar Bayero.

Surayyah ce ta fara hango shi daga tagar dakinta, daidai lokacin ta dage labule don samun iska kasancewar ‘nepa’ sun yi mata halin su na dauke wuta tana tsaka da shaqar barcin rana cikin A.C, wani hucin zafi ya tada ta, don haka ba shiri ta tashi ta dage labulen ta don ta samu ‘natural’ iska ta shigo mata, wannan ne yasa duk gidan ita ta fara ganin sa yana fitowa daga mota. 

    Banda ‘jini’ sunan sa ‘jini’ da Surayyah bazata gane Bhaiyan Sumayyah ba sam, ko ta ce Yaya Doctor yadda take kiran sa ita, sabida girman da ya kara da irin canzawar da yayi a shekaru ukun da ya kwashe a kasar Saudi-Arabia, ilhamarsa da cikar zati sun karu, sun ninku akan wadanda ya bar gida dasu. Yayi haske kadan, fatar jikin sa ta yi ‘fresh’ kamar wanda ya shiga injin wankin fata. 

    Karadin Surayyah shi ya tashi Sumayyah dake falo a gaban TV tana kallon diramar Hausa, ta yo dakin nata a guje don ta dauka wani abu ne ya same ta, da karfi Surayyah tace, “Summy Bhaiyan ki ne, Yaya Doctor ke shigowa”.

    To amma me? Sai ta tuno wani abu, wanda yasa nan da nan ta nutsu, ta daina murnar dawowar Bhaiya, gashi dai ya dawo ‘unexpected’, gashi ta masa babban laifi, tace cikin damuwa.

     “Summy na dauka ba yanzu zai dawo ba, na saka a raina kafin lokacin da zai dawo na hada kudin nan na baki sakon nan na mutanen nan kin kai musu duka a dunkule”.

    Sumayyah ta ce cikin mamaki “wane sako? Wadanne mutanen?” Cikin damuwar data fi ta baya Surayyah ta ce. “Ki min afuwa Summy, ban taba gaya miki Yaya Doctor yana aiko kudi ta account dina in baki ki dinga kaiwa mutanen nan nasa talakawa da ya likewa na kofar Na’isa ba, ni wallahi na ma manta, sai yanzu dana ganshi na tuna”. 

    Ta kara da cewa “Summy don girman Allah ki rufa min asiri in ya tambaye ki kice ina baki duk wata kina kaiwa, in yaso zan dunkule duka abinda ke hannu na a yau in baki ki kai musu kafin ya je gidan, wallahi cosmetics (kayan kwalliya) and other stuffs kawai nake karawa da su duk wata, saboda Mama bata yarda ta saya min irin wadanda nake so.” 

    Idon Sumayyah har rawa yake don bacin rai, da tsoro da mamakin abinda ‘yar uwarta ta aikata, har ta fara hango irin hukuncin da Bhaiya zai mata, ta fara hango shi ya dauke Surayyah da mari kodayae Bhaiya baya duka baya zagi, amma fa bai iya fushi bay a kuma kware da (silent punishment), fatar bakinta ma rawa take yi, ta kasa murnar dawowar tasa ma don haushi da mamakin Yayar ta Surayyah, da kyar Sumayyah tace,

     “kin ci amana amma, Yaya Surayyah kin ci amanar Bhaiya, na rantse da Allah babu ruwa na, count me out of your dirty game”. 

    Daga haka Sumayyah ta fice da gudu tana “Oyoyo! Bhaiya, Mama Bhaiya ya shammace mu”. Sai ga Mama ta fito daga dakin ta itama kan ta ko kallabi babu, tace “really?” Surayyah kuwa bayan gida ta shige ta boye kanta, jikin ta ba inda baya rawa.

    Sumayyah ta kusa kai Sarham kasa sakamakon tsallen da tayi ta shako shi da sunan murna. Haba! Sarham sai ya balle da fada blah! Blah! “Sumayyah meye haka? Baki san kin girma bane? Ko an ce miki da da yanzu ma daya ne? Bana son irin wannan haukan welcome din, an wuce wajen, kada ki kara”.

    Mama ta iso falon tana cewa “kai mai hali dai baya fasa halin sa, kai kuma daga zuwa sai fada kamar tsiduhu? Shekara uku ba kwana uku ba basu saka ka a idon su ba, ba dole su yi murnar ganin ka bagatatan yau ba?”.

     Sarham ya mike ya isa gareta ya kama hannayen Mama ya rike cikin tafukan sa, yana murmushin farin ciki ya kai su ga fuskar sa kan sajen sa, wanda a baya kafin ya tafi bashi da shi yace “My Mommah, I missed you badly kin sani. Amma autar ki bata san ta girma ba, kullum tana nan jiya I yau shiyasa bazan daina fada ba”. 

    Kafin kace meye wannan gida ya kacame da murnar dawowar Dr. Sarham. Da Abba Prof. ya dawo murnar tafi armashi, a ranar har dare suka raba a falo suna hirar yaushe gamo, amma an nemi Surayyah an rasa a falon, tunda ta zo ta yi masa sannu da zuwa ta gudu gidan Kakar su Haj. Kulu a gadon kaya, don tayi-tayi Sumayyah ta karbi ‘yan kudin da ke hannun ta ta kai Kofar Na’isa, ta roke ta kan ta rufa mata asiri tayi maza ta kai musu tun kafin Yaya Doctor ya huta ya waiwayi zancen, wadanda ko kwatan abinda ta kashe daga abinda yake aikowa din basu kai ba.

     Sumayyah ta ki amsa, ta kuma ce in ta takura mata ta cigaba da saka sunanta cikin laifi nan wallahi zata tona ta, “kawai ki yi harkar ki Yaya Surayyah ki rabu da ni, ni ba maciyiya amana bace kuma ba’a shirya rashin gaskiya da ni”.

    Duk da ta san Sumayyah ta gaya mata bakar magana sosai amma ta kasa cewa komai wannan karon, girma da mutunci ai madara ne, kuma mutum shi yake rike kayan sa, ta yarda ita ta zubar da girman ta har Sumayyah kanwar bayan ta yau ta nemi zagin ta (in disguise). Don haka Surayyah ta ga gara ta gudu gidan Hajiya, inda ba abinda Sarham ya isa yayi mata in dai a gaban Hajiya ne koda ta bare da ita.

    Washegari walima sosai Mama ta hada musu a babban falon ta, ta murnar dawowar Sarham da kammala zurfafa karatunsa, wato kwas din da ya je yi na tsayin shekaru uku a (KAU, Jeddah) ta kasar Saudi Arabia, don haka aka tura direban zuwa Abba Gadon kaya don ya dauko Hajiyar Gadonkaya.

     Jin maganar zuwan direba daukan su daga bakin Maigadi yasa Surayyah duk ta damu, lokacin da da aka ce su fito a tafi gidan Abba, Hajiya tace ta shirya su tafi gidan nasu tare, ta yaya ana can ana murnar zuwan dan uwanta da taya shi murnar zama babban likita zata taho ta zauna ita kadai anan kamar mujiya a cikin ‘yan uwanta? 

    Tace lallai ta shirya su wuce, bazata bar ta ita kadai a gidanta ba.

    Da Surayyah ta ga ba sarki sai Allah sai ta fadawa Haj. Gaskiya cikin damuwa, cewa laifi tayi masa fa, bata so ya kure ta, don zai iya dukan ta, Hajiya kuwa ta saka ta a gaba tace sai sun tafi taren, mai dukan mata ita sai ruwan sama.

    Mama da hannun ta tayi girke-girken walimar nan, don haka sun kwashi gara mai dadi sosai. Sarham yayi wa girkin Maman sa cin yaushe rabo! Da sweet cook din Mama!? Ba abinda bai ci ya hantse a wajen ba. Da yake magananne ne har gobe tunda ya fara cin abincin nan bai yi shiru ba, yana yi ne yana zuba santi, saida Hajiya Kulu ta saka masa filon kujera a kuturin sa, tace, “gara a saka maka waigi haka likita Sarhamu, Allah yasa dai matar duk da zaka aura mai iya girki ce.

     Shin ma ina aka kwana kan maganar aure? Wannan karon kam zan bada cigiyar mata har a masallatai idan bakin jini ne ya hana ka samun mata”. Daga Abba har Mama duk suka bi shi da ido kamar Hajiya ta ci musu albasa ne ta fadi abinda ke ci musu rai, suka dakata da cin abincin suma suna jiran amsar sa da zai fada, da alama dukkannin su suna da wannnan damuwar tuntuni kawai Hajiya ta riga su furtawa ne.

     Ai yau Sarham da karfin guiwar sa ya ce “ki kwantar da hankalin ki Hajiya, ba sai kin kai tallata a masallaci ba, an riga an bani mata cikin daraja da kima kuma wadda nake so tuntuni, ku ake jira ku je tambaya da sanya lokaci”. 

    Mama da Abba har suna hada baki wajen tambayar sa.

     “Daga ina ka samo matar kuma ‘yar waye a Kano a ina suke? Tun yaushe kuke tare bamu da labari?” 

    Yace “Mama zaki iya tuna yarinyar dana ke tare da ita tun zuwana karatu MBBS na farko? Ina nufin MADINAH. Ke ai kin jima da sanin labarin ta, wadda a baya mahaifin ta yace bazai bani ba, to ita din ce dai muka sake haduwa a wannan karon muka sulhunta, mahaifin ta kuma ya bani auren ta already ku kadai yake jira, ‘yar gidan Attahiru Habibu SoronDinki ce”. 

    Mama da yake ta san zancen Madinah tuntuni nan da nan ta ci magani, fuska a gintse tace “shima ai ya sani” (tana nufin Abba Prof.) ta kara da cewa “ko ba yarinyar da ka kusa kashe kanka a kanta ba, saboda uban ta ya wulakanta ka? Yarinyar da ka zauna shekara bakwai cikin tuzuranci babu aure saboda an hana ka ita, sakamakon cewa sun raina arzikin mu da mutuncinmu? Itace ko ba ita bace?” 

    Sarham yayi shiru, gaban sa da zuciyar sa na wani irin faduwa, tsoron sa Allah tsoron sa kada Mama tayi (opposing) maganar Madinah, shi kam da ya shiga uku, don in har ba Madinah ya aura ba, babu shi babu aure a duniya (ya fada a zuciyarsa).

    Abba ya ce “Lelen Abba rabu da Mama, yi min cikakken banyani, diyar Attahiru Sorondinki wanda na sani ce da gaske? Ina nufin na ISDB? In haka ne kenan jikar Alkalin Alkalai Habibu SoronDinki kake nema kenan fa?”

    Sarham ya dan samu kwarin guiwa da hope, domin a muryar Abba kawai ya ji ‘excitement’ na sanin iyayen Madinah da yayi, kamar zai yi na’am da maganar shi kam. Yace,

     “sune Abba, his last daughter Dr, Madinah Attahiru”. Da rashin karsashi a muryar sa ya baiwa Abba tarihin su Madinah da iyayaenta kamar yadda ya ji daga bakinta, da kuma na rayuwar su a Jeddah itada mahaifanta da ‘yan uwanta maza, inda a can aka haife su itada wasu daga cikin yayyen nata, da yadda mahaifin ta ya raba su a baya, yanzu kuma su da kan su suka neme shi ba shi ya nemi Madinah ba ta dawo masa ba, har pretending din da yayi tayi mata don kada ya koma mata ya gaya musu, da kiran sa gidan su da Daddyn nata yayi, domin ya bashi hakuri da uzurin sa na hana shi auren Madinah.

     Amma abin mamaki duk da wannan labarin da Sarham ya bayar Mama taki saukowa ta amshi zancen Madinah da hannu bibbiyu, musamman da taji wai har aure an daurawa Madinah bata tare ba mijin ya rasu, sai ta kara ninka ‘opposition’ din ta da zancen, inda tace cikin mamaki,

     “Sarham! Kai kuma inda Allah yayi da kai kenan saboda soyayyah? Bazawara/widow zaka dauka kana saurayi wanda bai taba aure ba? Bazawara fa kaikuma saurayi? Ni ban yarda wai bata je gidan mijin ba, sun dai rufa ka ne don su sayo mata matsayin budurwa, shiyasa ko lefe aka ce ka bari, kai kuwa saboda Allah me Madinar nan ke da shi da sauran mata da kake gudu suna rububin ka basu dashi?”

     Abba yace “Maimuna har gobe baki san SO ba na ga alama, kyale rai da abunda ya afu ga so, aure kuma ai ba kaskanci bane daraja ne, haka mutuwar miji baya nufin darajarta ta ragu, ni ban ga laifi anan ba don yarinya ta taba aure, shin Manzon mu ba da bazawarar ya fara ba?

    Yarinyar nan ‘yar manyan mutane ce kuma ‘yar babban mutum, sama da abunda yafi haka zasu iya cewa kafin su bada auren ‘yar su, aka ce tuwon girma… miyar sa nama Maimuna, ko yanzun ba don ta rasa miji bane yasa suka bashi, a’ah, ya ci darajar soyayyah ne kawai Allah kuma ya tsaga cewa ita din rabon sa ce”. 

    Mama tayi shiru amma ta ki gamsuwa, ta ce “ni kawai ko ‘yar shugaban kasa ce bai dame ni ba, tunda suka raina arzikin mu tun farko nima na raina mutuncin su, saboda basu yi amfani da ilmin su ba anan don wallahi ba yabon kai ba, Sarham dina ya wuce raini, tunda Allah ya bashi addini, nasaba, ilmi da basira to ya gama bashi duk wani arziki na duniya koda kuwa a kan jaki yake yawo”. 

    Duk aka yi wa Mama dariya Abba yace “Maimunatu Dan farin? Kike wannan zakewar a kan sa babu fulatanci? Ina fulatancinki ya tafi ne?” Ta yi fuska sosai ta ci laya tace “ko rabin farko ne shi ba Dan fari ba, ina son abuna yadda suke so ‘yar su koma fiye, sun dauko sudin kwano sun bashi, ina dalili da gatan sa shima da komai?” Abba yana danne dariyarsa yace.

     “Barr. Maimunatu to yaya zaki yi? Tunda shi ya ji ya gani yana son leftover din nasa a haka?” 

    Sarham dai bai ce komai ba kansa na kasa, kamar yace da kasar ta tsage ya shige, amma ya ji ciwon kalmar nan ta an bar masa sudin kwano, ta kara rura wutar kishin sa akan auren Madina da AVM Alkali. Duk ya daina dokin auren ma, Madinar ta kara bashi haushi, amma baya jin ruwa da iska zai fasa karbar auren Madinah ko da ta haihu goma da AVM wanda ke nufin so na hakika yake yiwa Madinah.

    Abba da Hajiya Kulu, suka yanke shawarar wadanda za’a tura Sorondinki daga waliyyan Sarham don gabatar da zancen aure don itama Haj. Kulu tayi na’am da zancen dari bisa dari don kuwa ta san Kakan Madinah farin sani marigayi Alkalin Alkalai wanda tace zuri’arsa ne kaf suka samar da Sorondinki.

    A daren Abba Prof. kwana yayi yana lallashin Mama cikin dabara da soyayya irin ta manya akan maganar auren Sarham, yace mata abu daya zata duba kawai; son da Sarham yake wa Madinah, in ta duba wannan to sai ta sakawa ranta salama.

    Domin shi ya lura son da Sarham yakewa Madinah mai yawa ne, tunda har ya iya kwashe shekarun nan babu aure saboda rashin ta, kuma jin ta auri wani kafun shi, bai say a ce ya fasa ba.

    Ita kuma Mama irin iyayen nan ne masu kishin ‘yayan su, wannan son da ake fadi yana wa Madina shi yafi komai bata mata rai, don a tsarin ta sam bata son Sarham ya auri macen da son da yake mata ya zarta wanda take masa, ko wadda zata zo ta canza masa behaviours da alaqarsa dasu. A ganin ta son da yakewa Madinah yayi yawa har ya zarta nata son, ba don haka ba ai da bata yarda ta auri wani kafin shi ba, tana tsoron kada Madinah tayi amfani da hakan ta bautar mata da shi, ko ta wahalar mata da shi tunda ta zame masa rayuwa dungurungum. Duk da ta san Sarham jarumi ne akan komai nasa ko a cikin maza, kuma tsayayyen namiji ne tun yana yaro akan ra’ayinsa, amma tana tsoron wannnan matsiyacin son da yake yi wa Madinah Attahiru. 

Haka Abba Prof. ya samu ya lallaba ‘yan kayan sa, don shikadai yasan abinda yake zuciyar Mama, ya nuna mata in bata cire kishin matar Sarham daga ranta ba zata zubar da girmanta, kuma zata sha wahala don matsayin kowaccen su daban a wajensa, ya roketa kada ta zama fitinannun iyayen mijin zamani masu tsanar surukansu babu gaira babu dalili kawai don yaransu na son su, tunda itama ba haka Hajiyar Gadonkaya tayi treating dinta ba duk da ta san son da Abban  yayi matukar yi mata, da haka ya samu ya lallabata har dai ya samu lagonta ta amince aje akai kudin auren, ta kuma sakawa al’amarin albarka.

Washegari waliyyan Sarham suka tafi SoronDinki. Suka dawo da albishir mai dadi na cewa Baffanta yace Juma’ar nan za’a je a daura auren a babban masallacin juma’ah na Kano, su sun shirya tuntuni, su suke jira dama. Suka kuma fadi irin karbar mutunci da saukar girma da aka yi musu, wannan ya kara sauko da zuciyar Mama. 

Iyayen Sarham sun gabatar da komai na auren har sadaki ga kanin Baban Madinah tun kafin juma’ar ta zo, kuma Baban Madina yana ta kara jaddadawa kanin shi ta waya ya gaya musu shi baya karbar lefe, sadaki da kudin aure kawai yake amsa. Wannan ma ya kara sanyayawa Mama. Juma’ah na zagayowa aka daura auren.

****                ****                  ****

    Tun dawowar sa Najeriya Sarham bai samu nutsuwa ba ko ta kwabo, sai yau da aka daura auren sa da Dr. Madinah Attahiru bayan saukowa daga juma’ah, mahaifin ta da duka ‘yan uwanta maza hudu sun samu sun halarci dauren auren, Madinah ‘yar dangi ce gaba da baya kasancewar auren zumunci ne a tsakanin iyayen ta, sun kuwa nunawa Hajjah Ramlah zumuncin da karah, don kwansu da kwarkwatarsu zuri’ar Sorondinki sun yi dafifi a ‘main house’ din su, don halartar yinin bikin Madina a ranar da aka daura aure.

     Iyayen Madinah su ya kamata a kira masu Kano, ba kuma wai sarauta ce dasu ba domin iyayen ta da dangin ta na uwa dana uba wadanda duk abu guda suke, sun kame duk wasu madafun iko na Kano.

Sai bayan daurin aure ne, da ya samu ya huta ya samu nutsuwa bayan mutane sun watse, a daren daurin auren ya samu ya zauna da Sumayyah yana tambayar ta yaya labarin su Hauwa da Inna? 

    In ce ko tana zuwa tana gano masa su da baya nan kamar yadda ya bar mata sallahu? Kuma in ce ko duk wata tana kai musu sakon da yake aikowa ta hannun Surayyah?”

     Ya tsare ta da kaifafan idanun shi ganin yanda tun bai gama magana ba Sumayya ta shiga cikin rudani da damuwa, na farko dai itama ta mance da su Hauwa, bata kara tunanin zuwa kofar Na’isa ba tun bayan tafiyar sa, na biyu ga abunda Surayyah tayi, wanda ke nufin dukkan su sun zama masu laifi ga Bhaiya, sai dai a ce laifin Surry ya take nata wato, sawun giwa ne ya take na rakumi. 

    To amma ta kwana da sanin halin Bhaiya baya son yayi maka tambaya wadda a wurinsa mai muhimmanci ce ka zuba masa na mujiya nan da nan zai harzuka, sai duk ta daburce, ta hau inda-inda da in-ina, tana son cewa ba ita bace Surayyah ce, tana kuma son kare Surayyar. 

    Kawai sai jikin sa ya bashi babu gaskiya acikin al’amarin ta, ko wani abu mummuna ya faru dasu Inna a bayan tafiyar sa, gabansa yayi mummunan faduwa ya fiddo wayar sa ta tafi da gidan ka daga aljihun gaban farar shaddar shi Wagambari wadda ta sha maikon sabunta, Ango sosai, sai walainiya yake yi a cikin farar Excelcior din, yasa dan yatsan sa daya yana dannawa Surayyah kira, tana amsawa yace ta same shi a karamin falon Mama.

    Tun daga jin kiran sa itama Surayyah ta hau numfarfashi ta san ta gama barewa, a lokacin suna tare da wanda zata aura a harabar gidan su wato Engnr. Aliyu Barde, wanda dan abokin Baban su ne, iyayen su suka hada su, Aliyu ya fahimci hankalin ta ya rabu gida biyu tun bayan amsa wayar ta, yace “me ya faru ne a wayar?” Surayyah ta dauki excuse daga wajen Aliyu kan Yaya Doctor dinsu yana kiran ta a cikin gida, ko zai bata minti goma?

     Egnr. Yace ai tafiya ma zai yi don akwai inda zashi, don haka suyi sallama kawai, sai wajen jibi zai dawo. Don lokacin an saka musu lokacin aure.

     Bayan sun yi sallama ya tafi, Surayyah ta taka zuwa cikin gida tana tafe salalau-salalau kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki.

Sarham har ya gaji da jiran shigowar ta ya mike zai biyo bayan ta yana huci sai gata tana shigowa. Tun kafin ta zauna ya jefo mata tata tambayar kamar yadda yayiwa Sumayyah game da sakon su Inna da yake turowa ta account din ta duk wata, yau shekara uku bai taba fashin turowa ba, wanda yace a dinga kaiwa mutanensa na kofar Na’isa.

     Surayyah tayi zuru-zuru ta yi wiki-wiki da ido tayi masa shiru, kiris ya rage ya mare ta, don baya son halin ko’in kula in yana maka maganar da a wurin sa mai muhimmanci ce, kayi shiru ka zuba masa ido kamar tsohon maye kana kallon sa. 

    Da kyar Surayyah ta motsa baki ta ce cikin rawar murya “I’m sorry Yaya Doctor!” Ta kara cewa “I’m so sorry” “Sorry for what?!” Ya tambaya (in exclamation).

     Sumayyah kanwarta wadda ta soma hawayen ganin yadda ransa ke hauhawa wajen baci tun ma kafin yaji laifin da Surayyah tayi masa, taga basu da mafita banda ta gaya masa gaskiya, sai tace.

     “Bhaiya, maganar gaskiya ko sau daya bata taba bani komai tace in kai musu ba, sai ranar da ka zo take gayamin ai kayan kwalliya take saye da kudin, ni ma kuma ban taba zuwa duba su ba, wallahi na manta hanyar gidan sam, lokunan (are complicated), don haka dukkan mu mun yi laifi Bhaiya, muna rokon ka in ka tashi hukuntamu, to kayi mana sassauci a hukuncin ba don halin mu ba, ka yi mana uzuri da ajizanci irin na kowanne dan adam”. 

    Sarham ya kasa magana don takaici sai raba ido yake a kan su su biyu, amma kalaman ta na karshe sun yi tasiri sosai a cikin ran sa dake tafasa, ya ciza fatar bakin sa kadan, yana kallon su da lumsassun idanu duk sun zama unease, kada Surayyah ta ji labari, wadda ta kasa zama tana daga tsaye har lokacin amma kafafun ta rawa suke. Da kyar Sarham ya hadiyi miyau, yace cikin sanyin murya.

    “My only two and beloved Sisters ne suka ci amana ta haka?!” 

    Sumayyah ta cigaba da hawaye tace “wallahi Bhaiya babu ruwa na, bata ma taba gaya min ba ni sai ranar da ka dawo. 

    Ni nawa laifin na rashin zuwan maka ne kawai, da kuma rashin taya ka kula da abinda kake so a bayan idanun ka, wanda ko kadan baka cancanci hakan daga gare ni ba. Kamata yayi ace ko kare ka ajiye don kana son shi ya kamata in kula maka dashi in your absence balle mutane ‘yan adam.

     Na yi kuskure Bhaiya, amma na tuba, ka karbi hanzari da uzuri na, ajizanci ne na dan adam da mantuwa, na tuba Bhaiya bazan sake ba”. 

    Sumayah ta durkusa a gabansa ta daga hannu cikin roko, hawaye na bilbila, Surayyah ta kasa kare kanta amma hakika yau ta ji kunya, ta kuma yi nadama a lokacin da bata da amfani, wato lokacin da ko ta bada sakon ba zai yi masa amfanin komai ba tuda ya riga da ya dawo, gashi ta san ta sirewa dan uwan nata yanzu, saboda rashin amana, koda bai fada ba bai kuma bai doketa ba. 

    Mama ta shigo da sauri jin kukan Sumayyah, tana tambayar su “me ke faruwa ne haka a falon nan ake kuka har da kururuwa?” 

    Sarham ya ce cikin kololuwar feeling of disappointment “Mama kin gan su, su duka sun ci amana ta!” Mama ta ce “kada Allah ya nuna mini ranar da zan haifi Da maci amanar dan uwan sa, sun dai yi kuskure wanda ba wanda yake sama da aikata shi, ka yi hakuri Sarham ka yafe musu kaji! Duk da ban san girman laifin ba”.

Sarham ya dubi Surayyah (feeling disappointed) ya ce “Surayyah idan abinda kika yi kyautatawa ne ga zumunci na da ke, na gode. Allah ya saka da alkhairi.

     Ke kuma Sumayyah baki yi min laifin komai ba, amma daga yau na san matsayina a wajen ki, na kuma ga ajin da kika ajiye ni, tunda bazaki zame min ‘yar uwar da a bayan raina zata kula da haula ta ko abinda na bari ba”.

     Sai ya sa kai ya fita, makwallaton sa har motsi yake don tsananin bacin rai, ba tare da ya tsaya yi wa Mama bayanin laifin da suka yi masa ba. 

    Mama duk suka saka ta a duhu, ta rasa gane komai, sai da Sumayya ta share hawayenta ta gaya mata komai cikin muryar kuka.

Mama ta kasa tuno mutanen da ake matsalar a kan su, ta san dai ire-iren jama’ar sa ne da baya rabo da kyautatawa, da irin jajibe-jajibensa, amma hakika ta harzuka da abinda Surayyah ta yiwa Yayanta, bata san ko su waye wadanda yake turowa kudin ba duk wata tun daga Jeddah ba, ba kuma tareda ta damu da ta sani ba, amma tunda har ya dauki tsahon shekaru uku yana turo musu kudi duk wata bait aba mantawa ba to masu muhimmanci ne a wajensa, kasancewar ta san halin sa akan son tamakawa mutane da son kyautatawa na kasa da shi da marassa lafiyansa, sai hakan bai zame mata wani sabon abu cikin halayen dan nata Sarham ba, Mama tace.

     “Da gaske wannan cin amana ne, kuma zai fi bakanta masa rai ne kasancewar mutane mafiya kusanci da shi ne suka yi masa”, ta dube su cikin fushi ta sake cewa “a duniyar nan in dan uwanka ciki daya bai rike maka amana ya rufa maka asiri ba, in bazaku kashe ku rufe kai da shi ba, ba tareda ko iyayen ku sun ji ba, waye zai yi maka? 

    Sannnan da wa zaka yarda a duniya, kuma da wa zaka aminta? 

    Kin yi kuskure Surayyah, ba dan uwa irin naku ake badawa kasa a idanu ba, saboda shi din dan uwa ne har dan uwa guda har da rabi, ko in ce Yayan da babu irin sa, ko don son da yake muku da kulawar sa da kyautayinsa gare ku”.

     Surayyah ta gama dukkan nadamar da mutum zai iya, a lokacin da yasan bai kyauta ba aka kuma ankarar dashi. Cikin kuka ta ce.

     “Mama don Allah ki bashi hakuri, na tuba na bi Allah na bi shi, zan biya shi duka kudin sa da zarar na fara aiki, dama ban kashe da niyyar bazan biya ba, kawai ya zo ba ‘notice’ dina ne, nayi niyyar in bata ta kai musu kafin lokacin zuwan sa, wallahi zan biya shi”, Mama ta wani harareta ta ce “ta baya ta raggo.

     Duk abinda zaki biya shi yanzu bazai karba ba, kuma bazai masa amfanin komai ba. Surayyah an yi bokon banza tunda shi ya koya miki son abin duniya, kayan kwalliyarbanza kayan kwalliyar hofi, saboda Allah da me iyayen ki suka rage ki banda son kyale-kyalen ki na banza da wofi da kika dorawa kan ki tun shigar ki jami’a, da son lallai sai kin hada kafada kin goga da kawaye da suka dauki karyar rayuwa suka dorawa kan su? 

    Kullum ina nuna miki ‘reality’ akan barin sayen abubuwan nan masu tsada da suka fi karfin aljihun ki ko na iyayen ki, kina ganin kamar ni kaina ban waye ba, tunda bana sayen turare su ‘designer’ sai Humrah sai Oud, har ni zaki nunawa sanin ya kamata akan rayuwar duniya Surayyah? Yaushe aka haifeki har kikayi wayewar??”

     Mama tayi ta fada ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, daman tana cike da halin Surayyah din kan irin tsarin rayuwar ta mai tsada, fadan da Sarham bai tsaya ya yi musu ba don bacin rai shi Mama tayi ta yi musu ta wanke Surayyah tas. Wankin babban bargo. Surayya dai sai hakuri take baiwa Mama ganin har tafi Sarham daukar zafi da al’amarin. 

    Aka ce dan uwa rabin jiki, ganin yadda duk ta muzanta sai ta koma baiwa kanwar ta Sumayyah tausayi, Summy ta ji kamar a maida laifin ya koma kanta, ita a cigaba da yi mata fadan ita kadai, ta koma taya ta suka yi ta baiwa Mama hakuri da rokonta kan ta bashi hakuri in ya dawo, sunyi alkawarin bazasu sake yin kuskure makamancin wannan ba, Sumayyah dai ta ari laifin suka yafa shi tare da ‘yar uwar ta.

    ****                 ****                     ****

    

    SARHAM

D

a ya fita cikin zafin rai, wata motar Abbansa (Peogeot 504) ya dauka wadda tun saukarsa da ita yake amfani, kasancewar bai kai ga sayen motar kansa ba tun dawowar sa, ya fizgeta a guje ba tareda ya san wajen zuwa ba, yana dai so yayi nesa da gida don shi kansa ya san bai iya fushi ba, baya son ‘yan kannen sa su ga launin fushin sa mara kyau, ana he’s jovial amma in yayi fushi kamar zawayi yake komawa don rashin hakuri, musamman akan Surayyah da baya son wasu halayenta. 

    Sai ya samu sitiyarin nasa na sarrafa shi, ya dauke shi yayi hanyar titin da zai sada shi da kofar Na’isa. Yana tafe yana gayawa kan sa ya yafewa Surayyah duniya da lahira, ya yafe mata, amma hakika ta ragewa kanta matsayi a idon sa. kuma ‘outing’ din da yayi niyyar fita dasu zuwa Dam, don tayata murnar kammala degree ya gayawa kansa ya fasa.

    Duk da Mama ta ce zata bashi hakuri inya dawo, amma hankalin su su duka bai kwanta da fitar sa cikin fushi ba da kuma ganin tsayin lokacin da ya dauka bai dawo gidan ba.

Ya isa kofar Na’isa da yamma lis, ya karya kan motar sa zuwa titin da zai kai shi lokon su Hauwa, yana tafe yana tunane-tunane akan su, ko a wane hali zai same su? Ko Hauwa ta gama makaranatar sakandire yanzu? Ko yaya suke rayuwar haka babu tallafin kowanne namiji? Ko Baban su Malam Bilyaminu ya dawo? Ko yaya idanun Hauwa? Allah Masani! Bai san meyasa zuciyar sa ta damu da al’amarin su ba, take kuma daraja su, yana saka damuwar su a ran sa in ya tuna a hannun sa Hauwa ta karbi shaidar makanta da lasisinta, daga zuwa neman magani. Shi ya san da ace ba shi yayi mata aikin nan ba, da bazai damu ba don an samu mishkila. 

    Har gobe kuma ya kuma kasa yafewa kan sa a kan makancewar Hauwa, ya ki cire abun a ran sa, duk da ya san kaddararta ce, shima kuma ba yin kansa bane amma har gobe Sarham yana ganin negligence dinsa ne wato (sakacinsa da rashin iya aikin sa), su suka janyo har Hauwa ta kai ga rasa idonta completely.

Haka tunda ya tafi Jiddah yau shekara uku bai taba kasa tuno su ba kullum, har Allah-Allah yake a yi albashi don kawai ya tura musu, ranar Allah dai-dai ce da baya tuna su, tare da yi musu addu’a da fatan alkhairi. Ya san kuma kudin da yake aiko musu daga albashin sa zai ishe su kananan bukatocinsu na yau da kullum da makarantar Hauwa.

Bayan motar Abban sa da ya tuko, shake yake dankam da tsarabar su Inna rankatakaf! Wadanda tun daren jiya ya saka su a mota yana jiran ya samu nutsuwa ya je kofar Na’isa, yayi ido hudu da Innar sa Safiyya, don ba Hauwa yake kewa ba Inna yake kewa. Eh mana, Hauwa da bata son sa kuma take kullace da shi. Hauwa danger Hauwa hukuma.

Har sabuwar waya nokia karama ya sayowa Inna, da alkawarin yanzu in ya koma Jiddah kai tsaye zai ke kiran su. Idan har Hauwa ta kammala sakandire da kyakkyawan sakamako ya fara tunanin bincike akan yiwuwar cigaba da karatun ta a jami’a, idan hakan mai yuwuwa ne.

     Zai nemi dai wanda zaiyi ‘coaching’ din sa akan ilmin ‘visual impaired’, ba zai koma Jeddah ba sai ya tabbatar rayuwar su bata da matsala ta zama ‘stable’ kuma Hauwa na kan turba ta tafiya zuzzurfan ilmi.

     Wanda shine kadai zai zame mata gata a dukkan rayuwar ta, a matsayin ta na mai nakasar da ake kira mutuwar tsaye.

To amma me? Sai zuwa yake yana dawowa a inda ya san lokon gidan su Inna yake situating, amma baya ganin gidajen da ya sani a wurin sai fili fetal. Da aka zagaye da langa-langa. Ya ilahi! Ko dai yayi batan kai ne? Ko makuwa yayi? ko kuma ya manta hanya ne?

To amma da mamaki ai ace ya mance hanyar gidan su Hauwa, ko shekaru goma yayi baya nan ba uku ba, in dai ba juyewar kwakwalwa ya samu ba ko shafewar tunani wato ‘amnesia’. Kuma dai ga Kofar Na’isan nan dai tana nan bata je koina ba. 

    Da ya gaji da zuwa da dawowa wato ya gaji da safah da Marwah a cikin mota sai ya fito yayi ta zagaye wajen da kafafun sa, amma ya kasa ganin gidan Malam Bilyaminu, ya kuma tabbatar anan gidan yake, sai ma yaga ‘pure water’ na leda ake bugawa a filin wajen. Kamar an maida wajen kamfanin ruwa leda. 

     Ya tambayi wani saurayi cikin masu buga ruwan ledan don Allah ko inane gidan Malam Bilyaminu dan Kofar Na’isa? Ya ce da saurayin “kamar na maku, don na jima bana nan”. Saurayin yace shima bako ne a unguwar, amma bari ya hada shi da Malam Isa mai faskare shi da ya dade a unguwar.

Gidan malam Isa ne kawai ba’a rushe ba cikin gidajen wurin don gidan yayi gefe sosai, saurayin ya raka Sarham suka samu Malam Isa a zauren gidan sa yana aikin itacen sayarwar sa, ya yiwa Malam Isa bayanin wanda Sarham ake nema ko ya san shi? Wai gidan Malam Bilyaminu.

Malam Isa ya bar abinda yake yi ya juyo ga Sarham sukayi musabiha, sai ya bashi wajen zama kan buzun sallahr sa yace ya zauna, da ya tambaye shi ko wa yake nema a gidan Malam Bilyaminu? Sarham yace.

     “Innar Hauwa”.

Sai Malam Isa ya tambayi Sarham “kana da alaqa da Innar Hauwa ne?” Sarham yayi dan jim! Kafin yace “eh, amma na dade bana kasar, ina fatan ba wani abu ne ya faru da su ba?” 

    Malam Isa ya nisa yace, “eh toh, samari, ai Innar Hauwa ta gamu da sharrin wani azzalumin kanin miji, ya sayar da gidansu, rana daya muka ga an zo ana rushe gidan, aka maida wurin wajen hayar neman kudi kala-kala, na so ta zauna mu je kotu a kwato musu hakkin su ni da sauran makwabtan su, kasancewar a gaban mu Zakari ya sayarwa da dan uwan sa gidannan aka raba rigima tun a lokacin a gaban marigayi mai unguwa, amma matar nan ta ki tsayawa, ta gudu daga gidannan bamu sani ba, yau kusan shekara uku zancen nan da nake maka, bamu kara jin duriyar su ba ita da ‘yar ta Hauwa-Kulu”.

Sarham ya ji idon sa har rawa yake banda fatar idon dake raurawa itama, da kyar ya iya yace wanene kanin mijin nata? Ya ce.

     “Zakari sunan sa, don kawai dan sa ya zo yace zai auri Hauwa-Kulu, shine ya sayar da gidan don ya kore su ko ince yasa aka rushe shi, to ya ci galaba kam don daga ranar da aka zo aka rushe gidan su basu kara waiwayar kofar Na’isa ba, kuma ba wanda ya kara jin duriyar su, ina tabbatar maka bazasu zauna a Kano ba yadda suka fita a tagayyare, wutsiya zage, kuma cikin mummunan bacin rai.

     Jifa aka dingayi da komai nasu. Tausayi yasa na tattara tumakin ta da akuyoyin ta na kado su gida na, na hada na nawa na cigaba da kiwata mata, muje in nuna maka su cikin shekaru uku gasunan suna ta hayayyafa ban san ya zan yi da su ba”. 

    Sarham ya rasa a halin da yake ciki tsakanin tashin hankali da gigicewa, yace da Malam Isa “basu da wasu ‘yan uwa da zasu iya zuwa wajen su?” Malam Isa yace “eh, toh, ai dukkan su ‘yan cikin Badalar nan ne a sanin da muka yi musu, in ma suna da su, to mu bamu san su ba, basu da wasu ‘yan uwa da bamu sani ba, dangi kam sun kare ai, kuma bana jin a zuciya irin ta Innar Hauwa zata yarda ta rabi wani nata in ma tana da shi.

     Tun tali-tali tanada wani irin hali, tafi gane rayuwa ta tsayuwa akan kafafun ta fiyeda ta rabu da wani ya taimaka mata, har kuwa bayan batan mijinta, bata taba neman taimakon kowa ba”. 

    Sarham yace “shin a ina wannan Zakari din yake?” 

    Zai so kwarai yayi ido hudu da wannan Zakarin, don kwatarwa su Inna hakkin su, zai so kwarai yayi shari’ah da shi, daganan har kotun daga ke sai Allah ya isa! Domin ya kwatowa Inna hakkin ta, a daure shi har sai igiya ta yi rara, amma Malam Isa ya gyara murya ya kuma gyara zama, yace masa “ka manta da Zakari kawai, ka nemo su Hauwa din shine mafi a’ala, ganin Zakari bazai kare ka da komai ba sai karin bacin rai, don zai iya yi maka mummunan bita da kulli, idan ya gano su Safiya suna da wani gatan bayan shi a duniya.

    Ai sanin cewa basu da kowa da zai tsaya musu ne yasa yayi musu haka!”.

    Sarham yayi shiru, can yace Baba ina so in sake saye filin wajen ne, ina nufin filin gidan nasu daga hannun wadanda suka saya”. Malam Isa yace, ai hakkin mallakar filin ya bar hannun Zakari tuntuni, wannan mai kamfanin ruwan shi ke da wajen yanzu, kana iya tuntubarsa ko zai sayar maka, amma lallai sai ka nunnunka masa kudi”. 

  Tare suka je har gidan mai kamfanin ruwan ledan da ya kafa rumfa a filin gidansu Hauwa yana sana’ar ruwa, suka gaisa, Sarham yana hadiye hawayen sa yace, so yake ya sayar masa da filin wajen, inyaso ya yanka masa kudin ko nawa ne zai biya shi, ya bashi takardun mallakar kangonnan. 

    Hakan kuwa aka yi, da mutumin ya ga kudi ya amince, ya yanka kudin da yaga dama Sarham ba musu yace gobe zai kawo masa su (in cash) ya karbi takardun wurin bisa idanun shaidu kwarara da sabon mai unguwa.

Bayan ya bar Kofar Na’isa kasa komawa gida yayi, ya kuma kasa tuka motar, ya koma gefen titi ya kashe motar ya kifa kansa a kan sityarin, yana tuno fuskar HAUWA-KULU da kyawawan manyan idanun ta da ya nakasta mata su bisa kuskure, da kuma murmushin Innar ta. Daga baya ya ja motar ba tareda ya san wurin zuwa ba, haka yayi ta yawo kwararo-kwararo titi-titi a cikin BADALOLIN KANO, ya taho tun daga Kofar Na’isa, ya isa Kofar Gadon kaya, ya bi ta kofar Dukawuya, ya bulla ta kofar Kabuga, daga can ya karya kan motar yayi kofar Kansakali, ya taho har Kofar Ruwa, bai ga ko mai kama da Inna ko diyarta Hauwa ba, ya dawo baya ta cikin gari ya bulla ta Sabuwar Kofa, kafin ya isa kofar Nassarawa ya dawo da baya ya isa kofar Dan agundi yana ta fatan Allah yasa ya ga Inna da Hauwa koda a hanya ne, amma har duhu ya baibaye sararin samaniya, wanda yasa ya daina shaida fuskokin mutane, kuma man motarsa ya kusa kafewa, ko mai kama da su bai gani ba, duk kuwa da irin kallon kurillar da yake yiwa mata da musaki bisa tituna da Kofofin Kano, da cikin unguwannin Badala.

Allah sarki Dr. Sarham! Kafin ya koma gida har rama yayi, yayi zuru-zuru yayi dan wuya sabida yunwa da damuwa da gajiya da bacin rai. Kamar ba sabon ango ba, na Madinah bada kanka a sare! Ya koma gida a jigace, wajen karfe goma na dare, amma sai ya kasa zaman falon duk kuwa da cewa ya gansu a zazzaune duk zaman jiran dawowar sa suke yi har Abba, domin a bashi hakurin laifin Surayyah gareshi. 

Ganin yana nema wucewa dakin sa bayan ya gaida Abba da Mama, ba tare da ya ko zauna an yi hira yadda aka saba ba. Abba ya dakatar da shi, ta hanyar bashi kujera da hannun sa ya ce ya zauna, Sarham ya tsaya a tsaye kamar mai ciwon kafa, sai Abba yace,

     “lelen Abba daga ina kake haka, kamar an maka dukan tsiya? Ka gan ka kuwa?”.

    Sarham bai yi aune ba yaji wata irin hajijiya na neman kayar dashi saboda yunwa da gajiya, ba shiri ya lalubi kujerar ya zauna yace “wash! Abba, kai na!” Ya kama kannasa da hannu bibbiyu. Abba ya ce “sannu, Sumayyah kawo masa ruwa da abinci, hajijiya ai yunwa ce, me ke faruwa?” 

    Sarham bai san lokacin da yace “Abba na neme su na rasa, ba inda ban dub aba, ba Badalar Kano da ban zagaya ba, ko mai kama dasu ban gani ba, duniyar nan cike take da azzaluman ‘yan uwa Abba, kowanne dan uwa ya samu faraga sai ya ci amanar dan uwan sa in baya nan, why?”

Surayyyah ta saka kuka don ta dauka wannan maganar da ita Sarham yake ta ce “wallahi Bhaiya ban yi da niyyar cin amanarka ba, na tuba ni kam na shiga uku!  Ka dauki abinnan da zafi har fiye da kima Bhaiya” wata uwar harara daya zabga mata ya ce a fusace “na saka ki a cikin magana ta? Kin san wa nake nufi ko su wa nake magana akan su?”

     Mama ta ce “kayi hakuri Sarham, zancen nan ya wuce don Allah bazata sake ba na mata fada sosai”.

     Yace Mama ni ba zancen ta nake ba Mama, already na yafe mata, na fadawa kaina da kaina na yafe mata yafi sau shurin masaki, tun fita ta ban fita da ita a raina ba, zancen su Inna da Hauwa nake,”

     “Su waye kuma Inna da Hauwa kuma?” 

    Abba da Mama har suna hada baki wajen tambaya, da tunanin ko gamo yayi, ya ce “yarinyar da ta makance a hannu na, (excuse me) na makanta ta by mistake, tun daga lokacin kuma nake kula da karatun ta.”

     “Au ho!” in ji Mama, ai kuwa ban manta da zancenta ba, da yadda ka shiga damuwa a lokacin, har yanzu idon nata bai gyaru ba? Kuma wai basu da Uba ne?” 

    Sarham ya baiwa iyayen sa kaf labarin su Inna, tun ranar da suka fara haduwa a asibitin Murtala, da aikin da yayi mata da sabon da ya shiga tsakanin su aftermath wato bayan hakan, da yadda aka yi ya kai Hauwa makarantar (Special School Kano), da yin sallamarsu lokacin da zai tafi Jeddah, zuwa yanzu da ya dawo yaji abun da ya faru da su daga kanin Baban ta, ya kuma gaya musu batan Malam Bilyaminu tun kafin haduwar sa da su. 

    Mama don tausayi har da kwallah tace “Allah to ya jefa su a hannu nagari, ya kuma bata lafiya a duk inda take, kai kuma ya baka ladan taimako”. Abba yace “amin, Allah kuma ya saka musu. Ya bi musu hakkin su. Amma don Allah ka ci abinci, ka huta, ka nutsu, ka tuna cewa kaifa sabon Ango ne akwai nauyi yanzu a kan ka.

Ya gaya masa cewa sunyi waya da Daddyn Madinah dazu, nan da kwana uku za’a taho da ita Kano, ba sai ya koma Jeddah dauko ta ba, Babanta yace ya daina cewa ango ya zo ya dauketa kasa-ya-kasa tun daga abinda ya faru kan mijin ta na fari, ina ya tanadar mata domin a sauke ta? 

    Sarham babu wani doki a tare da shi don zuciyarsa bakidaya bakikkirin take, yace shi ginin da ya fara bai kammala ba, sai dai Abba ya ara masa gidan sa na Rimin Gata (nan baya sabuwar jami’ar Bayero) a sauketa acan. Yace amma in son samu ne shi ya fi so Madinah ta zauna a nan gidan su tashin farko, ba don komai ba sai don ta saba da su Mama tunda na dan lokaci ne zasu koma Jeddah. 

    (A baya baiyi niyyar komawa Jiddah ba amma yanzu Kano ta fice masa a rai). Daddy ya ji dadi sosai, don a yadda na gina rayuwar iyalinsa da so da kaunar juna, kwarai yake so matar duk da Sarham ya aura ta zamo daya daga cikin iyalin sa, baya so don yayi aure yayi nesa dasu, musamman saboda shakuwar sa da kanwarsa Sumayyah, shakuwar dake tsakanin su har tsoro yake kada yayi aure mace ta zamo sanadinta, Abba ya ce,

     “shike nan hakan yayi kyau, madallah, ita Sumayyah sai ta koma dakin Surayyah, su zauna tare for the mean time, sai a gyara ma Madinah dakin Sumayyah ta zauna har zuwa lokacin da zaku koma Jeddah din, Abba ya tambayeshi ko ya gama kwas din sa? kuma yaya batun aikinsa na Murtala da yake batun komawa? Ya gaya masa cewa ya gama, amma zai koma bikin kammalawa da karbo shaidar kammalawa, shi da Madina har yanzu basu zauna (officially) sun magantu sun yanke shawarar inda zasu zauna ba. Amma yanzu kam yafi so ya koma Jeddah. 

    Bayan ya koma dakin sa yayi wanka ya yi sallolin dake kansa sai ya samu kansa da zama dirshan akan dardumar sallahrsa ya rasa abinda ke masa dadi, abun mamaki ga kiran Madinah na ta shigo masa akai-akai don tun bayan da aka daura musu aure basu yi magana ba, amma ga mamakin sa ya kasa dagawa, a lokacin damuwar da yake ciki tasa komai ya fita kan sa, ya samu kan sa da daga hannu yana yiwa su Hauwa addu’a, damuwa tasa a ranar ko runtsawa na awa guda bai iya yayi ba.

Washegari yaje ya kai kudin filin gidan su Hauwa, ya karbi takardun filin a gaban kwararan shaidu dattijan unguwa su malam Isa da sabon mai unguwa, kowa yana ta mamakin ko me zai yi da filin, shi ba dan unguwar ba, ba kuma dan Malam Bilyaminu ba, amma dai ai yace shi dan uwan Innar Hauwa ne. 

    Wayar da ya sayawa Inna sai ya samu kansa da mallakawa Malam Isa, ya kuma karbi lambarsa yace zasu dinga gaisawa kuma zai dinga turo masa kudin abincin dabbobin Inna da yake kiwata mata, ya fadi hakan ne a lokacin suna cikin garken dabbobin, suna zagawa yaa kallonsu, ya ga yawan su ya karu nesa ba kusa ba akan sanin da yayi musu, sosai ya jinjinawa Malam Isa da iya kiwon dabbobi da zuciyar makwabtaka irin ta mutanen da, ya kuma yanke shawarar taimaka masa akan kiwon dabbobin shima daga ranar da kudin abincin su.

Malam Isa yana ta murnar mallakar waya, saboda a lokacin bata zama a hannun talakawa, ya sakawa Sarham albarka yafi cikin carbi. Da zasu rabu kuma Sarham ya gaya masa niyyar sa, wato yana so ya gine filin nan, so yake ya a gina musu gida kwatankwacin nasu a filin su, gini na zamani, ya ce shi ba mazauni bane don haka zai turo magina kuma zai bar komai a hannun sa da masu ginin, yana so Malam Isa ya kula da ginin har a gama, don zai jima bai dawo Kano ba.

    Malam Isa yana ta mamaki, ko meye alaqar wannan matashin mai kirki da kyakkyawar zuciya da su Innar Hauwa haka, haka suka yi sallama bayan Sarham yayi masa kyautar kudi, kuma a washegari aka saka tubulin harsashin ginin gidan su Inna da kudin da jima yana Tarawa don yin nasa ginin gidan.

Kwana uku bayan nan, ba abinda Sarham yake yi sai yawo a cikin garin Kano yana faman neman INNA da HAUWA har tambaya yake yi ko an san su, ya fasalta kamannin su, maimakon ya maida hankali wajen shirin taryar amaryar sa Madinah-Munawwarah mai isowa daga Jiddahn Saudi Arabia.

Amma ko wanda yace ya san mai kama da su bai samu ba. Wannan yasa duk zaman garin Kanon da dokin amarcin dake gaban sa ya kara fita a ran sa. Ya sa a ransa da Madinah ta zo bazasu dade ba kamar yadda yayi niyya zasu koma Jeddah, in yaso ya karbi tayin aikin da aibitin “SAUDI-GERMAN” suka yi masa, wanda a baya yaki karba, don ya so ne ya dawo gida kwata-kwata ya cigaba da aikin gwamnati a manyan asibitocin Kano da ya tabbatar sun fi bukatar sa, in yaso ya bude private clinic nasa na kansa ya hada, amma a yanzu bai san haka zuciyar sa ta dauki su Inna da matukar muhimmanci ba sai yau da take gaya masa rashin su ba zai sa ya ji dadin zaman Kanon bakidayanta ba, duk da gatan iyaye dana ‘yan uwa dake baibaye da shi, ga na cikar buri, wato na mallakar Madinah abar son sa. 

    Amma duka ya kasa enjoying ko daya. Saboda wasu bare? Ya ilahi, wane irin abune haka??? Shi kansa yana mamakin karfin ‘bond’ din dake tsakanin sa da ‘Inna’ don bazai ce ‘Hauwa’ ba.

    Don haka sai mu ce Amarya Madinah ta shigo kasar Nigeria da kafar hagu, don kuwa likitan zuciyarta Sarhamu babu walwala kota kwabo a tare da shi, gabadaya ya birkice da neman Inna da Hauwa, har iyayen sa suka fara damuwa da saka ayar tambaya, suka zaunar da shi suka ce ya gaya musu gaskiya, bayan tausayi da taimako, meye alakar sa da mutanen nan ne? 

    Ta yaya zai yi sabon aure amma ya raba hankalin sa da nutsuwar sa, ai sai suma ya saka su a damuwa.

    Sarham ya ce babu wata alaqa tsakanin sa da su, sai kauna ta fisabilillahi da haduwar jini, yace shi kawai yana tunanin a wane hali suke ciki ne, yana tsoron fadawar su mugun hannu ko fadawa hannun kanin uban Hauwa wanda baya kaunarsu kuma azzalumi ne, sannan basu da kowa da zasu kira nau in ba shi din ba (Zakari). 

    Mama tayi fuska ta ce daga yau bana son ka kara fita neman su tunda dai ba kananan yara bane, Allah shi yake kula da bayinSa marassa karfi da masu karfi, kafin ka shiga rayuwar su ai babu uban nasu, kuma hakan bai hana su rayuwa mai kyau da shaker numfashi ba. Saidai ban sani ba ko kana da wani dalilin a kasan ran ka a kansu bayan wannan?”

    Wai meyasa mutane suke kasa fahimtar sa ne akan Hauwa da Innarta? Zai iya rantuwa babu wani dalili a kasan ransa a kansu bayan wanda ya fada musu. Kwatakwata kenan babu alaqa ta mutunci da zumunci a tsakanin al’ummar Annabi sai mai kunshe da MANUFA? Haka mafa Sumayyah ta taba cewa wai….. abun babu ko dadin ji domin kuwa yadda yake kallon ta muharramar sa haka yake kallon HAUWA-KULU.

Can tsakar kansa ya tsinkayi sautin Abba yana cewa “talakawa nawa ne a Nigeria da suke cikin halin kaka-nikayi? In ka ce duka sai ka tsayawa rayuwarsu ka hada kan ka da abinda ba zai taba yiwuwa ba, tunda dai kayi taimako iya yinka wanda dace ya kamata ka bar su a hannun Ubangijin da ya halicce su haka, ka maida hankali ga abinda ke gaban ka yanzu. Wato sabuwar rayuwar ka ta girma da yah au kanka”.

    ****               ****                  ****

   

            THE ARABIAN BRIDE

M

adinah na gidan kakannin ta bayan saukarsu a Kano, a daren ranar za’a kawo ta wajen Mama, an gyara dakin Sumayyah da kyau wato inda za’a sauke ta da ‘yan uwanta. Gidan ya dauki kamshin turaren wuta dan Maiduguri ko ta ina mai dadin kamshi, Mama da kawayen ta su Barr. Hannatu Mahdi da ’yan uwanta suka shirya karbar amarya da danginta. 

    Har falon Mama aka shigar da Madinah-Munawwarah cikin lullubi, kafin a yi addu’a ta musamman ‘yan rakiyar amarya da ‘yan karbar amarya duk suka watse, gidan ya rage sai mutanen gidan kadai.

     Rana ta farko dasu Mama suka ga fuskar Madinan Sarham. So beautiful da ita, karshen gayu karshen class, Masha Allah.

Mama ta ce a ranta dole kam Sarhamunta ya kamu ya tsunduma iya wuya, Madinah ko daga cikin lullubi kafin a ganta a zahiri an san matar manya ce kuma ‘yar manya ce.

    Tayi fatan Allah ya basu zaman lafiya da zuri’a mai alkbarka. Ya kade fitina, ya basu ikon sauke amanarta da aka damka musu.

    Yau Madinah ta samu kanta a gidan surukan ta wato iyayen Sarham suna ta haba-haba da ita. Sumayyah da Surayyah ma ba’a bar su a baya ba wajen kula da bakuwar tasu, Surayyah kuwa duk da ‘yar tsamar dake tsakanin ta da Sarham sai da ta kasa shiru, da ya shigo gaida Mama bayan ya dawo gidan da daddare sosai tace dashi.

     “Yaya Doctor, wallahi ka iya zabo mata, class iya class malam, kyau iya kyau, dubi mata kamar hurul- eeni, kamar ita tayi kanta don kyau da gayu.

Wata mummunar harara Sarham ya zabga mata yace “ki fita idona in rufe, ki bar shiga harkata, na rantse Mama ki raba ni da Surayyah”. Sannan ya gaida Mama da gajiyar hidimar jama’a, wadda keta dariyar masifarsa, Mama tace “ban taba ji ko ganin ango yana masifa ba, duk wani ango far’a yake yi da farin ciki banda kai, tashi ka shiga dakin Sumayyah Madinah din tana can”, cikin jin nauyin Mama irin wanda bai taba ji ba a rayuwarsa yace, 

    “Mama ki barta, sai da safe in Allah ya kaimu zamu gaisa in sha Allah, a barta ta huta, na san ta gaji, gata bata jure hayaniya”. Nan kuwa kunyar idon Mama ya hana shi zuwa yiwa Madinah barka da sauka cikin rayuwarsa.

Sai da ya koma dakin sa yayi shirin kwanciya sannan ya kirata a waya, Madinah ta fito wanka kenan tana saka kayan barci zata kwanta kiran sa ya shigo mata, sai da ta ja aji, don taji haushin kiran data yi masa bai dag aba kuma bai biyo bayan kiran ba, kafin ta dauka da kyakkyawar sallama a bakin ta, maimakon ta ce tayi fushi, saboda bai zo inda take ba tun saukar ta a Kano, ko irin kananan korafin nan na amare da ke cikin lokacin da ake mararinsu, ina! Madinah nata salon daban ne, da wuya kaga bacin ranta akan abu, komai tana kokarin maida shi ba komai ba a rayuwarta (banda kishin Sarham), don ko shi Sarham zai rantse bai san me yake bata ran Madinah ba, sai ta karya murya cikin rangwadarta da zakin muryarta tace,

     “daga jin muryar ka mura kake, ina fatan angon Munawwarah yaci abincin dare?”

     Sarham yayi wata wawuyar ajiyar zuciya, tuni ya manta da kishin da yaci alwashin gasata akansa da zarar ta shigo gidansa, wato fushin aurenta da AVM Alkali, ya samu kansa da cewa “kayya! Anyway, kin zo lafiya Madinahtul-Munawwarah, ya gajiya ya aka ji da zafin garin mu?” 

    Madinah tace “garin ku kai kadai? Ai ba’a canzawa tuwo suna. Zafi kuwa ai yana Saudi Arabia”, yace “kiyi min alfarma mu Arabian Bride, na san ke dinnan ma’abociyar tsinkaye, fahimta, da yi min uzuri ce, bazan iya shiga dakin Sumayyah inda kike ba kusa da dakin mahaifiyata ne, ba zan iya tsallake dakin Mama a gidannan in dinga zuwa inda kike ba, amma already nayi kokari nayi mana booking na komawa Jidda, don ni garin Kano ya fita kaina, zamu tashi rana ita yau in sha Allah muje mu ci duniyar mu da tsinke.

     Na yanke shawarar karbar aikin nan na Saudi-German”.

    Farin ciki mai yawa ya cika fuskar Madinah da zuciyarta, don dama tana cikin tunanin yadda zata iya rayuwa a garin Kano, ta shiga damuwa akan yadda zata iya rayuwa a Nigeria ma in general, tana dai daurewa ne albarkacin soyayya da yadda kowa nata ke lallashin ta, yayyenta kuma suke gaya mata aure babu inda baya kai mutum har bukka a jeji, amma hakika tafi son cigaba da rayuwa a Jeddah. 

    A can aka haifeta acan ta rayu, acan ta girma. Abinda ta sani ta kuma yarda da shi kawai shine; ko a cikin ruga zata iya rayuwa in dai da Sarham Abbas ne, kuma in dai zasu kasance tare karkashin alfarmar aure da ni’imarsa itada shi har karshen rayuwar su. 

    Sarham ya katse mata tunani, “kin amince ko?” Da sauri Madinah tace “haba-haba ai nima zan fi son hakan, da kunya kam mu kebe ko na minti biyu ne alhalin Mama da Abba suna cikin gidan, Allah ya kaimu lafiya, ni da ka kara mana wani satin ma a kan dayan ya zama munyi biyu tareda su kafin mu koma”. Yace “no, zamu tafi rana ita yau in sha Allah bana son zaman garin ne”. Ya tambayi Madinah ko me take yi yanzu? Ta ce ta yi wanka ne zata kwanta, ta gaji sosai, tace tun saukarsu a Kano bata huta ba. Sarham ya ce,

     “ai kuwa baki ga ta barci ba, kamar yadda nima ban ganshi ba. On this special day, ki tashi ki dauro alwallah ki yi sallah raka’a biyu nima zan yi yanzu, mu godewa Allah da ya cika mana burin mu da cikar alkawuran da muka yi wa juna yau shekaru goma! 

    Kada ki manta a cikin sujjadar ki ta karshe ki roka mana ‘long life, prosperity, blessed children, unending love, and infinite peace. Madinah ina fatan ki zamo min ‘shelter’ kamar yadda birnin Madinah ya zamowa Annabin mu Shelter, refuge, security, safety and peace!”.

Madinah ta lumshe idanunta cikin farin cikin da bazai misaltu ba, tace “kaima ina rokon ka roka min aljannah, don Hajjah Ramlah ta gaya min aljannah ta yanzu ta tashi daga dugadugan su ta dawo bisa dugadugan ka.

     Ka roka min ‘ya’ya masu yawa tare da kai kuma masu albarka, ka roka min Allah ya mallakamin zuciyar Sarham dina, nikadai raina bakidayan ta, don itace kadai ‘weakness’ dina a duniya (zuciyarsa)”.

Finally, daga yau dai, sunansu ya tashi da ‘honorifics’ tunda ya koma Mr&Mrs. Dr. Shanono. Bayan tarihin fafutukar soyayyar shekaru goma!!!

  ****          *****             ****

A kwanaki bakwai din da Madinah tayi a gidansu Sarham, ta saba da kowa, kuma ta samu karbuwa ba laifi a wurin iyayen sa musamman Abba Prof. da yake ganin girman Kakan ta mai rasuwa Alkalin Alkalai, duk da ba wai sanayya ce a tsakanin su ba, amma yayi masa farin sani a matsayin daya daga cikin iyayen Kano. Ta fannin Mama kuma, ta zauna ne daga gefe tana laqantar Madinah a ma’auni na adalci da son sanin hakikanin halayen ta, inda a dan zaman su tare ta fahimci Madinah wayayyace, Madinah mai ilmi ce, bata da matsala sai ta rashin kawaici a kan Sarham, in bata gan shi ba sai ta ishi kannen sa da tambayar ina yake, wanda ke nuna zata yi kishi akan sa sosai, idan ya fita bazata nutsu ba sai ta ji shigowar sa gidan, tana da bala’in jan aji amma akan Sarham babu ajin ko kadan, don bata iya boye son da take masa a gaban iyayen sa da kannen sa. 

    Gata da halaye na kowa tasa ta fishshe shi, wato halayen nasara, kai bazaka ce girman kasar larabawa bace, amma kuma duk da haka tana girmama su, musamman su iyayen sa, ta fahimci Madinah ta san abinda take yi yadda ya kamata, tunda duk rashin kawaicinta data fahimta, a duka kwanakin nan bakwai data yi tare dasu, bata tsallake su ta kebe da Sarham ba, ko ta bi shi inda dakinsa yake, ita da shi sai ko a waya, ko in ya shigo ya taddasu duka a falo, sai ya zauna ayi hirar tare da shi, amma baya sakewa musamman in Mama na wajen, tana kallon Madinah na kashe shi da murmushi. 

Shi da kan sa Sarham ya fahimci wani abu, wato tun bayan zuwan Madinah, mu’amalar sa da Sumayyah ta ja baya, Sumayyah ta daina shiga sha’anin sa sam, ko wuri ya shigo tana dariya sai ta daina, ta yi fuska. Ta daina kai masa abinci ko gyaran dakin sa wanda aikinta ne. A’ah, tun baya damuwa har ya fara tunanin laifin me yayi mata don wannan ba halin ta bane, me yasa ta daina ajiye masa abinci ko kiransa yazo ya ci, da gyara masa daki alhalin ta san ba wai Madinah ta tare bane, da zata cigaba da yin wadannan hidimomin da tazo ta tarar tana yi masa. 

Yau ya fita can karshen layin su yana wata irin romantic waya da Madinah, don hakurinsa kusan ya fara karewa da takunkumin da ya sanya musu, haka suke yi yanzu kullum da yamma in jama’ar gidan basa nan ko suna wasu sabgogin a kitchen, ko can dare in kowa ya kwanta, sai ga Sumayyah ta karyo kwana tana tafe cikin nutsuwa, ta zo har inda yake ta gifta shi bata ce masa ko sannu ba, har ta zarta shi kadan ya kashe wayar ya saka a aljihu, ya ce,

     “Sumayyah!”.

    Sumayyah ta dan dakata amma bata juyo ba, ta daure fuska sosai, ya ce “ko ba da Sumayyah nake magana bane?”

     Ta dawo ta tsaya a gaban sa tana tura baki gaba, ya ce “kin gama hada kayan naki?” Ta ce “hada kaya kuma? Ina zani?” yace “eh, Abba bai gaya miki da ke zamu tafi Jeddah ba, zaki zauna a gida na ki fara MBBS? Tukunnama wai me nayi miki kike gaba da ni haka? What’s wrong with you?”

     Sumayyah mai neman kuka an jefeshi da kashin awaki, nan da nan ta soma hawaye na babu gaira babu dalili, tace “wallahi in dai a gidan ku zan zauna to na fasa karatun a can, ni ba don kai da matar ka zan je Jeddah ba, ba ‘yar zaman daki kuka samu ba, zani jami’ar Sarki Abdulazeez ne, zaman karatun kaina, kowa yayi rayuwar sa a inda yake zaune duk da muna gari daya”. Cikin madaukakin mamaki Sarham ya ke duban Sumayyah, da babbar murya yace “Summy! Kina cikin hankalin ki kuwa? Ko kin fara shaye-shaye ne?” Sumayyah ta murgude baki gefe tace “Allah ya sauwake in yi shaye-shaye, kawai dai… ni bazan zauna a gidan ku bane, in ba hostel za’a kaini na zauna ba, to a nema min admission a BUK”. 

    Cikin kokarin hadiye fushi da bacin rai da ke tunkudo masa Sarham ya ce “to na ji, matsalar ki ce wannan yin karatu a Jeddah ko barin sa bakidaya, amma ki gayamin dalilin ki na kulla gaba da ni, da fita sha’ani na alhalin ba haka muke nida ke ba, sai yanzu da na yi aure, bayan kinsan mata ta bata tare ba balle ta cigaba da yimin hidimar da kike yi min”.

     Sumayyah ta ce “Bhaiya, kaima gashi nan aika fada da bakin ka, “KA YI AURE!” Tunda kayi aure ni ba ruwa na da harkar ka gaskiya, kada wataran azo an araba ni dambe da matarka don na fahimce ta mai kishi ce, sannan na san wannan matar taka mai kama da larabawan aljannah, ba zata barni da kai ba sai ta raba mu, ga shegiyar kissa da kinibibi da rashin kawaici a kanka, tana wani kalmashe murya kamar kyanwa, shiyasa tun yanzu na raba kaina da kai, ba sai ta raba mu in zo ina jin zafin ta ba”.

Sarham baki bude yake kallon Sumayyah, yaki yardarwa kansa bata sha kwaya ba, yana ji ana cewa wai kanne na kishi da matan yayyun su, bai taba yarda ba sai yau.

Sai ya kwantar da ido da murya ganin Sumayya na share hawaye kuma, tana tuno irin tsananin shakuwar dake tsakanin ta da Bhaiya, yau ga wata ta zo ta shiga tsakani, ta fita kusanci dashi, kuma ta san ta shigo rayuwar su kenan har abada, bazasu kara samun kusancin da suke da shi ba ita da shi yanzu, saboda matar sa.

Yanzu kam ya yarda Sumayyah bata sha komai ba, ‘inner feelings’ dinta kenan, wanda ya sabawa hankali, shi take fada masa ba karya take ba, ba kuma hassada take yi wa Madinah ba, a’ah tata damuwar ce ta karan-kanta, saboda yadda ta damu da zumuncin da ke tsakanin ta shi.

Yace “Sumayah kada Allah ya baiwa kowacce irin mace da zan aura iko a kaina, ba a kan ki ke kadai ba, har iyayena da Surayyah, kada Allah ya dora min soyayyar da zata rufe min idanu in canza muku da wani abu saboda mace, ko in yanke zumuncin dake tsakanin mu, ko in kasa kyautata muku da kula da rayuwar ku”. 

    Sarham ya ja mumfashi a hankali, kafin yace “My sister Sumayyah, ki taya ni addu’a kin ji?” 

    Sumayyah tace “ai son da kake mata yayi yawa ne, Yaya Sarham ban so ka auri macen da son da kake mata ya rinjayi nata ba, don tsaf! Zata raba ka da kowa naka”. 

    Sarham yace “Sumayyah wannan tunanin ku ne irin na mata, ki bari ki ga kamun ludayin Madinah tukunnah, ina tabbatar miki Madinah daban take da sauran mata, don bata tashi anan ba, kuma bata tashi cikin mata ba sai ‘yan maza, duka wadannan halayen na mugunta bata san su ba, I assured you. 

    Madinah mai ilmi ce kuma mai hankali, ta san abinda take yi kin ji?”

Da wadannan kalaman ya samu yayi ta lallashin Sumayyah, har ta dan saki fuska ta daina kukan, amma tayi masa rantsuwa akan ita ba zata zauna a hannun Madinah a Jeddah ba, a makaranta zata zauna. Sarham yace “in aka barki kika zauna a makarantar shikenan baki da damuwa?”  tace “eh, saboda matar ka ce raina baya so” ya ce cikin rashin jin dadi, “to na yarda, ban kuma isa in sa ki so ta dole ba, amma don Allah Sumayyah kada ki kulla gaba da Madinah akan haka, mai son naka masoyinka ne ba makiyin ka ba, ki bata dama ki ga irin halayenta”.

     Sumayyah tace cikin jin tausayinsa “toh!” ya ce “zaki gyara min dakin nawa yanzu? Yau kwana bakwai baki share min ba, ban ci girkin ki mai dadi ba kanwata ta kaina”, tayi dan murmushi tace “zan gyara dakin, for now, amma ka cire ni daga dafa maka abinci da gyara maka daki kaima daga yau, ka koyi cin na matar ka”.

Da wannan suka tako a tare zuwa cikin gida. Sumayyah ta je ta gyara masa dakin sannan ta tafi hada kayan ta da zata tafi da su Jeddah, tana cikin hada kayan Mama ta kirata tace taje ta zo da Madinah, zasu fita ssallama gidan Hajiya Kulu su kuma gaishe ta bata jin dadi.

    Sumayyah ta bata rai, tace “Mama why not Surayyah ta kira miki ita? Tunda tasu ta zo daya?” Mama ta ce “ke bana son rashin hankali kishin kannen miji, ki raba kan ki da wahalar da bata da amfani, tunda ke dai bazai aure ki ba, ita din da baki so ita Allah ya halatta masa”. 

    Sumayyah tana kokarin ta hadiye bacin ranta, ta ce “Mama Allah ya sawwake in yi kishin Yaya na, kawai ni I DON’T LIKE HER! AND I DON’T KNOW WHY?” Sai tasa kuka.

     Mama ta rungume Sumayyah tana lallashin ta, a lokacin tayi ta kokarin ganar da ita hakan bashi da amfani kuma kuskure ne, in har tana so ta zauna lafiya da dan uwanta dole taso matar sa wadda bada jimawa ba zata zama uwar ‘ya’yan sa. Ta tilasta mata kan ta je ta kira Madinah da kanta su tafi Gadon Kaya tare. 

    Ko da ta shiga dakin Madinah na waya da Sarham, ana kalmasa harshe da larabci ziryan, cikin wani ‘accent’ dinta da shi kadai take yiwa magana da shi. Kyabe baki Sumayyah tayi ta ce,

    “in kin gama an ce ki zo mu tafi Gadon kaya”. Ta juya tayi ficewar ta.

Batun yau ba Madinah ta fahimci Sumayyah bata yin ta, ba kuma don tayi mata wani laifi ba sai don a matsayin ta na masaniya akan halayen mata ‘yan uwanta psychologically ta gane Sumayyah irin kannen mijin nan ne masu kulafucin zumunci da yayyensu. Wanda hakan ke sawa su kasa shiri da matan su na aure don a ganinsu zasu raba su, amma ta san Surayyah sosai take yin ta, halinta daban dana ‘yar uwarta, itace ‘yar dakin ta, tasu tafi zuwa daya, kullum sai ta zo mata hira.

    Madinah tasa a ranta daga yau zata fara kyautatawa Sumayyah. In har kyautatawa na sawa a so mutum, to Sumayyah sai ta so ta, don an ce zuciya na son mai kyautata mata.

Sun je sun gaida Haj. Kulu Surayyah ce ta tuka su a motar Mama su uku, daga nan suka dan zazzaga da Madinah taga gari, sune har Gidan Makama Museum da Gidan Dan hausa, Madinah ta roki Surayyah bayan sun gama zagayen da su je ‘main house’ din su a SoronDinki.

Tun daga gate suka tabbatar sun zo babban gida, kuma tun daga karbar da akayi musu suka yarda gidan su Madinah gidan karamci ne da karrama baki. Sannan ana ji da Madinah a family dinta. Basu jima sosai ba tayi sallama da Kakar ta da sauran ‘yan uwan ta suka koma gida.

Washegari ya kama ranar da zasu koma Jeddah, shiri sosai Mama ta yi musu na kayan abincin da babu a can, su maggi dunkule, ta kuma yi musu dambun nama mai yawa, gasu alkaki, dubulan, nakiya, bakilawa da gireba na cikin garar Madinah da aka kawo, duk tasa an shirya musu a jakunkuna daidai kilo dinsu, Sarham yayi sallama da iyayen sa da Kakar sa Haj. Kulu. Surayyah ta dauke su a motar Mama tayi musu rakiya zuwa filin jirgin malam Aminu Kano, suka tashi su uku wato, Sarham da Madinah, da kanwar sa Sumayyah wadda zata fara karatun medicine karkashin kulawar Yayan ta a birnin Jeddah.

******                *****                *****

S

umayyah Allah-Allah take su sauka a Jeddah, ta kama hanyar makaranta, ta kyale Sarham da matar sa, don ta gaji da ganin salo da rashin kawaici irin na Madinah. 

    Bayan saukar su a Jeddah hidimar makarantar Sumayyah ya fara yi, tun ma kafin su tare a gidan su, Madinah ta sauka wajen iyayen ta kafin a gama shirya musu gidan su da Saudi-German suka basu a gidajen likitocinsu, cikin kwanaki uku da saukar su har Sumayyah ta fara karatun ta, aka bata daki a hostel din dalibai kamar yadda tafi so, shi kuma yayi ‘documentation’ na karbar aikin sa a cikin kwanakin da asibitin kwararrun ido na Saudi-German. 

    Dr. Sarham Abbas Shanono ya zama cikakken likitan fidar ido (ophthalmic surgeon), daya daga cikin manyan likitocin idon da Saudi-German ke ji dasu da alfahari su.

     Saida ya kammala ‘documentation’ din sa aka kuma gama shirya musu gidan nasu daga dukiyar gidansu Madinah, daga nan gidan su ya dauketa suka wuce babban birni wato (Riyadh) ta jirgin sama domin barje gumin amarci, abinda larabawa suke kira ‘Shahar Al-asal’ wato (honeymoon) da harshen larabci, inda acan Sarham ya gama gane aya da tsakuwa wato AVM Alkali bai yi masa barnar da yake tsoro ba, tuni ya ware aka barji amarci gangariya da matar da yakewa so gangariya, wanda shi kan sa ya san son da yake wa Madinah mai yawa ne, da har wani lokacin yake tausayin kan sa. 

    Daga ‘first-night’ din su, Madinah ta idasa tashin kan Sarham, domin abinda yake zato ba haka ya sameshi ba. 

    AVM bai yi masa barna ba, bai kuma bar masa sudi ba, domin kuwa shi ya bare alewar sa a leda.

     Suna Riyadh ana barzar amarci a wani babban hotel na kasar, har tsayin sati guda kafin su dawo Jeddah. Dr. Sarham Abbas, ya kama aikin sa ka’in da na’in a asibitin “SAUDI-GERMAN”. 

    ****                   ****                      ****

    Kullum amarcinsu sabo dal yake komawa basa taba gundura da juna. Amma duk da haka Madinah tana ta zuba idon taga Sumayyah ta dawo wajen su da zama bayan dawowar su gida daga honeymoon, amma bata gan ta ba, bata kuma ji Sarham yayi maganar dawowar ta wajen su ba ko sau daya, sai ta tambayeshi a wani maraice.

     “Ni Dr. ina Sumayyah ne? Sumayyah ba a wajen mu zata zauna bane? Ta yaya muna gari daya amma zamu barta ta zauna a hostel?”

     Yace cikin rashin damuwa da maganar “kada ki damu, zabinta ne”. Madinah bata gamsu ba, tace “amma dai Mama bazata ji dadi ba in taji bama tare da ita, kamar mun kasa rike ta zata gani” ya ce cikin kosawa da zancen “Madinah ki yi abinda ke gaban ki kin ji! Ki manta da Summy. Ban san ki da shiga sharo ba shanu ba.

     Summy wata irin hutsuwa ce, bata son shiga harkar mutane kamar yadda kema bakiso kowa ya shiga taki in ba ke kika saka kanki ba, itama haka take”. 

Ya fadi hakan ne don bazai iya gaya mata gaskiyar cewa Sumayyah bata yin ta ba, wanda gaskiyar maganar kenan, jininsu bai hadu ba, wato bata a layin mutanen dake son ita Madinar, ta bangaren ahalinsa. Amma duk da hakan data fahimta da kanta ba tareda ya fito fili yayi bayanin ‘fear’ din Sumayyah a kanta ba, Madinah bata fasa kyautatawa Sumayyah ba, haka kawai zata yi shopping niki-niki ta dauka a bayan mota ta kai mata har dakinta na hostel din, ko kayan abinci ko na shafa. Daidai gwargwado Madinah tayi kokarin jan Sumayyah a jiki ko don ta samu ‘yar uwa mace, kasancewar nata ‘yan uwan duk maza ne amma abin mamaki ko kadan Sumayyah ta kasa son Madinah, ta ki sakar mata jiki. 

    Sarham ya sha zama yana lallashin Sumayyah a bayan idon Madinah, kan ta bude zuciyar ta wa Madinah, ta dauka ita da shi ba banbanci, wato ta dauketa matsayin Yayar ta kamar yadda ta dauke shi Yayanta, amma taurin kai irin na Sumayyah akan Madinah ya ki canzuwa, Sarham ya danganta hakan da rashin haduwar jini kawai a tsakanin su, tunda shi kam ai zuwan Madinah bai sa ya canza ma kannen shi ko iyayen shi da komai ba.

    To haka Surayyah ma dake can gida tana shan aiken kaya daga Dr. Madinah duk lokacin da ta samu mai zuwa Kano, lazim ne ta yiwa Surayyah aike. Haka koyaushe suna like a waya tasu kam ta zo daya, amma Sumayya kullum ranta kara nesanta yake da shiga harkar Madinah, saidai ta yarda auren sa da Madinah, da kuma uwa uba zazzafar soyayyar da yake mata kamar ya hadiye ta duk basu sa Sarham din ya canza musu ba su kannen sa da iyayen sa.

“Madinah-Munauwarah”, cikin watanni uku ta zama GIWAr mace a gidan ta, shi da kan sa Sarham in yayi nishadi GIWAR SARHAM yake kiranta, Madinah ta samu fada a wajen mijin ta yadda ba’a zato, saboda tarin baiwarwakin da Allah yayi mata musamman na iya masa da duk fitinar sa a shimfida, Madinah ta yarda da gaske ko a cikin maza nata mijin daban ne a fannin shimfidarsa da matar sa, ta iya kalamai masu sanyi da sanyaya zuciyar miji a duk halin da yake ciki, ta kalmashe shi da iya girki na zamani,  da iya kula da shi a shimfida, ta kware wajen taya shi kula da tsaftar jikin sa, kula da kannen sa wadanda ta gama lura baya hada kaunar su da komai a ransa saboda irin ‘upbringing’ din da iyayen su suka yi musu kenan na kaunar junan su da hadin kai a junansu, kasancewar basu da yawa a wurin iyayen su.

    Madinah irin matan nan ne masu nacin shiga (educational programs) da ake yi a Saudi-Arabia, duk wasu programs irin na (marriage coaches) na mata musulmi masu burin karawa juna sani akan ilmin zaman aure da zamantakewa da ake yi a kasa mai tsarki ko na likitanci komai nisan gari zaka samu Dr. Madinah na kokari ta halarta, wannan ya karawa Madina (exposure) akan ilmin data ke da shi.

    Domin bata tsaya ga bangaren karatunta na likitanci kadai ba, a’ah, tana kara fadada ilmin ta a kan zamantakewar aure da zamantakewar al’umma, tana da yawan rubuce-rubuce (wadanda bata wallafawa) akan sha’anin mata da aure musamman da bata fara aiki da kowanne asibiti ba a lokacin, kullum cikin bincike take a yanar gizo kan yadda zata kara inganta kimar ta a gidan auren ta.

     Ko wata uku ba’a rufa ba da auren su, Madinah ta fahimci yaron ciki na wata guda a tare da ita.

     Ciki irin silent dinnan (mara laulayin nan), cikin data kira da suna DAN SO. Yo dan ta da Sarham ai dole ta kira shi DAN SO wanda tarihin soyayyar shekara goma ne ya samar da shi ‘sharp-sharp’ kamar a dokin kofa tayi tuntube da cikin sa. Koda cikin ya soma girma ya shiga watanni biyar bai hana ta komai daga harkokin ta ba, amma yasa ta fasa karbar tayin aikin da ta samu da Dr. Siddiqah hospital, domin ta zauna a gida ‘fully’ ta raini dan So, ta kuma baiwa ubansa kulawar da zata gusar da hankalin sa daga kan sauran mata.

    Addu’ar ta kullum Allah yasa abinda ke cikin ta namiji ne, tana fatan yayo kamannin Sarham, da halayen sa da kwakwalwar sa. cikin ‘yan watannin da ta kasance kullum a gida Madinah ta kara kaimi wajen ganin ta samarwa kanta kyakkyawan matsugunni a zuciyar Sarham, ko dama matsayin ta mai girman ne, to ta kara girman matsayinta ta hanyar kula da shi da bukatocin sa, ta tsare masa cikin sa, ta kware wajen iya girke-giren zamani dana larabawa, ta mallakawa Sarham duk wata kauna, soyayya, kulawa da yardar da diya mace kan yi wa namiji.

    ‘Yan gidan su Madinah na yawan zuwa gidanta, haka Daddy din ta da kan sa sai ya dauko Hajjah Ramlah a gaban mota ya tuko da kansa su zo ganin ta, musamman da cikin ta ya soma girma, dokin su ga haihuwar Madinah kamar a kan ta zasu fara samun jika bayan kuwa jikokin su sun kai goma daga yayyen Madinah, don cikinsu Usman ne kawai bai yi aure ba. 

    Amma a wajen Hajja Ramlah da Dr. Sorondiki na auta Madinah na musamman ne tunda ko cikin ‘ya’yan su ita din ta musamman ce. Don haka sayayya sosai ake ana tarawa don jiran haihuwar.

Cikin Madinah na da watanni takwas Hajjah Ramlah tace a dawo da ita Sorondinki ta haihu a can, ita bazata iya zamar mata jego ba (zaman dabaro), da farko Sarham yace bai yarda ba amma Mama ma sai tace a kai ta, ai haihuwar fari ce, normally a wancan lokacin ana zuwa wankan gida. Don haka bada son ransa ba ya fara ma Madinah shirin tahowa haihuwa, don dama sun riga sun gama sayayyar haihuwar su tuntuni, shi yayi, su Daddy sun yi, Sumayyah ma ta tara kayan baby da yawa iya karfin ta ta bashi da zasu taho, koda bata yin Madina tana maraba da isowar dan ta ko ‘yar ta daga Bhaiya.

    Sarham yana cike da damuwar yadda zai rayu a gidan su shi kadai ba tareda Madinah ba. 

Shi ya kai Madinah gun kakanninta, weekend kawai ya samu yi tare da su Mama ya koma Jeddah. 

    Tafiyarsa da sati uku Madinah ta haihu, ta haifi lafiyayyar diyar ta mace, mai kama da ita, amma kalar fatar jikin da bafulatanar sumar ‘yan Shanono yala-yala ta Sarham ce, Surayyah ce ta fara kiran sa tayi masa albishir, cike da doki. Sannan Mama ma ta kirashi don duk suna asibiti tareda ita aka yi haihuwar, Daddyn Madinah tuni ya fara shirin tahowa Kano tarbar amaryarsa da aka haifa ranar Laraba, “Laraba Tabawa Ranar Sa’a” inji Haj. Kulu. Tana mai jan hancin yarinyar dan sirit da shi.

Ranar da Daddyn Madinah da Sarham suka sauka a Kano kwana shidda cif da haihuwar, da yammacin ranar ya je gidan su Madinah a Sorondinki ya dauki yarinyar yana kallon ta da wani irin paternal love, kafin Madinah ta fito daga daki, ta sha ado, kamar ba itace ta dawo daga kofar lahira kwana shidda a baya ba, Sarham ya daga kai yana duban ta da wani irin murmushi, amma sai me? Sai kwakwalwar sa ta gaya masa cewa kawai ya saka ma baby din Madinah suna HAUWA’U ya dinga kiranta da Maijiddah, in the memory of his lost blind sister (miskiniya KULU).

Madinah ta fito ta same shi da yarinyar a hannu amma yayi nisa cikin tunani, yana murmushi shikadai, sai da ta sakala hannayen ta a wuyan sa ya dawo hayyacin sa, ya sumbaci goshin yarinyar itama Madinah ya sumbaci goshin ta, Madinah duk ta kumbure a hakan ma ta dan sace, “an sha gumurzun haihuwa an zama uwa”, da ya dube ta yaga yadda hancin ta da bakin ta suka bubbude leben ya zama tafkeke saiya fashe da dariya.

    Madinah ta san me yake yi wa dariyar don yanzu itama ta gama kallon kan ta a mudubi kamar ta fashe da kuka, amma wannan yasa ta kara kaunar Hajjah Ramlah, ko ba komai ta ga yadda ta kawo ta duniya ba wasa bane, ta kuma kara girmama lamarin ta fiye da na Daddyn ta. Yo Sarham yana can Jeddah cikin ofishin sa yana shan rabar AC tana labour room tana gumurzu kamar ta sheka barzahu. 

    Kwafa tayi ta cuno bakin gaba tace “ai na gama daga wannan babu kari” Sarham ya sake darawa ya ce “ah haba Madam Dr. yaushe aka yi daren garin zai waye? Yanzu muka fara saka kwallo a raga, sai kin yi dozen Hajjaju wannan ta ladan noma ce, ki rubuta ki ajiye na gaya miki” ya hada su ita da jaririyar ya rungume su, yayi musu kyakkyawar sumba a bakunan su, sannan ya yi mata sannu da sauka, ya kuma saka mata albarka, daga bisani yace. 

    “Allah ya raya mana Nana Hauwa’u, AKA Kuluwa, Kulun Majadun”.

     Madinah ta zaro ido ta ce “sunan tsofaffi zaka saka mata? Ka rufa min asiri don Allah ka sa mata ko sunan Sumayyah mana”, yace “Sumayyah ce ta taya ni haihuwar ta? ko sanda nake shan yakushi da cizo a Riyadh Sumayyah ta zo ta taimake ni?” Madinah ta rufe ido cikin jin kunya tace “kai don Allah SARHAM!” Yace, “of course, sunan da na ga yayi min daidai kenan, Hauwa’u, Hauwah uwar al’ummar duniya, Hauwa uwar matan duniya bakidaya, uwar bil adama”. 

Sai da ya kama hanya a mota zai koma gida yana cikin matsanancin nishadi, akwai contentment mai yawa on becoming a father, ya tambayi kan sa “why HAUWA? Me yasa sai Hauwa zai sakawa ‘yar sa? Bayan in don yake tuna su ne, sunan Inna ya kamata ya saka wato Safiyyah?

     Murmushi yayi, a lokacin yazo zai wuce ta kofar Na’isa, yana kallon kofar wadda aka sake ginewa aka sabuntata, bayan hawan sabuwar gwamnati, sai kawai ya tuna da Malam Isa, kawai sai ya karya kan motar sa ya nufi gidan Malam Isa mutumin sa.

     Tun daga nesa ya hango ginin da yasa ayi na gidan su Hauwa ya kammala, gini ya fito sosai na zamani, amma ba’ayi fenti ba tukunna.

    A zaure ya tadda Malam Isa yana shirya itacensa, ya yi masa sallama, tun daga nesa da Mal. Isa ya hango shi sai ya saki hamdala, Sarham na isowa tun kafin su gaisa yace “Dan nan kana lafiya? Ina ka shiga shekara guda da watanni ina neman ka? Tuntuni nake ta jiran zuwan ka, gashi ban san gidan ku ba, aikin gini tuni an kammala, wayar da ka bani kuma na kasa magana da ita tun lokacin da ta fada ruwan wanka na ta lalace, na sunkuya sai ta fado daga aljihuna ta shige bokitin ruwan wanka, shirun ka yayi yawa baka leko ni ba, in ce ko dai lafiya? Kusan shekara da rabi kenan ban ji daga gareka ba.

     Tun bayan tafiyar ka da kadan nake ta son in yi magana da kai abu ya faskara, in labarta maka abinda ya faru.

    Wato cikin ikon Allah kwanaki Mai kosai (matar sa) ta je tashar Kano line zata hau motar Zaria ta ce min ta ga wata mata kamar Innar Hauwa tana sayar da abinci a tashar, amma bata yi mata magana ba ta fasa tafiya Zaria tazo ta gaya min, don ta san irin neman da mukeyi mata. A take na bar abinda nake yi na bita muka je amma bamu same ta ba, sai wasu mata guda biyu a wajen dake yi mata aiki, muka tambaye su ko anan Innar Hauwa take, tana da ‘ya makauniya, suka tabbatar mana anan take sana’ar ta saidai ba kullum take zuwa ba yanzu, don bata da lafiya, su suke rika mata aikin yanzu, amma tabbas bamu ga Hauwa a wajen ba. 

    Wallahi tun lokacin nake so in gaya maka na rasa hanyar isa gare ka, ni kuma ban kara komawa tashar ba har yau, don a washegarin ranar Sunusi dan waje na ya zo ya tafi damu Ikko, can inda yake sana’ar sa, mun jima bamu dawo ba sai jiyan nan muka dawo nida Maikosai”. 

    Sarham bai cika katse mutum kafin ya kai aya ba, amma hakika yau ya gundura da dogon bayanin Malam Isa, kawai ya ce masa ya ga Innar Hauwa mana ‘short and simple!’ Mikewa tsaye yayi jikin sa yana dan tsuma, yace.

     “Sako takalmanka Malam Isa mu je ka raka ni inda ka gan su suna sayar da abinci din”. 

    Malam Isa ya ce” ai ka bari ka fara duba ginin daka bar min amanar aikin sa ko? Kafin mu je neman nasu, tunda takamaimai bamu sani ba ko har yanzu suna can” Sarham ya kufula, kamar ya kaiwa Malam Isa naushi, don ji yake kamar yayi fiffike ya tafi shikadai. 

    Malam Isa ya ce “to tunda naga ranka ya baci, bari to in kira Halilu ya zo ya zauna min akan itacen nan, in yaso in muka yi la’asar sai muyi maza mu tafi”. Kawai sai Sarham ya samu kansa da ce masa “ai nayi sallah kafin na zo don Allah Malam Isa, ka daina ja min rai, bani da hakuri wani lokacin kamar zawayi nake”.

     Malam Isa yayi dariya yace “ai wallahi sai ka jira ni na yi tawa sallahr, na kuma kora dan farau-farau a cikina, baka ji shi ba kamar bakin akuya tun dazu sai kururuwa yake”.

      Sarham ya koma kasa ya zauna, dabas! Kamar kayan wanki, dole ya jira Malam Isa yayi alwallah a gefe ya hau buzunsa ya tada sallah, ya gama ya jawo kwanon sha a rufe ya sha farau-farau din sa ya koshi, sannan ya dubi Sarham wanda ya kai kololuwa wajen hadiye fushi, Malam Isa yayi dariya yace “irin wannan zama a kasa haka duk ka bata farar shaddar ka, wai ni ko son Kulu kake yi ne, don itama haka take da kyau tubarakallah kamar ka, koda idanun suka makance sai suka kara zame mata gwanin kyau” Sarham bai tanka ba don bacin ran bata masa lokaci da yake yi, yace

     “in ka gama muje ko Malam Isa”. Yayi gaba ya bar shi yana masa dariyar shegantaka wai matuka zai dace da Kulu, don idan ta yi fushi haka fuskarta take komawa kamar balam-balam yadda ya koma dinnan”.

    Sarham yayi masa banza. Ya budewa Malam Isa gaban mota ya shiga ya rufe ya zagaya shima ya shiga, Sarham ya wani irin juya sityarin a guje da hannu daya saura kadan hular Malam Isa ta fado, da haka ya bar kofar Na’isa, suka hau titi sambal. 

    Malam Isa da yaji sanyin AC ta ratsa shi sai ya hau sakin zance ba kai ba gindi, ya ce “na so hada Kulu da Sunusi, tun tana yarinya, na gayawa Malam Bilyaminu kuduri na, sai cewa yayi “shi yafi so ‘yar sa Kulu ta je makaranta, baya son auren wurin nan da muke yi wa yara, ka ga yanzu da ya barta ta auri Sunusi, da ta tara yara sun kai biyar, don bana tantama Innar ta ma irin sa ce shiyasa suke zaune lafiya baka taba jin kansu, su dai makaranta-makaranta kamar goyon Mungu Park, don har bayan data makance wallahi mutanen nan basu raba ta da boko ba, haka muka ga sun samar mata dan jagora kullum sai ta je, ban taba ganin masifar son boko irin na Innar Kulu ba, bayan ita ko a zaure bata taba zama da sunan karatun bokon ba”.

     Sarham ya juya kan mota cikin kwarewar tuki suka shiga tashar Kano line, ko tanka masa bai yi ba yana mamakin surutu maras ma’ana irin na Malam Isa, fadi ba’a tambaye ka ba, da alama bashi da matsala a rayuwarsa sai ta saida itacen sa.

    Malam isa ya wuce gaba kuma har zuwa lokacin bakin sa bai yi shiru ba, yana gaya masa shi ya san dama Innar Hauwa bazata zauna babu sana’a ba, musamman ta abinci, don aljanunta na girki da tsaftane. In ta fara girki duk gidan sa sai miyau ya tsinkewa kowa, saboda kamshin girkin ta, yanzu ma ashe shiyasa ta zabi sana’ar abinci, Malam Isa ya kara da cewa Sarham,

     “to Allah yasa ba’a tashar suke kwana ba, ko don ‘yar makauniyar nan Hauwa-Kulu, kada mazan tasha su dinga yi mata dan kira”.

    “A’uzubillah!” 

    Sarham ya fada a zuciyar sa, lokacin sun kawo kofar rumfar abincin Inna mata biyu da dattijuwa daya suna ta kula da kwastomomi daya na zuba abincin in anzo saya, sukayi musu sallama, suka amsa suna tambayar su “me za’a zuba musu?” Kai tsaye Malam Isa ya ce nawa kwanon shinkafa da wake da miya da nama? 

    Sarham yayi masa kallon takaici ya ce “Malam Isa abinda ya kawo mu kenan?” ya ce “au, yi hakuri na manta ne, ‘yammata Innar Hauwa-Kulu muke nema”.

    Dattijuwar mai zuzzuba abinci ce ta basu amsa. “Ayyah ai Innar Hauwa jiki ya ki dadi, yau wata guda kenan bata zo shagon nan ba, na ji ance ma bata gari, wani makwabcin su ya kai ta gidan mai maganin gargajiya na ‘ciwon zuciya’, a can wani kauye wai Albasu, don Innar Hauwa sam-sam ta ki zaman asibiti.

    Allah ne yayi Innar Hauwa na da nisan kwana da yanzu wani zancen ake akan jinyar ta ba wannan ba”.

    Sarham yace cikin yanayina gigicewa “na roke ki da Allah da Manzon sa ki raka ni gidan nata yanzunnan”. 

    Numfashin sa har gwamuwa yake tsabar yadda ya saka Innar da son ganin su a ransa, dama tace watakila bazasu kara ganawa ba, watakila sallamar su kenan, Allah ya gani yayi duk iya kokarin sa a kan ya san halin da suke ciki a wancan zuwan nasa Allah bai yi sun hadu ba.

    Matar ta sallami kwastomomi sannan ta baiwa ‘yammatan sallahun abinda zasu yi mata kan ta dawo, daga nan ta bi bayan Sarham da Malam Isa zuwa mota.

    Suna tafe tana basu labarin ai Innar Hauwa ta dade a kwance, watakila tayi shekara tana jinya, shagon ma yanzu ya zama nata.

    Don dama haya muke kamawa, a da ina mata aiki ne da ta kwanta ta bar sana’ar sai nikuma na kama rumfar hayar, ba don ‘yar ta makauniyar nan mai kokari ba da tuni Innar Hauwa babu, da tuni ta kashe kanta da ciwo a gida, don bata son maganin asibiti.

    Sarham ko magana ya kasa, yana jin ta ita da Malam Isa suna ta maganar kin asibiti irin na Innar Hauwa, yace ai tun sanin da yayi mata a haka take da akidarta ta amanna da maganin gargajiya.

    Malam Isa yace “kuma fa akan kin asibiti ne har idon Hauwa ya mutu da hakiya, ni nan ba yadda ban yi da ita ba akan ta kai ta asibiti tun yana apolon sa, sai da ta ga ‘yar ta gama makancewa sannan ta kaita, a lokacin aka ce ido ya mutu, yadda suka je haka suka dawo.

    Matar na nunawa Sarham hanya har suka isa wani dan mitsitsin gida a wata unguwa can ciki, kamar duk rabin unguwar kwatami ne, kasancewar unguwa ce ta masu karamin karfi sosai. Amma gidan nata sai suka same shi a kulle.

    Sarham kamar ya dora hannu aka yayi kuka, don matuka ya saka ran sa da ganin Innar Hauwa da Hauwa a yau ba sai gobe ba, koma musu yayi kamar sabon kamun hauka, don cewa yayi da matar ba inda zai bari ta je sai ta hada shi da Innar Hauwa, ta ce itafa bata san gidan mai maganin da aka kaita ba, sai yace to su kai shi gun makwabcin nata da ya kai ta Albasu ne koma ina ne, in ba haka ba itada makwabcin na Inna zai yi karar su ga hukuma kan cewa sun batar da bayin Allah.

     “Yau nake ganin abun da ya gagari Kakata” in ji Tafada mai Tuwo, daga abun arziki zaka daura min jakar tsaba kaji su bi ni, ni fa tsakanina da Innar Hauwa mutunci ne kawai, Allah ya gani ko a kwanciyar nan da tayi sau biyu ina taya Hauwa kinkimar ta ta kai ta asibitin Kuroda amma bata yarda ta kwana, yadda kake tunanin mu muka batar da su, to akan me? Daga zaman amana???”

    Malam Isa ya lallashi Tafada yace, “kada ki damu ba kya ganin a fusace yake? Ina ne gidan makwabcin nasu?” Ta nuna gidan dake jikin na Innar.

    Aka yiwa makwabcin su Inna sallama ta hanyar tura yaro cikin gidan sai gashi ya fito, suka gaggaisa da Malam Isa yace “Tafada ya akayi? Tace ga masu neman makociyarka nan, har suna neman kala mana sharri wai mun batar da ita”. Malam Sani Albasu yayi dariya yace, “Innar Hauwa mai jama’a, ho! Tana can kauyen mu gidan Malam Bagobiri mai maganin gargajiya na Albasu, in kuka je Albasu duk wanda kuka tambaya gidan Malam Bagobiri ya sani, ko daga tashar Albasu ne kukayi tambaya za’a kai ku har gidan sa”.

     Sarham yace “me zai hana ka daure ka rakamu kawai, ina ganin zaifi sauki, tunda kai ka kai ta? 

    Malam Sanin ya yarda zai rakasu har Albasu, Amma yace saidai su dawo gobe yanzu yamma tayi.

    Sarham, Wanda hakurin sa ya tuke a lokacin sai yace da Malam Isa su je kawai su yi tambayar har su samu gidan. Malam Isa ya yarda don yaga damuwar sa karara, ya yarda cewa wannan bawan Allah Sarham, da gaske ya damu da Innar Hauwa Allah kadai ya san tsakanin su. 

    Musamman filin gidan su da ya saye dinnan ya hau ginewa, duk da bai yi masa wani bayani ba ya fahimci yana da niyyar sake mayar musu da gidan su ne. Wanda baya ko tantama kulafucin ta da gidan, da unguwar bakidaya, da mutanen ta na arziki da aka raba ta dasu rana daya, sannan da makancewar tilon diyar ta rana daya, da kuma damuwar batan mijin ta Malam Bilyaminu dare daya, su suka taru suka haifar mata da kamuwa da ciwon zuciyar da ake cewa tana fama da shi a yanzu.

     Malam Isa ya tuna Innar Hauwa yanzu mijin ta ya fi Shekara biyar da bata, me zai hana ta yarda tayi GAIBA in ya so shi ya aure ta ya rike mata 'yar ta guda daya ya killace su a gidan sa su daina rayuwar sayarda abinci a Tasha?

      Shi kadai yake wannan tunanin na babu gaira babu dalili har suka isa Albasu.

Malam Isa ya tafi tunani bai san har sun shiga garin Albasu ba, sai da Sarham yayi masa magana yace “gamu cikin Albasu” suka tsayar da motar a gefen titi Malam Isa ya tambayi wani mai Amalanke ko ina ne gidan Malam Bagobiri mai maganin gargajiya?”

     Mai Amalanke yace “kun baro gida can farkon shigowa gari, ku koma da baya ku tambaya” Sarham yace “in dai ka san gidan shigo ka kai mu, zan baka kudin Babur ka dawo”.

       Hakan kuwa aka yi, mai amalanke ya shiga bayan motar yana nuna musu hanya har kofar gidan malamin.

Wato abun babu kyawun gani, Yaa Subhanallah! Marassa lafiya ne rututu a zube a kasa tun daga zaure, cutututuka iri daban daban masu tasa tsigar jiki. Sarham sai da ya dauke numfashin sa na lokaci mai tsaho sabida kazantar gidan da cunkoson marassa lafiya. Tausayi da haushin Inna ya kama shi, wato har yanzu tana nan da halin ta na rashin yarda da asibiti kamar bai isa ace ta dau darasi tun akan Hauwa ba?

    Ganin cewa jinin sa na neman hawa, sai ya umarci Malam Isa ya yi musu sallama da malamin, aka ce ai sai sun hau dogon layin ganin sa yanzu kuma dare yayi, saidai su dawo gobe da safe.

Malam Isa yace da Tafada “shiga kawai ki fito mana dasu, ya gansu hankalinsa ya kwanta, don ni kam ban iya kwana garin nan”.

Tafada ta shiga gidan da sallama, wani ikon Allah da Hauwa ta fara tozali, wadda ke bakin kofar dakin da Inna ke kwance, Hauwan kuma nan da nan ta dauki muryar ta, ta kira sunan ta da ‘yar dusassar murya.

     “Tafada, kamar muryar Tafada nake ji”.

     Tafada ta isa ga Hauwa da sauri, wadda tayi kozai kozai tayi zuru-zuru, rabon ta da wanka yau kwana bakwai, wato tun kawo su da Malam Sani yayi kauyen nan ya tafi, ya kuma karbe duk ‘yan kudaden hannun su da sunan yana biyan mai magani, amma kullum jiya I yau, babu wani sauki a tare da Inna sai na Allah. Yau kam wuni tayi tana suma babu wanda ya tsaya a kanta sai Hauwar da ba gani take ba, itama an gaya mata dai uwarta na suma.

     Don haka yau Hauwa ta wuni kuka wurjanjan har ta gode Allah, idan ta rasa Inna, bata san yaya zata cigaba da rayuwa ba.  

Tafada ta gaisa da mutanen data gani a zazzaune kafin ta kama Hauwa ta ce “nice Tafada, ina Innar taki wani ke ta son ganin ta tun daga Kano ya sako mu a gaba saida muka kawo shi nan, kamar dai dan uwanku ne”. Babu wanda ya zo wa Hauwa a rai da zai biyo bayan su har nan, cikin ‘yan uwan su duka sai Yaya Jamilu! Watakila yayi ta tambaya ne a kansu har ya gano inda suke.

Tafada tayi mata jagora suka fito, a yadda Hauwa ta lalace ba don yayi mata farin sani ba da bazai gane ita ce ba, sabida yadda tayi baki ta kuma rame, Sarham ya runtse idon sa cikin tausayi marar misali, muryarsa na shakewa da sarkewa yace.

     “MAI-JID-DAH!”.

     Sai tayi sak! Da rai da kwakwalwarta cikin son tuno inda ta san sassanyar muryar, da kuma inda ta taba jin an kira ta da wannan kebantaccen sunan. Duk fadin duniya mutum daya ne ya taba kiran ta da “Maijiddah”, ya kuma ce sunan nashi ne shi kadai, bai yarda kowa ya kwaikwaya ya kira ta da shi ba wato LIKITA SARHAM!!!

    Hauwa-Kulu ta yi shiru na wucin gadi, kwakwalwarta na faman processing tattausar muryar data kira sunanta. Muryar Likita Sarham ce tabbas, wadda ko mutuwa tayi ta dawo bazata manta ‘accent’ dinta ba. Wani kwayan mutum guda daya da komai nisan shekaru bazata taba mantawa da shi ba, saboda kyakkyawar rawar da ya taka cikin rayuwar ta da gudunmuwar da ya basu, a lokacin da rayuwarta gabadaya ta dauko nakashewa. Duk da a cewar Hauwa, shi Sarham din shi ya karasa mata idanu, wato shi ya karasa makantata, amma bayan faruwar hakan ya kyautatawa rayuwar su, ya kuma taimaka ya hana rayuwar ta karasa rugujewa, ya karfafa mata da cewa kada ta bari ta durkushe a dalilin makanta.

Rawar da Dr. Sarham Abbas Shanono ya taka cikin rayuwar su, duk da cewa ta dan lokaci ce, to fa hakika mai girma da muhimmanci ce domin ya nuna musu kauna da mutunci na masu ilmi. Da wuya ka samu mutum irin sa a wannan zamanin da yake yiwa talakawa da yafi matsayi da ajin rayuwa kamar su daukar mutane. Balle don wani tsautsayi ya faru a dalilin aikinsu su tsaya su yi waiwaye a kai. Ta tabbata da ace bai tafi inda ya tafi ba, da ba’a kawo wannan matakin ba a lafiyar Inna, da karatun ta, da komai ma na rayuwar su, ta tabbata zai cigaba ne da tsayawa rayuwar su kamar Baba da Zulkiflu na raye. Da bazai bari Zakari ya tozarta rayuwar su ba ya raba su da farin cikin su.

     Bata yi masa farin sani ba, saboda ko sanda yake tare da su kullace take da shi, bata tsaya ta saki jiki dashi ba, balle ta saba da shi, ko tayi masa kyakkyawan sani, amma ko daga sanin nesa nesa din data yi masa a gidan su ta shaida cewa shi din mutumin kirki ne, mai taimako ne, mai yawan alkhairi ne, ya san (human dignity), kuma yana matukar kaunar su sosai. 

    Sai hawaye ya soma zubo mata, don ji tayi ma kamar BABANTA MALAM BILYAMINU YA DAWO! Tamkar wani ‘SAVIOUR’ (mai ceto) ya iso cikin rayuwar su, koko tace kamar wani Mala’ikan rahma ya riske su, a lokacin da Inna ke kan gargarar mutuwa cikin rashin gata, kuma a lokacin data fidda rai da tashin Inna.

A can cikin kunne da kwakwalwarta, Hauwa ta tsinkayi muryar nan ta Dr. Sarham mai sanyi da gardi tana tsokanarta, zolaya irin wadda baya rabo da ita, kuma ya saba yi mata don ya samu ta kula shi. Aka ce a bar hali a ci me? Dr. Sarham har yanzu yana nan da (jovial personality) din sa. Hausawa suka ce in ka shekara baka ga mutum ba, ranar da kuka hadu, tambaye shi wani abun daban amma banda halin sa. 

    Wato a nufin bahaushe halin mutum baya taba canzawa sai dai ko mu ce Sarham ya rage wasu daga cikin halayen sa na sakin fuska, da yawan magana, a dalilin girma da nauyin iyali da yanzu ya hau kan sa.

     “A yi magana ki ce an yi miki “GORIN IDO”, dubi kwala-kwalan idanun nata a jike jagab, jawur dasu, kamar kosan da ya soyu a cikin mai don kuka, maimakon ta saki far’a tace “Jabbama-jabbama…lale-maraba da bakon KANO. Ko tace YAYA SARHAM SANNU DA ZUWA”.

     A’ah ta tsaya tana mana ambaliyar hawaye, watakila anan garin nasu na Albasu, da haka ake saukar bako”. 

    Sarham ya fada cikin zolayar Hauwa-Kulu, don rabata da hawayen dake ta satatar mata, da kokarin sa na hadiye nasa hawayen. Ba kankanin abu ke sa shi kuka ba, amma a yau ya san in bai yi da gaske ba ‘he cannot control his tears’ a gaban Hauwa, abinda bazai so hakan ba ko kadan. Kokarin gaske yayi da ya iya hadiye hawayen sa a kan idon Hauwa, wadda yake ma kallon kanwa ta jini, kamar Sumayyah, yadda ba zai iya bari Sumayyah ta ga raunin sa ba, haka ba zai bari Hauwa ta gani ba, ba don haka ba da tuni ya sake su sun shatato shima akan kundukukinsa, kamar yadda Hauwan ke faman yin nata, amma fa ita nata na farin ciki ne.

     Ganin yanayin wahala da rashin lafiya da ya same su ciki kuma a kauye ya karya zuciyar sa, wanda ba cikin sa ya tafi ya barsu ba. 

Cikin muryar kuka Hauwa ta ja sheshsheka ta ce “Likita sannu da zuwa”, tana mai yi ma saitin da muryarsa ke fitowa kallon ga ZULKIFLU YA DAWO.

    Sarham ya matso gaban ta har tana iya shako kamshin hamshakin turaren sa na ‘Oud Abyad’ ya ce “to ko ke fa Maijiddah! Amma kawai daga ganin mutane sai ki balle da bokitin hawaye? Ai sai su Malam Isa da Tafada su dauka baki yi maraba da zuwa na ba sam”.

Tayi murmmushi, har kuncinta ya lotsa ciki sosai, wani abu da ke kara ma Hauwa’u kyau, yace “maza je ki kwaso kayan ku, Inna Tafada taimaka min ki dauko Inna don Allah a sa min ita a bayan mota, in yi maza in kaita asibiti, a kula min da ita da kyau”. A yau yana dakacen inama shi ba likitan ido bane, na zuciya ne! So that ya iya duba Innarsa da kansa”.

Hawayen dadi ya sake kecewa Hauwa, don ita ai tayi-tayi Inna ta yarda ta zauna a asibitin Murtala a cigaba da dubata ta ki, tace in mutuwa ce ta isko ta, a barta ta mutu a cikin dakin ta yafi mata, ta fi so ta mutu a gida akan gadon asibiti, kada taje a kai gawarta mutuware a ajiye a firinji, a kuma jinkirta yi mata janaza. 

    Kuma ita har gobe bata yarda da maganin asibiti ba, don bata ga ranar da ya yiwa idanun Kulu ba, aikin Kulu yasa ta kara nesanta kanta da asibiti, dama dole ce ta kaita a kan Hauwa dinma, shi yasa tunda ta fara ciwon nan suke dambarwa ita da Hauwa akan zuwa asibiti, daga bisani Hauwa ta dauko shatar mota tace mata zasu je asibitin Kuroda a bata magani kadai su dawo, da suka je asibitin, kallo daya likita yayi mata yace kwanciya zasu bata.

    Hauwa bata ankara ba sai ji tayi Inna ta tashi tsaye tace ta tashi su tafi, data tsaya yi mata magiya da gardama kan ta tsaya sai Inna ta kamo hanya abinta, ta kyale Hauwa a tebirin likita, dole Hauwa ta taso ta biyo bayan ta tana kira. Tausayi yasa ta dakata ta kama hannun ta, a lokacin suka taho gida.

    Hauwa bata daddara ba, washegari tayi ta rokon ta kan su je asibitin Murtala, ta tabbatar mata su bazasu kwantar da ita ba, da kyar da nacin kukan Hauwa Inna ta yarda suka je Murtala, nan suka hau layi har suka samu ganin likita, anan ne likita ya yiwa Hauwa bayanin dole Inna ta kwanta ayi mata aiki a zuciya, domin ta samu rami (hole) a zuciyarta. Ai jin haka Inna ta mike ta fice ta bar Hauwa da likita suna kiranta (again), Hauwa ta biyo bayan ta tana kuka da roko, sai Inna ta dakata da tafiya tace da Hauwa.

    “Idan kin manta haka aka ce min za’ayi miki aikin ido ki warke daga hakiya, amma kin warke din? 

    To ni yanzu in aka yanka min zuciya kina da tabbacin zan mike?

     Ba tsoron mutuwa na ke ba domin kuwa a shekaru hamsin me nake jira banda neman hanyar dacewa da cikawa da Imani? 

    Ke nake ji Hauwa-Kulu, in babu ni, rayuwar ki zata shiga wani hali na garari da walagigi har da da bara akan titi, don baki da mataimaki da mai yi miki jagora bata idanu kadai ba harma da rayuwar ki gabadaya, sai Allah da ya halicce ki”.

    Abinda Inna bata sani ba, ko babu ita Innar, ita HAUWA-KULU (modern makauniya ce), bata bukatar dan jagora don zuwa wani waje, kanta tsaye take zuwa ko’ina, iyakaci kai in ka fahimci bata gani kai ka kauce mata, wata irin brainlliant ce mai kaifin kwakwalwa da kaifin basira, gata da ji mai karfi irin na wadanda suka rasa idanun su da kuruciyar su Allah ya bata. Don dai UWA-UWA ce amfaninta yafi ga haka, wato ya wuce ta rayu don ta yi mata dan jagora, sai dai don ta zama GARKUWAR ta a rayuwa bakidaya kuma cikon farin-cikinta ta.

    Tun daga ranar bata kara yarda Hauwa ta ja ta asibiti ba, tayi ta kwanciya a gida suna cinye dan jarin nasu a sayen abinci kullum, tunda ba juyawa ake ba yanzu kashewa ake yi yasa kullum daurin kudin su sai kasa yake yi, kafin makwabcinta Malam Sani mai irin ra’ayin ta kan traditional medicine ya ce da gaskiyar ta, tazo ya kaita gidan mai magani inda zata samu magani na kowacce cuta ba tareda an tsaga kirjin ta ba.

Aka fito da Inna daga cikin gidan ranga-ranga da daurin kayan su a bakko, aka sa a bayan motar Sarham, Tafada da Hauwa suka shiga, suka sa Innar a tsakiyar su, wadda bata san ma ko su waye a kan ta ba lokacin. Rabin jikin ta na kwance jikin Hauwa. Malam Isa na gidan gaba Sarham ya ja motar cikin nutsuwa da hanzari suka hau titin da zai maida su cikin birnin Kano.

Suna tafe a hanya suka fahimci Inna ta farfado daga suman data yi, suka yi ta yi mata sannu da jiki. Malam Isa nata yiwa Inna fada da dacin rai, na yadda ta shiga duniya ta bar makwabtan ta masu kaunar ta, wai ace yanzu ta gwammace rayuwar sayar da abinci a tasha a kan zaman gidan sa, yace to yanzu me kika tsinto a tashar duk sana’ar taki ban ga kinyi arziki ba, ban ga kinyi kiba ba, na gan ki tsiya-tsiya rakace-rakace wutsiya a zage cikin ciwo. 

    Rayuwa bata raggo bace. Haka azzaluman mutane ba’a kyale su su cigaba da aikata zalinci son ransu ga marassa karfi a doron kasa musamman mata da kananan yara kamar Kulu. 

    Da kin zauna mun tashi tsaye mun hada karfi da karfe mun kwato miki hakkin ki, yadda makwabtanki suka fusata a lokacin da kin tsaya, in yafi karfin ki ai bai fi karfin shari’ah da Alkali ba, cewa fa mukayi ki tsaya zuwa wayewar gari mu shigar da kararsa maimakon mu dau Shari’ah a hannunmu.

Kuma ni da kin zauna kin yi gaiba, na rufa miki asiri na killace ki a gidana karkashin inuwar aure in taya ki kula da ‘yar makauniyar ‘yar ki, amma ina! Ke ga ki kububuwa sarkin masu zuciyar duniya, kika dauki ‘ya ba ido kika bar BADALA!” 

Sarham ya rage gudun motar sa a dokar daji, a fusace yace “wallahi Malam Isa in baka yi mata shiru ba zan cillar da kai a dajin nan in ja mota ta, da me kake so ta ji? Da ciwon jikin ta ko da hayaniyar ka?” 

Daga haka aka samu Malam Isa yayi shiru, bai kara magana ba har suka isa asibitin Malam Aminu kano.

Tun kafin su iso dama Sarham yayi waya da Dr. Babangida, wani babban likitan zuciya ne (cardiologist) abokin karatun sa a Jiddah da ya dawo yake aiki a nan AKTH, shi yasa aka karbi Inna cikin kulawa daga shigar su asibitin, aka yi imajensi da ita. Kuma da taimakon sanayyar sa da Dr. Babangida yasa ta samu attention din likitoci da yawa suka rufu akan ta, don binciken hakikanin abinda ke damunta.

Sai da suka kwana suka wuni a A&E ana bata taimakon gaggawa kafin a basu daki a kwantar da Inna, amma da Sarham ya zo asibitin a washegari sai yace a maidata dakin ‘Amenity’ ya kuma biya komai aka maida Hauwa da Inna kebantaccen daki wato ‘Amenity’ a sashen mata.

A kwana uku sakamakon gwaje-gwajen da likitoci suka yi wa Inna ya fito, da gaske tana da huda a zuciyar ta, wadda ke bukatar sai an yi mata aiki an cike ramin da zuciyar tayi. Madinah na can gidan kakannin ta tana jego, Sarham na jelen asibiti dasu Inna daga nasu gidan yake zuwa shi yasa bata san me yake ciki ba, sai dai duk sanda ta kira shi a waya zai ce mata yana asibitin Aminu Kano yana da ‘patient’ yana ‘busy’, ta kuma san shi sosai da Dr. Babangida shiyasa ta daga masa kafa, yau kwana uku bai zo Soron dinki ba balle ya ga Baby Hauwa da take kira (Waheedah) tun ranar sunanta.

Kowa ya dauka saboda Haj. Kulu Sarham ya sakawa ‘yar sa suna Hauwa, shi kuwa zai iya rantsuwa ya saka sunan ne don ya dinga tunawa da Inna da Hauwa a lokacin da ya neme su ya rasa. 

Hatta a gida sun gane yana zirga zirga, kuma ba a wajen masu jegon ba, ko jiya ya saka Surayyah girki na hanta da koda da ‘vegetables’ da kunun gyada yace ta zuba masa madarar ruwa a ciki, Surayyah ta dauka shi zai ci, bayan ta gama ta gaya masa ta gama, sai yace ta shirya a basket ta kai masa mota, Mama ta bi Surayyah daki bayan fitar sa tana tambayarta ko wa Sarham zai kaiwa abinci? Surayya tace bata sani ba, yace dai yana da mara lafiya a asibiti ne.

     Mama tayi wani dan tunani sai ta ce “in kika bibiya bazai wuce mutanen sa na Badala ya gano ba. sune kadai zai dauka da muhimmanci irin haka ya kasa nutsuwa in suna cikin matsala”.

    Surayyah ta ce cikin mamaki “ba sun bar Kano ba? Ba sun bace masa ba tuntuni?” Mama tayi dariya tace “ko a ina suke in dai a fadin Najeriya ne na tabbatar miki sai Sarham ya nemo su, ki bar Sarham akan abinda yasa kan sa, ko yake kuma kauna da son taimakawa da zuciya daya”. 

Surayyah ta kwana abun yana bata mata rai, na yadda ta zage ta shirya masa abincin nan da kyau, don ita bata son zancen su ma, yadda aka sakata girkin wahalar wasu kauyawa wai su su Innar Hauwa, tarkacen BADALA, don haka washegari da ya saka ta girkin again tayi maza ta ce kanta na ciwo bazata iya ba, dole sai Nancy sabuwar mai aikin Mama ya saka tayi masa ‘potatoe porridge’ da yaji ganyen alayyahu. Da dafaffen kwai.

    Ita Hauwan ma da ake kaiwa garar abincin mai dan gina jiki, don a samu ta murmure ta tada komada daga muguwar ramar data yi da mokadewar da kashin wuyan ta yayi a Albasu, sam bata iya ci, bakin ta ya kasa karbar dandanon abincin don bata saba da cin mai lafiya da dadin dandano irin sa ba.

    Ruwan bunu (lipton) ko na Milo kawai take iya zubawa a cikin ta ya zauna da dadin rai, ta zama kamar ka bushe ta ta fadi don kamar ma bata da lafiya, nan kuwa yunwa ce kawai ta zaman Albasu ta zauna a jikinta tayi mata illah. Abu daya ke faranta mata in ta tuna Inna na bisa karkashin kyakkyawar kulawar asibiti yanzu, kuma ana tabbatar mata da tana jin sauki kasancewar idonta a rufe yake kuma kullum ana mata karin ruwa kafin ranar da za’a yi mata aiki tazo.

Sarham ya biya komai ranar aikin, ya kuma saka hannu aka yiwa Inna aikin zuciya. Aka yi lafiya cikin nasara ba kamar yadda Inna ke tsoro ba.

     A lokacin ne ya samu ya koma cikin hayyacin sa tun daga ranar da ya dauko su Inna sai yau ya samu nutsuwa, bayan an gama aikin an kai ta dakin hutu, inda Hauwa ta cigaba da jiran farfadowar ta.

     Sai ranar ya samu ya leka su Baby Hauwa. Madinah bata iya fushi da Sarham ba, ko me yayi mata kuwa, komai girman laifin, amma yau a kwayar idonta ya gane tayi fushin, musamman da yaga tana ‘avoiding eye contact’ da shi, ya san tayi fushi mai ban mamaki ko bata furta ba.

Ya sa hannu ya dauki Hauwa cikin dan kyakkyawan gadon ta tana barci, ya zauna dab da Madinah yace “Likita matar Likita barka da yau, ya kuka kwana? Ya kukan daren uwar bil’adama?” Madina ta amsa fuska ba yabo ba fallasa, sai yace “ba sai an gaya min ba, na san nayi laifi wa GIWAR SARHAM, kuma na karbe shi tun ba’a bani ba (laifin), tun kwanaki uku baya ma fa ya kamata ace na koma Jeddah, amma inada uzurin da ya rike ni mai muhimmanci, kiyi hakuri kin ji Madindin din Sarham! Madinatul-Munawwarah my shelter, my eternal happiness, my home peace, my safety and my security, in sha Allahu nama fasa komawa, sai kin gama wankan jegon ki sai mu koma tare, zan yi amfani da lokacin (as annual leave) dina”.

Amma har ga Allah ya fasa komawa ne saboda lafiyar Inna, yana kuma son daukan ‘measures’ din da ya dace akan rayuwar su Inna kafin ya koma Jeddah. 

Madinah da bata iya dogon fushi da Sarham ba jimawa ta yarda da uzurin sa ta kuma saki rai suka shiga hirar arziki da hirar soyayyar su da bata kodewa, suna yi suna kallon kyakkyawar fuskar ‘yar su Hauwa (Waheedah) wadda suka saka a tsakiyar su tana barci da sauke numfashi cikin koshin lafiya. 

    A lokacin Madinah da Sarham suka hau musu akan wanda Hauwa tafi kama dashi, shi yace da shi take kama completely, ita tace kalar su da gashin su ne kawai iri daya amma fuskar da yatsun, duk nata ne.

Madinah a idon sa kadai ta fahimci ya jima bai ci abinci ba, amma da yake a dabi’ar shi baya dorawa matar sa nauyin ta tashi tayi masa girki a duk sanda yake so, sai bai mata complain ba, ita da kanta da yake ta san kan kayanta, ta gane sosai yake cikin gajiya da yunwa, don tun haduwar sa dasu Inna bai samu nutsuwar cin kyakkyawan abinci ba sam, don haka ta tashi ta hado masa abinci mai rai da motsi, sai da yaci ya koshi suka gaisa da Kakarta Haj. Lailah, wadda ke falo, sannan yayi musu sallama ya wuce asibiti don ya tadda su Hauwa ya ga farfadowar Inna, don haka daga nan Soron dinki can ya nufa.

Saida ya tsaya a hanya ya yi musu sayayya sosai kamar yadda ya saba duk da ya lura Hauwa bata iya ci, yau sai ya saya mata fresh milk da yawa (unsweetened) kafin ya wuce aibitin.  Da sallama ya murda kofar ya shiga dakin, bayan Inna tayi masa iznin shigowa, amma Hauwa a ciki ta amsa masa kamar yadda ta saba amsa sallamarsa tun fil azal, ya tadda su tare da Malam Isa ya zo dubata shi da dan gidan Inna wato Saleleh.

Malam Isa har gidan su Salele ya je ya gaya musu an ga Innar Hauwa, shine fa Salele ya biyo shi. Inna ta dubi Sarham tana daga zaune jikin filo. Ba don ba karamin sani tayi masa ba da bata gane shi ba, don ya canza gabadaya daga yadda ta san shi, dan siririn saurayin likitan nan na Murtala, ya girma ya kara cika ido cikin shekaru kalilan, ilmi da kwarjinin addini sun kara bayyanar da cikar zatin sa. Tayi murmushi a hankali, ta ce.

     “Inda rai da rabo, likita Sarhamu! Ashe Allah yayi zamu gana?”

     Sarham ya ja kujera a gaban ta ya zauna, yana kallon Hauwa tana shafa hoda irin mai like da mudubinnan a jikinta, saura kadan ya fashe da dariya, kasa amsawa Inna maganar data yi yayi saboda dariya dake cinsa, ya nuna wa Inna ita da baki, itama tayi dariya, tace “kuma ayi magana cibi ya zama kari ba!”.

     Malam Isa ya juyo garesu yace “dariyar me kuke haka?” Inna tace “kai dai abar kaza cikin gashin ta, daga jiya zuwa yau na kirga shiga wankan ta ya kai goma! Wai biyan bashin wankan kwana bakwai da bata yi ba a kauyen Albasu take yi yanzu, tunda ta samu ruwan dumi da sabulu mai kamshi ai shikenan, har da yi wa Malam Sani Allah ya isa da yayi mata sanadin komawa zaman kauye”. Sarham yayi dariyarsa mai isarsa, har da sunkuyawa da rike ciki, sai lokacin Hauwa ta gane da ita suke. 

    Ta dan dakata da shafa hodar, duk ta sha jinin jikinta, ga mudubin a hannun ta, kai sai ka rantse tana ganin fuskar ta cikin mudubin, jin sun kara ninka dariyar ta ji haushi, ta mike ta fita daga dakin sai Sarham ya mike ya bi bayan ta don ya bata hakuri.

A jikin barandar dakunan ya same ta a tsaye fuskar ta ta hade kamar kunun kanwa. Tana tsaye kawai harde da hannuwa a kirji. Ya lallaba ya tsaya dab da ita shima ya harde nasa hannuwan a kirji irin yadda ta yi. Ya ce.

     “Kuluwa, ni fa ba ke nake yiwa dariya ba, labarin da Inna ta ke bayarwa ne ya bani dariya”. Hauwa tayi narai-narai da idanu kiris ya rage ta fashe da kuka, tace “idan makanta abin dariya ce ai bata wuce kan kowa ba, idan gorin ido abun yi ne, ba komai ku cigaba da yi min”. Sarham ya kama baki cikin jin wani iri a ransa yace “kina nan a Kulun ki, Kululu, Kulun Majadun sarka mai rikicin gangan, har gobe baki canza ba, dama Inna ta ce ayi magana cibi ya zama kari. Yanzu saboda Allah ba dama muyi dariya sai ki ce rashin idon ki ake wa gori?

     Idanun nan fa mun fi ki son su dawo, ta yaya zamu yi murna da halin larurar da suke ciki? Kawai dai kina ji da rikicinki ne na gangan.

     Kullum addu’ar mu shine su dawo da gani kamar na kowa, idan masu dawowa ne, idan kuma ba masu dawowa bane Allah ya sa rashin su ya zama silar kaffara a gare ki da iyayen ki, ya baki aljannar Firdausi a madadinsu”.

Hauwa ta dan saki rai, sai Sarham yace, “Maijiddah, tunda muka hadu bamu gaisa ba, bamu zanta ba, bamu yi fadan namu ba, koda yake yau mun dan taba. Anyway, nayi kewar ki MAIJIDDAH, bayan a baya na zaci bazan taba yin kewar ki ba, tunda baki damu da ni ba”.

Hauwa ta yi murmushi ta ce a ranta,

    “kwarai kuwa, don ni dai kam in ba na dauko littafin makaranta ba, sam-sam bana tuno ka, gara-garama a lokutan da kalamanka masu haska min rayuwa ke sawa in tunaka”. 

    Unfortunately, bata san cewa a fili ta fada ba. 

    Sai ji tayi Sarham yace cikin rashin jin dadi da sosuwar rai, “I know, ba tun yau ba na sani ai, Inna ce kawata, uwata, kuma ita ta damu dani. Ni din a wurinki ba kowa bane face…”. 

    Yayi shiru cikin tsananin damuwa da rashin sanin ta yaya zai yi ya kankare wannan tunanin daga zuciyar Hauwa-Kulu? Wanda ba tun yanzu ba ya lura yayi mugun samun muhalli a cikin ranta? 

    Hauwa tace “kaima da ita kadai ka damu (Innar), daga zuwan ka ai ko la’akari da halin dana ke ciki baka yi ba ka fara tsokanata a kauyen Albasu, wai idona kamar ana soya kosai cikin mai, baka san cewa kukan farin cikin ganin ka nake yi ba, baka san halin dana ke ciki ba a lokacin, don ji nayi kamar Yayana Zulkifilu ya dawo, kamar farin-cikin rayuwa gabadaya ya dawomin, duhun zuciya ya gushemin, haske ya dawo a cikinta”.

    Da mamaki da jin dadi a muryarsa Sarham yace “to kiyi hakuri Maijidda, mu ajiye wannan a gefe, I’m happy to be your sourse of happiness, koda wannan kadai yau kin karramani, yanzu inaso ki bani labarin bayan rabo, da rayuwar ku gabadaya daga farkon tafiyata har ranar zuwan ku Albasu gidan mai magani”.

     Hauwa ta nisa, kafin tace “dogon labari ne likita, amma mun sha wahala wajen neman na kan mu a tashoshin mota, mun yi girki iri-iri ba hutu tamkar injin girke-girke a kowacce rana daga safe har yamma hakarkarinmu bai hutawa, ba don komi ba sai domin kada mu yi bara. Allah ya sani, ba abinda nake gudu da nakasata irin bara! Alhamdulillah for being alive, and for everything, musamman karatuna na sakandire, wanda (against all odds) sai da Allah yasa na kammala shi.

    A kullum inna sare da karatun, saboda wahalar zirga-zirga ta rashin idanu, kalaman ka nake tunawa suke zame min ‘inspiration’, kuma madubin dubawata a rayuwar lalurar dana tsinci kaina.

    Kalaman ka likita sunyi tasiri sosai wajen karafafani domin ina matukar jin dadin su a lokutan da na bukacesu, cewa da ka yi “akwai iyawa cikin nakasa”, kuma ka ce min “ba nakasashshe sai kasashshe”. Wadannan jimlolin naka guda biyu su suka zame min food for thought; su suka sa na dage na jure da zuwa makaranta ba ido. ‘Obstacles’ da ‘hindrances’ da ke cikin lalurar makanta duka basu sa na bari ya salwanta ba.

    Babu wani abin karaswa cikin labarin namu a bayan tafiyar ka, sai na bacin rai da wahala na zallan zalunci wanda kanin mahaifina ya sanya mu a ciki, a dalilin kwace gidan mu ya rusa shi. Ni ban sani ba ashe tun lokacin batan Baba, Inna ta fara ciwon zuciya, don likitan dazu ya tabbatar min ramin ya dade a zuciyar ta yayi akalla shekaru biyar, tana dai yin cuwuka a tsaitsaye tana kuma kula da shan magungunan gargajiya dake kara mata ‘immunity’, shiyasa bai ci karfin ta da wuri ba, bamu ankara ba sai da ya kayar da ita kasa warwas.

    Likita rayuwar da muka yi gabadaya kaji-ka ji….” ta zayyano masa daga farko har karshe har labarin bugeta da Yaya Jamilu yayi da mota ya kuma dage daga baya zai aure ta, wanda duk shi ya janyo musu komai.

    “Yanzu ina Jamilun? Me zai aura a wannan kankanuwar yarinyar? Bana jin lokacin ko SS2 kin gama, haba! This is sheer abuse. To ya san abinda Baban nasa yayi muku?”

     Sarham ya tambayi Hauwa, (furious in anger), ji yake idon sa idon Jamilu da Babansa Zakari sai ya shake su. Hauwa ta ce.

     “Yaya Jamilu ban kara haduwa da shi ba, bamu kara jin duriyar sa ba tun tafiyar sa Delta, kuma bana jin ya san abinda Baba Zakari ya yi wa gidan mu, saboda a lokacin yayi tafiya, ban dai sani ba ko idan ya dawo daga tafiyar da yayi wani ya bashi labari”.

     Sarham ya dade kan sa a sunkuye, yana tunanin ta wace hanya zai gayawa Hauwa ya sake gine musu gidan su, da gini irin na zamani? Jira yake a sallami Inna daga asibiti ya dauke su ya maida su gidan su na asali, ya kuma yi karar Baba Zakari kan abinda yayi, ko ba’a yi masa komai ba hukuma ta shiga tsakanin sa da su”.

    Sun dade a wajen suna labari shi da Hauwa, irin yadda bai taba jin tayi magana mai tsayin ta yau ba, sai da mamakin sa ya kasa boyuwa yace.

    “Maijiddah, ashe dama kina magana haka? Da ni ne ba kya yi? To meyasa Maijidda? Me nayi miki haka da zafi?”

     Ya tsareta da ido cikin tuhumar dalili, kai kace kamar tana ganin sa, Hauwa ta rufe ido cikin jin kunya, ta ce “ai don na dade ban ganka bane, daga yau zan rufe bakin ya koma kamar da” Sarham ya lumshe ido kamar tana ganin sa, idonsa a kan zara-zaran ‘yan yatsunta ya ce “a’ah ban yarda ba, a bude shi muyi ta shan hira abinmu, irin ta Yaya da kanwar sa da sukayi kewar juna, kin san ni mai baki ne, mai yawan hira ne, shiyasa tamu ta zo daya nida Inna. Maijiddah ina so in zama babban Yayanki daga yau, wanda kafin kowa ya ji damuwar ki nine mutum na farko da zan ji.  

    Zan bar miki waya don mu dinga magana don zan koma wajen aikina babu jimawa, na rako matata wankan jego ne, amma mun koma Jeddah da aiki tun da jimawa”. 

    Hauwa ta fiddo manyan idanun ta cikin mamaki ta ce “likita dama kana da mata?” Ya yi murmushi ya ce “mamakin na menene haka? Amsarki a baya itace, a’ah, na dai aure ta babu jimawa, bayan na kammala karatun dana tafi yi a Jeddah, a can muka hadu, duk da dai ba haduwar mu ta farko kenan ba”. Hauwa tace itama likitar ido ce?” Dr. Sarham Yayi dariya yace “exactly! Amma ya akayi kika sani?”.

     Tace “na dade da sanin likitoci basa aure sai da liktoci ‘yan uwan su, watakila don kada a shafa musu cuta?” Sarham me zai yi ba dariya ba yace “wato shi likita bashi da cuta a jikinsa Maijidda?” Tace “da sauki dai” anan ma ta kara bashi dariya sosai, yace “ni kuwa da har na yi miki takwara, na dauka kema likitar zaki so zama?” Kafin Hauwa ta kara magana sai Malam Isa ya fito yana musu sallama zai wuce gida, tare da Salele.

     Salele yaga Sarham, nan da nan ya shaida shi, ya hau yage baki don bai manta shi ba da tarin alherin da ya dinga yi masa don ya dinga raka Hauwa Makaranta.

    Suka gaisa da Salele suka yi sallama da su suka wuce, shi da Hauwa suka koma wajen Inna. Hauwa na tambayar sa cikin mamaki.

     “Da gaske likita ka yi min takwara da ‘yar ka?” 

    Zancen a kan kunnen Inna, ta dago tana kallon shi da mamaki itama, tace.

     “Sarhamu kayi aure ne banida labari?”

    Sarham ya sunkuyar da kai yana dan murmushi yace “eh Inna, har an samu karuwar Hauwa’u, HAUWA-KULU!”. Ya dauko wayar sa daga aljihun sa ya nunawa Inna hoton Waheedah cikin pink shawul daya dauketa dazu. A takaice ya basu labarin yin auren sa da Dr. Madinah bayan ya kammala karatun da ya kai shi Jeddah, da irin neman da yayi musu kamar ya zautu bayan dawowar sa. 

    A ranar ya jima tare da su suna ta labarin rayuwar su a kurna, rijiyar lemo da kuma unguwa uku, da ta karatun Hauwa da aka samu kammalawa da kyar, da sudin ludayi, ta gaya masa Hauwa ta fiddo da kyakykyawan sakamako sosai, wanda ba kokarin kowa bane nasa ne, madallah da shi, madallah da haihuwar ’ya’ya irin sa, masu zamewa al’umma fitilar rayuwa kuma bango abin jingina, madallah da tarbiyyar iyaye irin nasa, madallah da shigowarsa cikin rayuwar su”. 

    Sarham (feeling overwhelmed with joy and happiness) saboda ya sha addu’a yau a bakin Inna, ‘yar sa Hauwa ma ta sha addu’a, tace yadda ya tsayawa Hauwa-Kulu wadda a yanzu za’a kira maariniya miskiniya ta samu ilmi daidai gwargwado duk da makantar ido, Allah ya tsayawa tashi Hauwar ko bayan ransa, yasa tayi ilmin da zata zamo mai amfani ga al’ummar duniya.

     Ita da kan ta Inna data nisa, taji yadda lafiya ta wadace ta, bata san sanda ta ce ta tuba tabi Allah ta bi asibiti ba! Daga yau ta daina kin asibiti tunda gashi ciwon shekara da shekaru ya tafi cikin sati biyu. Ta kara da cewa Sarham “ashe abin naku dace ne!”.

    Sai bayan kwana uku da yin haka aka sallami Inna, Sarham ya zo da mota ya dauke su zuwa gidan su na unguwa uku yace “Inna koda abinda zaku dauka a gidan ku dauka, ku fito ina jiran ku” Inna tace “ai nan ne gidan mu likita, yanzu anan muke zaune tun da jimawa” ya ce “na sani Inna, zaku raka ni unguwa ne bazamu jima ba, amma dai in har kin yarda da ni, to ki kwaso komai naku”.

    Inna ta hau kwasar kayan tana kaiwa boot din motar Sarham tana fadin “yarda da musulmi irin ka wajibi ne!”. Haka Hauwa ma, ta dauki kayan ta tsaf, suka kama hanya, Hauwa na gidan gaba Inna na baya. Sarham na tuki cikin nutsuwa da kwarewa, bai tsaya a ko’ina dasu ba, sai a kofar gidan su, gidansu na BADALAR Kofar Na’isa, dama sun riga sun shirya gidan dai dai gwargwado da taimakon Malam Isa da Salele. An zuba komai na amfani mai saukin kudi. 

    Inna tunda taga an doso kofar Na’isa ta soma hawayen tuna baya, kirjinta ya hau yin sama da kasa, ita ta dauka zai kaita ta gaisa dasu Maikosai ne.

    Amma sai ta ga anyi fakin a kofar wani sabon gida a bayan Badala, in har bata yi kuskure ba, kuma idan har ba idon ta ke mata gizo ba nan din lungun su ne kuma unguwar su, da ko daga makanta irin ta Hauwa ta warke itama zata gane su, tunda ga gidan Malam Isa nan ba abinda ya canza shi.

     Sai ta kalli Sarham a gigice, bayan ya kashe motar a kofar gidan. Sai a lokacin yayi musu bayani cewa gidan su ne ya karba musu.

    “Ka karba mana kamar yaya?” Inji Hauwa, (sounding extremely puzzled). Inna kuma tace “ko dai ka gina mana?”  Muryar Inna ta tambaye shi cikin kuka, don dai a kan idon ta taga lokacin da aka rushe gidan nasu wato gidan Malam Bilyaminu.

    Sarham yace “Allah ne ya nufa gidanki ya dawo gare ki Inna, ni kawai na taimaka ne, kuma kiyi hakuri zan yi wani shishshigi, a gaskiya zan yi karar kanin Baban Hauwa akan abinda yayi”. 

    Inna ta fara kukan farin ciki da dariya a tare, ta ce “Dan nan me zan ce maka? Wace irin addu’a ya kamata in yi maka? Na rasa kalma a bakina da zata gode min kai.

    Amma ka bar maganar Zakari, ni kam me zai sake hada hanyata da Zakari? Na roke ka ka rabu da shi Allah na kaiwa karar sa kuma na tabbata zai saka mini. Na bar shi da fitowar rana da faduwar ta”.

    Ta share hawaye da habar mayafinta ta sake cewa. “Dan nan me zan ce maka?” A karshe Inna ta fashe da kuka tana ce da Hauwa “gidan mu ne Hauwa-Kulu! Sarhamu ya kwato mana da karfin mulkin Allah”. 

    Hauwa wani irin shock ta shiga na wucin gadi bayan fahimtar hakikanin halin da ake ciki. A yau ma dakacen nan ta kara yi na shekara da shekaru, mai fatan “INAMA TA GA FUSKAR LIKITA SARHAM!”

    Suka karasa cikin gidan Inna rike da hannun Hauwa shikuma ya dauko bakko kayan su ya kai su har dakin da ya zama na Inna, an saka katifa a kasan kafet dirkekiya an shimfide ta da sabon zanin gado. A gefe ga kwabar saka kaya an yi mata. Haka dakin Hauwa ma amma ita a daki aka yi mata toilet don kada ta sha wahalar fitowa tsakar gida. Ga safayan daki da ba kowa yace na Baban Hauwa ne duk ranar da Allah ya dawo musu da shi. Sai kamshin sabon fenti da suminti gidan yake yi gwanin dadi.

    Dakuna uku ne aka yi musu kamar da, kitchen kuwa da toilets na zamani aka yi masu masu tangaran (tiles) da Inna tayi ta shafawa da hannun ta a gaban Sarham tana shi masa albarka.

    Hauwa duk jikin ta yayi sanyi musamman in ta tuna yadda ta ke share Sarham a baya, da kullacin wai ya makanta ta, Sarham is beyond her imagination a kaunar fisabilillah da yake yi musu.

    Aka kai Hauwa nata dakin aka nuna mata direction na sallah dana zuwa toilet da madannin flushing. Ga dan karamin firji a gefen katifar ta (bed side fridge) Sarham ya ajiye mata don ya san ta da son shan abu mai sanyi tun baya, kai yau Inna da Hauwa farin cikin ya fi gaban ayi masa kuka ko dariya sai dai kawai ayi kurum, kamar yadda Hauwa tayi kurum!

    Bayan sun gama zaga gidan sun zauna suna hira shi da Inna. Ya ce “wai ta yaya ma aka yi takardun gidan suka je hanun Zakari? Bayan kowa ya shaida ya sayarwa da malam Bilyaminu gidan kamar yadda Malam Isa ya bashi labari?”

     Inna ta ce “umh, ai in kana neman hatsabibi ka samu Zakari ka gode Allah, maiyuwuwa yana da na kwarai dinne ya bawa Malam na jabu, ko kuma yasa an yi masa na jabu, oho, tunda har gobe na gonar su Baban Hauwa ya gayamin suna hannun sa, gab da batan Baban Hauwa, yace min sai ya karbi hakkin sa gun dan uwansa Zakari, wanda yake boyewa don a tunanin sa ya dauka Malam bai san da su ba. 

    Ina nufin gonar mahaifin su ta Panshekara wadda girman ta ya kai na naira miliyan daya”.

    Sarham ya shiga mamaki mai yawa, ashe shiyasa Baban sa baya son sake aure? Kullum sai yace masa yana tsoron rarrabuwar kan su ne, shiyasa bai yi musu ‘yan uba ba.

    Sun dade suna zantawa kamar Da da uwar sa, Hauwa kuwa tunda ta shige daki ta kwanta a sabuwar katifa bata kara fitowa ba don daga baya ma wani ni’imtaccen barci ne yayi awon gaba da ita, irin wanda rabon ta da shi tunda Inna ta fara kwanciya ciwo.

    Da ya zo tafiya ne jin ta shiru ya dan leka dakinta, nan ya ganta tayi dai-dai tana kwasar barci da nutsuwa da kwanciyar hankali, numfashin ta yana hawa yana sauka freely, ashe tafi kyau in tana barci irin mutanen da ake kira sleeping beauty. Ya dan kalleta na ‘yan sakanni yana jin ta kamar Sumayyah a ran sa, ya kudurce a zuciyar sa zai tsayawa rayuwar ta, zai ingantata, zai mata abinda idan Sumayyah ce nakasar idanu ta sameta zai tsaya ya yi mata.

    Daga nan gidan su ya koma, a falo ya tadda iyayen sa, kallo daya zaka yi wa Dr. Sarham yanzu ka tabbatar yana cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ba kamar watannin baya ba, gashi Madinah ta cika masa ciki da abinci mai dadi, so bai waiwayi abincin sa dake bisa tebir ba ya zauna gun Abba Prof. amma ya killace bakin sa baiyi zancen su Hauwa ba, don ya lura bat un yau ba Abban (is not interested) akan zancen su, musamman da ya ga ya dauki al’amarin su da muhimmancin da yake neman wuce kima, kuma ya tambayeshi meye alaqar su ta hakika ya tsaya yi masa kame-kame. Tun daga lokacin yace,

     “to in babu wata kebantacciyar alaqa da musuluci ya yarda da ita, to ya cire damuwar rashin ganin su daga ran sa, ya bar su a hannun Ubangijin da ya halicce su, tunda uban su ma da ya bar su ai basu kasa rayuwa ba. 

    Don haka baima kowa zancen ya ga su Hauwa ba, bai sani ba tuni Mai Shari’ah wato Barrister (Mama) ta dade da ramfo shi.

    Kafin kwana uku duk makwabta sun san da dawowar Hauwa da Innar ta, aka yi ta shigowa ana ma Inna barka da arziki, da dawowar ta gidan ta, ana hirar yaushe gamo, aka yi ta tuna baya ana tattaunawa kan girman yara na yanzu, musamman ‘ya’ya mata da ba wuya sun girma, dubi dai yadda Hauwa ta gandame, ana tattaunawa a kai, kusan duk jama’ar Badalar Kofar Na’isa sun san Inna da abinda Zakari yayi mata saboda kyakkyawar mu’amalar ta da kowa, sannan yanzu sabon gidan nasu ya fito da gidan sosai. Har an sawa gidan suna sabon gida. A yanzu sai ya zamana babu gida mai zubin zamani da kuma kyawun nasu a bayan Badalar ta Kofar Na'isa.

    Washegari da suka wayi gari a kwana na uku da tarewar su. Inna ta ce da Hauwa zata shiga gidan Malam Isa su gaisa da iyalinsa, tace saboda ta ga kowa ya shigo mata murna banda Maikosai. Hauwa tace “toh Inna kada ki dade” tace “kada ki damu bazan jima ba”, ta fita.

    Tayi sallama gidan Malam Isa, Maikosai, wadda sunanta na ainahi Talatu, ta gama suyar kosan safe ta sayar, tana wanke kayan suyar ta a gindin rijiya ta amsa sallamar Inna, sannan ta juyo don ganin mai shigowa sai ta ga Innar Hauwa, nan da nan ta yi fuska ta juya ta cigaba da abinda take yi ta barta anan tsaye, sai da ta kammala tas ta zo ta zauna ta baiwa Innar Hauwa kujera ‘yar tsugunne, itama ta samu waje ta zauna akan tabarmar kofar dakin ta, suka gaisa kadaran kadahan sai Inna tace.

    “Zuwa nayi mu gaisa Maikosai, naga kowa na zuwa muna gaisawa, ke kadai ce ban gan ki kin zo ba, shine na shigo in gaida ke, Allah dai yasa lafiya”, inji Inna. 

    Mai kosai ta ce “in kinji shiru ai shine lafiya, lafiya ke buya ba rashinta ba, don haka ni lafiya ta kalau, har kin yi GAIBAR ne kin dawo?” 

    Cikin rashin fahimta Inna tace “menene kuma GAIBA?” Maikosai ta kalle ta a lalace tace “kina nufin ni zaki binne a baibai? Ko ba da hausa nake magana ba? Kin dauka ban ji me kuke shiryawa ke da bazawarin ki Malam Isa Mai Itace ba, na kiyi Gaiba ki dawo ya aure ki? 

    Allah na tuba ko meye abin likewa tsoho kamar malam Isa oho, yana fama da kakhi da majinar tsufa?”

    Inna tace “innalillahi wa’inna ilaihi rajioun, ni Safiya me nake ji haka? Da auren nawa na likewa Malam Isa? Ni Safiyar ko dai wata ce kike nufi kika dauka ni ce?” Maikosai tayi tsaki tace.

     “Ahap! Da bakin sa ya gayamin kin dawo zakuyi Gaiba ya aure ki, ko kin dauka akwai abinda yake boye min?” 

    Inna ta mike tsaye tana fadin “Maikosai baki da lafiya, ina rokon Allah ya baki lafiya”, daga haka ta fice ta barta tana ta sakin maganganu marassa kai bare kafa.

    A zaure ta ci karo da Malam Isa zai shigo, cikin far’a Malam Isa yace “a’ah, Innar Hauwa da kan ta yau a gidan mu? Maraba lale”, wani kallo da Innar Hauwa ta yi masa yasa nan da nan ya sha jinin jikin sa, yayi tsuru-tsuru kamar bafaden da yayiwa sarki karya, tasa kai ta wuce abinta ba tareda ta ce masa kanzil ba.

    Malam Isa ya fada gidan sa kamar an jefo shi, yana kwalawa Maikosai kira, a zaune ya sameta tana ta kunkuni ita kadai yace “uban me kika cewa Safiya?” Tayi tsaki tace “munafurcin da kuke kullawa na gaya mata na san komai” Malam Isa ya yi salati yace “amma Maikosai anyi dabba a cikin garke, kin jika min aiki, tsakanina da ke Allah ya isa”.

    Maikosai ta tafa hannu tace “kace haka mana, saboda kafi so ku cigaba da ninke ni a baibai, saidai inji sallamar kishiya a kaina, duk abinda kuke ciki na sani, da zaryar da kake tayi a gidan su, har kuka yi kulla-kullar da kuka nemo ta kuka dawo da ita unguwar nan duk don kana kulafucin ta”. 

    Malam Isa bai iya tsayawa ya cigaba da sauraron ta ba ya juya da sauri ya bi bayan Innar Hauwa. 

    Tana isa gidan shima ya iso sabida saurin da yake yi saura kadan babbar rigar sa ta tadiye shi. 

    Tana shiga gidan ya doka sallama sai Inna ta dauko mayafinta data rataye a jikin kofa ta fito. Sabanin da da zata yi masa iznin shigowa yanzu sai ta fita ta tadda shi a zauren.

    Suka gaisa Malam Isa yanata rawar jiki yana bata hakuri wai bai san me Maikosai ta gaya mata ba. Inna ta dube shi da manyan idanun ta irin na Hauwa masu neman fadowa kasa sabida girma ta ce.

     “Malam Isa, mutunci da makwabtaka ne tsakanin mu, ina ganin girman ka da mutuncin dake tasakanin ka da maigidana, da hakkin makwabta da kake saukewa dare da rana, bai kamata kuma ka yi min kazafi ba ban ji ba ban gani ba, yaushe nace zan yi GAIBA? Balle har na aure ka?” 

    Malam Isa ya hau gumi yana bata hakuri yace wallahi shi da bakin sa bai yi zancen nan da Maikosai ba, ya dai yi zancen cikin hira da Dan ta Sunusi, inda yace masa “da ace zata yi Gaiba….”.

     Bayan wannan bai kara komai ba, watakila Sunusin ne ya gaya mata, ita kuma ta canza maganar yadda taga dama, amma ta yi hakuri. Inna tace “baka yi min laifin komai ba sai alkhairi Malam Isa, amma ka sani ko Malam Bilyaminu bai dawo ba bazan yi wani aure ba, daga nan har gaban abada! 

    Burina kadai a duniya “Hauwa ce”.  In rayu tare da ita, in kula da ita, in tsare mata mutuncin ta. Amma bayan wannan bani da wani sauran abu da ya rage min a rayuwa ta sai fatan cikawa da Imani”.

    Malam Isa dai hakuri yake bayarwa, ya kuma roketa kan kada hakan yayi sanadin bacin zumunci da makwabtakar su, ya bar zancen har abada ba zai sake tada shi ba, don Sarham ma ya hanashi. Maikosai kuma zai ja mata kunne itama. Inna tace babu komai. Ya wuce. 

    Daga nan ya gaya mata maganar dabbobin ta daya kiwata mata, suna nan garke guda a cikin kangon gidan sa. Inna ta rasa da me zata godewa wannan karimin makwabci, ta yi masa godiya mai tarin yawa don tana matukar son dabbobin ta. Tace ya bar su anan su cigaba da zama tare da nasa, zata cigaba da bada abincin su. Wanda yayi a baya Allah ya biya shi da aljannah. Nan yake gaya mata ai SARHAMU yafi shekara yana sayen dussar su da harawar su.

    Mamakin Inna da Sarham ya kara ninkuwa, ta ji yaron ya kara kwanta mata a rai, wato ba ita kadai ba, ba ‘yar ta kadai ba, hatta dabbobin ta ababen kulawa da darajjawa ne a gare shi.  Ya Allah! Da me zata biya wannan bawan nasa banda addu’ar alkhairi mara yankewa gareshi, da iyayen da suka kawo shi duniya da zuri’ar sa???

    Sukayi sallama ya tafi, ta koma gida tana labartawa Hauwa abinda ya faru a gidan Malam Isa da zauren su. Hauwa tafi Inna fusata, tace zata je ta tadda Talatu Maikosai ta gaya mata ba abinda zai kawo su gidan ta koda zasu koma kwana a kan kwalbati in sha Allahu. 

    Inna ta hana ta tace “tura mata aniyarta mutuncin Malam Isan zaki duba, na gaya miki ashe dabbobina duka suna garken sa yana kiwata mini har yau”. Wannan ne ya dan sanyaya ran Hauwa ta daina jin haushin Malam Isa amma sosai ta shaka da Maikosai.

    ****            *****                *****

         RACE COURSE, KANO

A

 wajen kallon Polo na Dawakai wato a filin sukuwa (Race Course) dake unguwar Nassarawa, Salele ya ga Jamil Zakari a matsayin wanda ya lashe kofin gasar dawakai (sukuwa) wanda akayi a ranar, dama dai Jamilu kwararren dan Polo ne, sun dade suna haduwa da Salele a wurare mabanbanta na tseren Dawakai, suna gaisawa, don ya san shi tun a jinyar da Hauwa tayi, sanda ya kadeta da mota.

    Yau da Jamil Zakari ya lashe kofi Salele ya shiga sahun samari masu kutsawa suna gaisawa da Jamil Zakari Dan Agundi, Salele yana cikin samari ‘yan kallo masu cike da fata da burin watarana su zama manyan ‘yan Polo kamar Jamil Zakari Dan Agundi.

            An fara watsewa kenan Jamilu ya shiga farar motar sa kirar (kia picanto) zai tafi sai ya hango Salele yana ‘waiving’ dinsa daga nesa wato yana ta dago masa hannu, har ya kunna motar ya dakata har Salele ya iso da gudu yana haki yana dariya. Jamilu ya fiddo gudar naira dari ya baiwa Salele, wadda a yanzu zata yi kimar kamar ace naira dubu daya. Salele don murna bai san lokacin da ya hau barin zance ba.

    “Yaushe zaka zo gidan su Innar Hauwa ne? Sun dawo bada jimawa ba, sun gine gidan su ya koma sabo dal, sun tare tuntuni, jiya ma Innar Hauwa ta shiga gun Innata sun gaisa har Innata ta zo gidan ta yiwa Hauwa kitso”.

    Jamilu yayi sakare! Yana sauraron Salele, kafin ya ji zuciyar sa ta harba, tsohon mikin son Hauwa-Kulu da yake kwana yake tashi da shi ya motsa kansa a kasan ransa, bai san sanda yace da Salele ya shigo gaban motarsa su je ba. 

    Salele ya kame a gaban mota suka dauki hanyar Kofar Na’isa.


           Inna da Hauwa a tsakar gida, Inna na tankaden garin tuwo Hauwa na sallar la’asar akan dardumar sallah anan tsakar gidan su mai yalwa da sanyin sabon siminti, saidai yanzu babu shukokin su na Umbrella da bishiyar dalbejiya, don haka basu fiya zama a tsakar gidan da rana ba sai da yamma irin haka ko da daddare.

    Sai sallamar Salele suka ji, yace Inna kuna da bako” Inna da yake ta san Sarham zai zo sai tace “gidan bakon sa ne da zai tsaya a waje ya turo ka? Ko ba sallama yake da kansa ya shigo ba? Yau nake ganin sabon salo banbarakwai wai namiji da suna Hajara, kace ya shigo, kuma daga yau kada ya kara aikomin yaro idan yazo, shi da gidan su?” 

    Salele ya koma yace da Jamilu Inna tace ya shiga. 

    Inna da Hauwa sai ganin Jamilu Zakari suka yi a kan su, yayi sallama kamar an jefo shi. Ya shigo tsakar gidan su cikin kyakkyawar shiga ta hawan Polo.

    Idanun sa akan Hauwa ya hau sakin Hamdalah a fili kafin ya zube gaban Inna kamar mai neman gafara. Zai fara gaisheta Inna ta ce “tsaya-tsaya, wa nake gani kamar Jamilu? Wai dama kai ne ka aiko Salele?” yace “ni ne Inna” tace “to sawunka a likkafa Jamilu ka juya ka koma inda ka fito, kafin ka janyo min tijara, yau ko gaisuwa babu tsakanin mu wallahi ka ji na rantse ka tashi ka fice mana daga gida, kada ka kara zuwa balle ka janyo min bacin rai Ina fama da ciwon zuciya, zuciyata tayi rauni kuma bata da lafiya bazata iya daukar bakin cikin ubanka ba”.

     Inna ta soma hawaye, tana rokon Jamilu ya tafi. Tun ba'a kaiwa Zakari labarin an ganshi a gidansu ba. Jamilu ya mike ba shiru, yana kallon Hauwa da wani sabon so a cikin idanunsa, musamman da yaga ta kara girma tayi wani irin kyau ta yi bulbul da ita, datar ta tayi sumul. Likita Sarham ya tsaya mata da shan (freshmilk) wato danyar madara tana Nan fal firinjinta tun dawowarsu ita take daddaka don bata iya cin abinci sosai.

    Jikin sa yana rawa ya soma ja da baya. Tace “ko a lahira wani kan ci albarkacin wani, albarkacin ka Zakari ya ci ban yi karar sa hukuma ta kwatar min hakkina da tozarcin da yayi min a kan ka ba.

     Don haka tun muna shaida juna muna kuma ganin sauran mutuncin juna to ka fita daga inda muke”.

     Jamilu ya juya a hankali ya fice, saida ya tsaya a zaure ya share zufa da hawaye, shi ya san da gaske yake son Hauwa, son da yake mata ba shi ya dorawa kansa ba Allah ne. Saboda ita har yau ya kasa yin aure, alhalin ba abinda bai mallaka ba na rufin asiri a rayuwar sa.

    Daga nan gidan su Inna gidan Hajiyar sa ya wuce, ya kafa mata kahon zuka kan taje ta baiwa Inna hakuri, kada ta hukunta shi da laifin da ba nashi ba. Hajiya Rumanatu na jin an ga su Inna ta dauki mayafin ta tace su je ya kaita. Don dama zaman Jamilu har yau ba aure ya dameta.

    A mota Jamilu ya zauna, bayan Hajiyarsa ta shiga gidan, ya kifa kai a kan sitiyari ya rasa inda zai sa kansa da damuwa. Bai san yana son Hauwa bama sai yanzu, data kara girma ta zama cikakkiyar budurwa komai ya kai ya kawo. Hajiyarsa ta shige gidan da sallama.

     Inna sai ganin Haj. Rumanatu tayi tayi sallama, Inna ta amsa fuska ba yabo ba Kuma fallasa don ta gaji da nacin Jamilu da uwarsa.

    Inna ta yiwa kawarta tun ta kuruciya wato Rumanatu tarba ta mutunci, irin ta tsofaffin kawaye, bayan sun gaisa kafin Hajiya Ruma tace komai Inna ta hau rokon ta kan ta raba Jamilu da zuwa inda suke, ya rabu da Hauwa. Tace, “ku yi hakuri, ni babu wani aure da zan yi wa Hauwa-Kulu fau-fau, balle na dauketa da hannuna na kaita cikin zuri’ar Zakari a hallakamin ita da niyya sabida ‘yan ubanci irin nasa, muddin Zakari yaji labarin Jamilu na zuwa wallahi zai juyo da rashin mutuncin sa kan mu”.

    Iyayen suna can dakin Inna suna zantawa suna kuma fahimtar juna, Haj. Rumanatu na mai gamsuwa da hujjojin Inna akan bazata iya aurar da Hauwa ba, ba ga Jamilu kadai ba har ga kowanne namiji ma. A lokacin Salele yazo zai wuce, sai Jamilu ya roke shi ya sadada a hankali don Allah ya kira masa Hauwa su gaisa.

     Nan da nan Salele yabi umarnin ubangidan sa ya je yace da Hauwa tazo ana kiranta za’a bata sako, tace a baiwa Inna mana! Yace tana da bakuwa ne sun kule suna sirri. Haka ya kalallameta ta taso ta tako da hijab mai hannu har kasa a jikin ta zuwa soron su.

    Sai ta ji muryar Yayan ta Jamilu ya ce “Hauwa!” Ya saki ajiyar zuciya ya sake cewa, “Hauwa nine Jamilu, ni nace Salele ya kira ki, Hauwa ina kuka tafi duk tsayin shekarun nan kusan uku sai dawowa nayi daga Delta na nemeku na rasa? Ko kinsan har yau ban yi aure ba ina tsumayin dawowar ki Hauwa?”

     Hauwa ta dan waiga kamar me tsoron ko Inna na wajen, tace “Yaya Jamilu ne da gaske?” “Nine Hauwa’u, I missed you so much, and I truly love you kin sani Hauwa”. Hauwa ta ji duk ta rikice, ta kasa cewa komai domin maganar sa ta yau ta mata gingiringin, ta mata nauyi, rana ta farko da wani da namiji ya furta mata kalmar so da bakinsa da nata, taji kunya har kasan ranta, Jamilu yace.

     “Ki bani dama don Allah Hauwa, in turo magabatana gun Inna, in sha Allahu zamu yi aure ko a boye ne in ya so mu bar Kano gabadaya ba tareda Babana ya sani ba, ina mai baki hakuri kan abinda ya faru, na ji komai bayan dawowata kuma ba inda ban neme ku ba cikin Kano da wajen ta ban samu ko wanda yace ya san inda kuke ba.

     A kan ki Hauwa Babana ya kusa tsine mini, Inna kua ta kasa gane karfin son da nake miki ba irin wand azan iya hakura bane, don Allah Hauwa ki manta da komai, ki duba ‘yan uwantakar dake tsakanin mu, mu yi auren mu cikin alfarmar zumunci da kaunar juna, dama Bankinmu zasu yimin transfer kwanannan zuwa Ikeja, in yaso sai mu koma can”. 

    Hauwa ta rasa abinda zata ce, domin Jamilu ya matukar bata tausayi, ya tafi da imaninta, ya kuma gama saye zuciyarta da wannan kauna da ya nuna mata, tayi shiru kawai tana sauraron Jamilun da zuciyarta da kunnuwanta, tana mai yarda da kowacce kalma da kowanne harafi dake fita daga bakinsa, zuwa can ta ce.

     “Ni fa Yaya Jamilu banida matsala, amma babu ruwa na a kan maganar aure. Allah ya sani ban rike ka da komai a raina ba, sannan kuma bana kin ka, ina ganin abinda yafi, ka nemi amicewar Inna ba tawa ba, ni din da komai nawa ababen ikonta ne kuma ni mai son yin biyayya ce a gareta, don haka duk wani hukunci da Inna tayi akaina, inaso ko bana so, bani da ja a kansa”.

    Jamilu ya gyada kai cikin gamsuwa da kalamanta, at least ya fahimci Hauwa bata kin auren sa koda bata furta tana son shi ba, tofa babu kiyayyarsa ko kadan a tare da ita, ya rausayar da kai yace, 

    “ni kuma na yi alkawarin zan lallashi Inna, idan ta bani ke zan kuma kula mata da ke kamar yadda zan kula da kaina. I can understand her fear, kuma kwarai nake la’akari da abida take hangowa (taking the marital responsibility of a blind person will never be easy) amma abinda ta manta ni dan uwanki ne, jinin ki ne, I can possibly endure it fiyeda bare, aure sunnar Manzon Allah ne SAW bai yuwuwa ace saboda lalura ta makanta baza’a yi shi kwata-kwata ba tunda ke din ‘yar adam ce kamar kowa mai lafiyar yin aure, ni Jamilu na yi alkawarin zan zame miki miji abin alfahari kuma dan uwa wanda zamu raba rashin idanun ki tare, sannan wanda zai tsaya wajen ganin kin zamewa ‘ya’yan ki uwa tagari a yadda Allah ke son ganin ki, tsan tsaya tsayin daka wajen ganin cewa lalurar rashin gani bai sa kin kasa basu kulawa ba.

     Ni da kaina zan taya ki rainon ‘ya’yan mu Hauwa’u”. sai Hauwa ta kai tafuka ta rufe fuska cikin jin kunya tana murmushi kamar tace kasar ta tsage ta shige cikinta.

    Maganar Jamilu ta karshe kai tsaye ta sauka a kunnuwan Dr. Sarham Abbas ne, a lokacin da ya kashe motar sa “opel astra’, ya tako zuwa gidan ya sawo kai soron, cikin takunshin nan mai sauti gab-gab-gab na bakin cover shoes ma matukar daraja, ya shigo zauren su Hauwa, yayi harr da idanunsa a fuskokin su.

    Yana sanye da shirt fara kal, wadda aka yi rubutun ‘Dolce&Gabbana’ a jikin ta, da bakin Trouser ne na ‘Tokyo Jeans’. Kansa babu hula, sumar nan tasa baka wuluk ta fulanin Shanono ta cika kan sa har ta nannade (curl), a kafafun shi bain takalmi ne sau ciki na bakar fata kirar Italy. Da farko he was shocked, da ganin Hauwa tsaye da namiji a zaure, da abinda kunnuwansa suka jiye masa Jamilu na fade, da kuma yanayin da yaga Hauwa wanda kiri-kiri yana nuna tadin soyayya. Amma da yake shi din shine Sarhamu, sai ya bagarar, yashare, ya hadiyefirgicewarsa yayi kamar bai ji kalaman Jamilu ba, yayi musu sallama da dusassar muryarsa ya kuma baiwa Jamilu hannu suka yi musabiha, ya dan kalli Hauwa yana mamaki yana karawa, sannan ya shige cikin gidan.

    Inna ta rako Babar Jamilu zata tafi suka yi kacibusa da shi yana shigowa tsakar gidan, kafin Jamilu ya samu zarafin tambayar Hauwa ko wanene shi ya isa dakin Inna, shigowarsa tasa hankalin Inna ya koma kansa, a gurguje suka yi sallama da Haj. Rumanatu ta wuce, bayan ta tabbatar mata cewa kwarai ta fahimce ta, zata yi iya yinta wajen lallashin Jamilu ya hakura, ko don kwanciyar hankalin Inna da zaman lafiyar su da Babansa dan jidali (Zakari).

    Sarham ya zauna a falon Inna yana jiran ta har ta shigo ta zauna akujerar dake fuskantar sa, suka gaisa, sai ya koma cikin kujera ya kishingida yayi shiru, har da dan juyawa ya kalli taga yaga ko Hauwa taji kunyar idonsa na abinda ya tarar tana yi (soyayya) tayi maza ta baro saurayin ta shigo gida ko a’ah? Amma ina! Ko keyarta bai gani ba, tana can suna sallama da Jamilu kamar bazasu rabu ba, Sarham ya mike dogayen kafafunsa a kasa. Bai iya kara cewa komai ba don al’ajabi da mamakin Hauwa.

     Can jimawa sai ga Hauwa ta shigo, tana tafe abunta kanta tsaye, babu ko lalube irin na makafi, tsabar ta gane hanyar dakinta, tasa kai zata wuce dakinta taci uban tuntube da kafafun Sarham, saura kadan ta kifa ta ci da baka. Ko sannu bai mata ba balle yayi ‘apologizing’. Cikin fushi tace.

     “Inna wa ya saka min kafa zai kayar da ni haka?” Inna ta yi mata shiru, kafin tace “daga ina kike?” tace “Yaya Jamilu ne ya kira ni soro”.

     Haba! Sai Inna ta balle da fada kamar ta rufe ta da duka, cewa take “da iznina kika fita zance gun Jamilu? Kece da zuwa zance Hauwa da wane idon zaki ga saurayin?” Saida Dr. Sarham yace “ya isa Inna, kinsan kinada matsalar zuciya, kada ki dinga bata ranki irin haka kan kananan abubuwa har ya tabo zuciyar ki”. Hauwa ta wuce dakin ta a sanyaye, bayan ta gaishe shi. Dr. Sarham yaki ko amsawa balle ya nuna ya san tana gaishe shi, har ta wuce tana mamakin me ta yi wa Dr. Sarham yau? 

    Gashi dai yau bai kira sunanta da yake mararin kira na MAIJIDDAH cikin farin-ciki, yalwar fuska da far’ar nan tasa ba, bai kuma amsa gaisuwar ta da kulawa da (attention) kamar yadda ya saba ba. to me ta yiwa Likitan Inna?

    Ji yayi gabadaya yau ya kasa zama ya dade a gidan yadda ya saba, ya kuma kasa hira da Inna yadda suka saba, ita kadai take ta babatunta, daga karshe da Inna taga shirunsa yayi yawa sai ta dago ta dubeshi tace,

     “ko lafiya kake kuwa likita? Na ganka ba’a yadda na saba ganinka ba”.

     Sai kawai ya mike yana cewa “bari in karasa gida Inna, kaina ke min ciwo, yanata sarawa, idan na ji sauki zuwa gobe ko jibi in sha Allah zan shigo”.

     Inna tace “ni ai ban sani ba, gashi har nayi maka tuwon Acca kuwa, da miyar da kake so ta zogale” Sarham ya juya a lokacin yana saka takalman sa a bakin kofar falon, yace “ba komai Inna, some other time, zan ci”.

     Suka yi sallama dukkansu jiki babu kwari ya juya ya tafi. Ko sallama bai yiwa Hauwa ba.

    Yana tuki yana hada gumi kashirban, duk da sanyin AC din motar sa. Abun ya daure masa kai matuka. Ya kuma sakashi a damuwar da ya kasa sanin ma’anarta. Yana isa gida yaji ana murnar zuwan Sumayyah, wadda ta zo hutun karshen shekara da barkar haihuwar Waheedah. 

    Kamar bai ga Sumayyah ba, bayan kuma har ido sun hada a falon, ya dauke kai yasa kai ya wuce zuwa dakin sa bayan yace musu cikin jam’u “sannun ku da gida”.

    Mama ta bi shi da kallo, Sumayyah kuma ta ce. “Bhaiya lafiya kalau yake? Kaamr bai ganni ba Mama?” Mama ta ce “oho muku, kun fi kusa”. Surayyah ta ce “nafi tunanin wani ne ya bato masa rai daga waje, baki ga fuskarsa kamar hadarin da ya nausa yayi gabas ba?” Sumayyah sai ta mike ta bi bayan sa zuwa dakin nasa.

    Sallama tayi daga bakin kofa, sai da ya bata iznin shiga ta shiga dakin ta same shi zaune akan ‘study chair’ ya rafka uban tagumi, ta ce.

     “Bhaiya baka ganni bane ka wuce bamu ko gaisa ba?” 

    Ya dago ya dubeta da jan ido, a lokacin taga idanuwansa sun kada, yace “a’ah Summy ce yau a gari? Saukar yaushe?” Tace tun dazu na sauka, ta gabana fa ka wuce, har ido mun hada, ka san mun yi hutu shine fa nace bari kawai in taho ganin Hauwa’u”. 

    Ta zauna a kujerar ‘sofa’ kwaya daya dake dakin, ta ce “Bhaiya duk ka birkice, you are upset, anya lafiya kake kuwa? Na ganka ‘moody’ tunda ka shigo”. Yace “Sumayyah, bansan yadda zaki fassara abinda ya sani a damuwar ba idan na fada miki, ba wani abu bane serious I don’t know why I made it serious, abun ne ya bani mamaki, ya kuma bata min rai, wai Hauwar nan da kika sani ko ido bata da shi, amma ta iya tsayawa zance da saurayi a soro???

     Ni ban taba ganin abinda ya bani mamaki ya rikitani irin wannan ganin dana yi ba”.

     Sumayyah tana sane tace “Hauwa wacce? Baby Hauwan mu?” Ya harareta, “ke bana son sakarcin banza. Hauwa ‘yar Inna mana, kanwata ta kofar Na’isa” Sumayyah ta wani ce “au ho! Ka ce min kawai Hauwar Inna, HAUWA-KULU ‘yar cikin BADALA!”. Sai ta hau tuntsira dariya tace “Bhaiya, yanzu ganin Hauwa da saurayi shine abinda ya birkita ka haka?” 

    Sarham ya harareta yace “Sumayyah yaya ina miki magana ‘serious’ za kina dariyar rainin wayo, Hauwa fa, wadda ko ido bata da shi, ina zata kai wani namiji da sunan soyayya? 

    Ganin ta nayi da wani cousin dinta suna zance fa, zance na saurayi da budurwa! Wai sunan sa Jamilu, dan kanin Babanta ne”.

     Ai kuwa Sumayyah ta kara tuntsirewa da dariya sai da tayi mai isarta, shi kuma ya shaka sosai, saida dariyar ta lafa mata ta ce.

     “Bhaiya makaho ba mutum bane? Ko kuwa makaho bai san SO da mai son sa ba?

     Don tana makauniya shikenan sai akace bazata yi aure ko soyayya ta ji dadin rayuwar ta kamar kowanne dan adam ba? Ko in bata saurari masu son ta ba kai din auren ta zaka yi?

     Yau nake ganin ikon Allah, yau ina ganin abinda ya gagari Kakata Kulu, kai ka dafe dahir har da ‘yar ka tubarkallah, shine ita zaka yi mata fatan ta tsufa a dakin uwar ta, alhalin kai ba son ta kake yi ba, wannan fa shi ake kira karfin hali barawo da sallama ko in ce, Bhaiya na, da tsabar son kai tsagwaro. Wani hali da ban san shi da shi ba. 

    Ni wallahi gani nake ma babu wanda ya dace da ya aureta kamar dan uwan nata, tunda jinin su daya, ya san darajar ta, zai yi hakuri da nakasar ta, ya riketa da daraja a gidan aure, don kai kam Bhaiya, baka da alqiblah.

     Ayi magana cibi ya zama kari!”. 

    Ta sake tuntsirewa da dariya ta ce “sai amara kirazan biki, mu ne manyan kawayen amarya Hauwa’u, a bikin ta da Yayanmu Jamilu”.  Sumayyah har da dan gudu-gudunta ta bar dakin, tana cigaba da tillika dariyar shegantaka. Don ta san ta gama kunna shi in ta kara minti uku a gabansa zai iya losing control kai mata duka. Don tana ganin yadda yake girma idanunsa tunda ta soma shegantakarta.

    Maganganun ta dinnan, suka taru suka zamewa Dr. Sarham “a warm food for thought!” A tsayin wannan daren bakidayansa kona rabin away a kasa runtsawa. 

    Sarham sai faman juyi yake a kan gadonsa, daga wannan gefen zuwa wancan, yana tauna maganganun Sumayyah a kwakwalwarsa, yana kuma fassarasu a zuciyarsa cikinma’auni na hankali da tunaninsa. Daren da yazo masa da tarin ‘alterations’ koko ‘revolutions’ wadanda a can baya bai taba hango yiwuwar makamantansu ba.

    Ko na minti daya ya kasa rintsawa. Idan ya tuna maganganun Sumayyah. A ganin sa Sumayyah maganganu ta gasa masa masu zafi ta cikin ruwan sanyi, koko yace jirwaye tayi masa mai kama da wanka, don dama tana kullace da shi akan abinda yayi mata, don kawai ta tambaye shi ko son Hauwa yake yi shekarun baya, bazata manta ba yayi mata wulakancin da bata zata ba, kiris ya rage ya doketa. A nata bangaren Sumayyah, ta dade tana kiwon mu’amalar sa da su Hauwa ta rasa alkiblarsa, musamman in ta tuna abinda yayi mata daga ta tambaye shi ko son Hauwa yake? Ta tuna a ranar dukanta ne kawai bai yi ba, shine abinda take nufi da “ayi magana cibi ya zama kari”.

    Da gasken gaske ya kasa barci a daren, sai faman tauna maganganun Sumayyah wadanda ya kira jirwaye mai kama da wanka.

    Washegari ya samu kansa da kasa zuwa gidan Inna, saboda har zuwa lokacin ransa a bace yake, haka a sauran kwanaki ukun da suka biyo baya ko hanyar kofar Na’isa bai kalla ba, yana like wajen su Waheedah, kamar ya maidasu ciki, don a can yake samun sanyin ran sa, daga zafafan maganganun Sumayyah da haushin Hauwa (a ganin sa bakaken maganganu ne Summy ta gasa masa son ran ta), da suka dade suna dafa shi kamar dafaffiyar masara, kuma ya kasa cewa Sumayyah komai a kai again bayan kuma ita kadai ce zai iya zancennan da ita. Madinah ta samu lokacin sa sosai a wannan satin, don yanzu kullum yana wuni tare da su baya zirga-zirgar gidansu Inna.

    Inna na talgen tuwo a yammacin yau da Sarham ya kwashe kwanaki bakwai bai zo gidan su ba, sai ya fado mata a rai, ta dubi Hauwa dake wankin sittirun ta a bakin famfo tace.

    “Kuluwa!”

     Hauwa ta tsuke baki ta kuma tsuke fuska bata amsa ba, ai ta san in ta ce mata Kuluwa bazata amsa ba, sai ta ce “ni kuwa kin lura da abinda na lura da shi?” Hauwa tace “me?” “Likita Sarhamu, yau kwana bakwai bai zo gidannan ba, tun ranar da ya zo yace min kansa na ciwo, yanzu haka jikin ne ya matsa masa tunda har kika ga yayi wannan dadewar bai zo ba”.

     Hauwa ta yi shiru bata ce komai ba, ta cigaba da wankin ta, ashe ba ita kadai ta lura da rashin zuwan nasa ba. Inna ta sake cewa.

     “kin ga da ace na san gidan su sai in je in duba shi”.

    A nan ne Hauwa ta bata amsa,

     “kai su Inna akwai wuce gona da iri”.

     “Ba wuce gona da iri bane Hauwa-Kulu, baki ji fadar bahaushe ba? Yace KA GAIDA MAI GAISHEKA KO DA BAZAI AMSA BA!”

    Wannnan magana ta karshe da Inna ta yi, ta yi ta ne a kunnen dan halak din wato (Sarham), don a lokacin ya iso tsakar gidan da kasaitattar sallama a bakin sa.

     Nan da nan Inna ta bar abinda take yi a madafin ta fito, ta washe baki tana amsawa, “maraba da Da na Sarhamu, likita Sarhamu na ne tafe? Dan halak yanzu nake zancen ka, sai gaka”. 

    Sarham ya tsugunna a kofar kitchen din yana gaida Inna, Inna ta koma ta kashe wutar tuwon, ta taso suka shiga falon ta tare, suka kara gaisawa, Inna sai taga duk ya rame mata, tace “Likita jikin ne ya boye ka ne?” Ya ce “a’ah Inna lafiya ta kalau, kwana biyunnan dai ban cika fitowa ba, ina can wajen su Hauwa’u karama kullum”.

     Hauwa ta shigo da sallama tana dan dafa bango, ta isa kofar dakin ta sannan ta juyo saitin da ta ke jin tashin tattausar muryar Sarham, ta ce cikin girmamawa “Dr. barka da zuwa, ina wuni?”

     Ya dago kai ya kalle ta kadan, kayan jikin ta sun dan jike sun manne a fatar jikin ta, Hauwa yar shekara sha takwas ta gama samun duk wani dirin jikin da jikinta zai bayar, da kyakkyawar suffa na abinda ake nema a tare da budurwa ‘teenager’, nata har ya zarta yawan shekarun ta, don tsammani zakayi ta kai shekaru ashirin da daya. 

    Tun asalinta Hauwa bata da rama haka take ‘yar duma-duma, lubu-lubu (luscious). Dr. Sarham ya yi wata ‘yar ajiyar zuciya ba tareda ya san ya yi ba, yana tuno kwailancin ta na shekaru biyar a baya, wai itace haka yau a gabansa, yace a hankali “lafiya kalau, ina Saurayin ki dan polo dan gayu?” ‘yar dariya Hauwa ta yi, ta shige dakin ta bata ce masa komai ba. 

    Sai Inna ce tayi kwafa ta ce, “ai ka bar ni da Hauwa da Jamilu kawai, nice maganin su da rashin kangadonsu, da ni suke zancen wallahi, na sa uwarsa Rumanatu tayi musu iyaka, idan yaji toh, in bai ji ba na rantse zan iya kai shi kotu don alkali yayi musu iyaka.

    Na fada na kara ni fa bazan taba yi wa Hauwa wani aure ba, balle in bawa dan Zakari.

    Allah na tuba ko dan shugaban kasa ne ya zo neman auren Hauwa, wallahi bazani bayar ba, balle dan Zakari tsatson zalunci. 

    A cikin burika na masu kyau a kan Hauwa, babu batun yi mata aure a ciki, babban burina shine ta yi karatunnan na zamani mai zurfi in dai makafi na iyawa kamar yadda ta fara, ta samu abunda ko bayan raina zata dogara da kan ta, kuma in karfina ya kare kada nata raunin ya bayyana dalilin rashin karfi na, ko in ta Allah ta kasance min hakan ya kassarata. 

    Ni din nan nice karfin Hauwa, ni ce kuma idanun ta, bazan taba bari a wulakanta min ita da sunan aure ba, ko a ci mutuncin lalurar ta a dalilin aure, shi yasa na gwammace in adanata a gabana, in kula da ita, tayi ta karatu, duk da ni ma ba karatun nayi ba, amma alhamdulillahi ni lafiya ta kalau, zan rayu ko ba ilmin zamani ba tare da na zamewa kowa labiliti ba.

    Amma Hauwa fa? Ai duk wanda na bawa auren ta na kware shi, domin na hada shi da aiki da jidali. Itama kuma na sayo mata rashin kwanciyar hankali. Don haka maganin kada a ji, kada a soma. 

    Gashi bani da matallafi namiji wanda zai tsayawa Hauwa ta samu ta yi karatun nan tunda ni bansan kansa ba, da wannan yau nake baka amanar Hauwa-Kulu Sarhamu, ina mai baka amanar ta don na amince maka, na kuma amince bat un yau kaunar ka damu ta saboda Allah ce. 

    Don Allah likita ka taimaka min, wajen cikar burika na a kanta, na tayi karatu mai zurfi wanda zai amfani al’umma ya kuma amfane ta duk da nakasar ta. Bana so nakasar nan tata ta zame mata rauni, so nake nakasarta ta zama ado a gareta.

    Inna ta soma sharar hawaye ta ce “gashi Bilyaminu ban san inda yake ba, bansan a halin da yake ciki ba, yana mace ne ko yana raye Allah masani, na tabbata da ace yana tare da mu, shima burin sa zai zama irin nawa ne akan Hauwa, don a komai muna kasancewa da ra’ayi daya ni da shi.

    Allah ya gani bazan iya baiwa Jamilu auren ta ba duk da na san a shirye yake da ya tsayawa Hauwa, ba don komai ba sai don ubansa, amma ba don yayi min wani abu ba, ko bai cancanta a bashi aure ba.

    Ko Hauwa-Kulu zata tsufa ba aure, tana nan a kwibi na, (a kusa da ni) ba inda zata da sunan aure”.

    Hauwa daga dakin ta duk tana jiyo abunda Inna ke fadi akan ta, sai ta samu kanta da dimaucewa, don fisabililahi ko ba’a fada ba ta san zuciyarta ta amince da Yaya Jamilu dari bisa dari, yau ga Inna na cewa a dakin ta zata tsufa. Ya Allah! Itafa mantawa take da makantar nan tata, idan har ba bude littafi da zummar yin karatu taga duhu didim tayi ba, mantawa take bata da ido, saboda rayuwar ta cike take da baiwarwaki da kuma alfarmomin Ubangiji masu yawa da wadatar zuci.

    Ji take babu wani abu da mai lafiya yake yi a rayuwar duniya wanda bazata iya ba, musamman aure da hayayyafa.

    Inna da Sarham sun jima suna hira, yana zaune dirshan a gabanta. Inna nata kashe zuciyar Sarham da kalamanta masu nuna hakikanin MOTHERHOOD a kan diyarta Hauwa-Kulu, yau ya fahimci ba karamin so Inna take yi wa Hauwa ba.

    Ya ci tuwon da Inna tayi kafin ya tafi wanda tuwon masara ne miyar yakuwa, ta zuba masa soyayyen manshanu a ciki da yankan naman rago biyu. Ta kuma hada masa lamurje/zobo mai sanyi wanda tasa a firjin Hauwa yayi sanyi.

    Dr. Sarham tunda ya bar gidan su Hauwa ba tareda yau ma ya iya tsayawa a kofar dakinta yadda ya saba ya yiwa Hauwa sallama ba, kasa shiga Sorondinki yayi yau, saboda halin da ya samu zuciyar sa a ciki a kan maganganun da suka yi yau shi da Inna heart-to-heart, ta gama fede masa zahirin abinda ke karkashin zuciyar ta akan miskiniyar diyar ta, HAUWA-KULU, wanda dan cikin ta kadai zata iya gayamawa, amma shi yau ta zaunar dashi ta gaya masa duk wani abu dake karkashin zuciyarta a kan future dinta bisa radadin da take ji na nakasar diyarta.

     Kai tsaye ta bayan gidan ya wuce ya lallaba ya shige dakinsa, ba tareda kowa ya san da dawowar sa ba. 

    Sarham ya kulle kansa don kada Sumayyah ta zo ta dame shi da dumi, dama kuma Inna ta ciko masa cikinsa taf da abincin ta, don haka baya bukatar karin cin abincin Mama yau.

    Ya kwanta a ranar a tsakiyar gadon sa yana tunanin maganganun Inna, ya kuma debo na kanwarsa Sumayyah na rannan ya kara akan su, wato yayi addition, yana tarawa yana debewa, tsakanin maganganun Inna da maganganun Sumayyah….

    Sumayyah ta ce “Hauwa mutum ce kamar kowanne dan adam, tana da right din yin aure da bukatar yin sa kamar kowa ‘in spite of her disability’, Uwarta kuma ta ce ko zata tsufa a gida bazata bata wannna damar ba.

    Ba don komai ba sai don tana guje mata wulakanci da tozarci a dalilin nakasar da shi Sarham yayi mata lasisin ta.

     Bayan kuma addini da al’ada da ‘yancin dan adamtaka duka sun bata damar yin aure. Shin tsakanain Inna da Sumayyah, waye mai gaskiya akan future din HAUWA-KULU???

    A take kaso mafi rinjaye na zuciyar Sarham ya ce “Sumayyah ce mai gaskiya!!! 

    Ita Inna ba wai bata so Hauwa tayi aure bane a’ah, gudun kada a wulakanta mata ita ne da sunan aure, da guje mata tozarci da dawainiyar aure da take da tabbacin bazata iya ba sabida rashin ido, yasa ta gwammace tayi ta ajiyar ta a daki. Wato abinda ka san bazaka samu ba hada shi da bana so! Amma ita Hauwa din tunda har take kula Jamilu, to ya tabbata tana son tayi auren kenan ko bata furta ba. Don Inna ta gaya masa yadda Hauwa ke sakewa da Jamilu ita kanta abin yana bata mamaki matuka. Sai ya samu kansa da tambayar kan sa to KO DAI HAUWA SON AUREN JAMILU TAKE YI?      

      Sarham sai yaji ran sa yayi wani iri mummunan baci, a take wani tunani ya bijiro masa, me zai hana shi Sarham din ya aure Hauwa kowa ya huta (ko da baya son ta so irin na soyayyah irin wanda yake yi wa matarsa Madinah, don shi kadai ne solution ga rayuwar ta (shi Sarham din), da zamowa maslaha ga mahaifiyar ta, hakan zai fi alkhairi fiye da auren Jamilu ko wanin sa ga Hauwa. Tunda maganar Hauwa ta dauwama ba aure ba dabara bace so-karbau, a matsayin ta na ‘yar adam mai cikar lafiya da ‘sexual hormones’ kamar kowa dole tana bukatar yin aure.

    A take Sarham ya shiga gayawa kansa; zai auri HAUWA-KULU domin wasu dalilai masu tarin yawa da ya dade yana dambarwa da zuciyar sa a kansu, amma ba don kalmar SO ta gitta ko zata gitta nan gaba a tsakaninsu ba. SO guda daya ne a zuciyar sa; kuma na matar sa MADINAH uwar Hauwa-Waheedah ne.

    Zai auri HAUWA ne a dalilin ya san ta kullace shi, akan-karan kan sa kuma yana son kankare wannan kullacin nasa dake kasan zuciyarta, har gobe ya kasa yafewa kansa zama sanadin makantar ta. Babu kuma ta hanyar da zai iya kankare wannan tabon nasa daga ran Hauwa in ba ta sanadin aure da hayayyafa ba.

    Zai kuma yi amfani da kwarewar sa ta yanzu, wajen ganin ganin ta ya dawo, koda ba duka ba, da iznin Ubangiji. 

    A karshe ya gayawa kansa zai auri HAUWA domin yana tausayin Inna, kuma yana kaunar ta, don haka zai karbi amanar nan data bashi ne ta hanyar AURE wanda ta hanyar sa ne kadai zai iya cika mata burin ta, na kular mata da ilmin Hauwa da rayuwarta gabadaya, zai yi kokari wajen cikawa Inna burikan ta a kan HAUWA-KULU ne kadai idan ya samu damar auren ta tunda shi ba mazaunin Kano bane. Auren Hauwa gareshi ta kowanne bangare JIHADI ne maigirma kuma solution ga rayuwa da zukatan bayin Allah masu yawa. Ba sai don SO kadai ake aure ba.

     Ya san dole ce ta sata yanke hukuncin kin yi wa Hauwa aure, amma ba don bata so ba, tunda burin kowacce uwa shine ta kai ‘yar ta gidan miji, idan ta isa munzali.

Ta amma ta wacce hanya zai fara? Wadanne matakai zai bi wajen ganin tabbatuwar hakan? Ya san dai wannan hukuncin da ya yanke daidai yake da a ce ya daukowa kansa Dala babu gammo. To amma ya shirya kinkimar wannan Dalar, ya dora a kansa, koda kuwa babu gammon babu gudu babu ja da baya, in sha Allahu ruwa ko iska babu mai hanashi aiwatar da shawarar da ya yanke shi da zuciyarsa ta sanya HAUWA’U CIKIN IYALIN SA.

Sai dai kuma ta ina zai fara? Abin nufi ta wane bangaren???

    Ta matar sa abar kaunar sa masoyiyar sa GIWAR SA MADINAH? Ko kuwa ta rigimammiyar uwar Hauwa wato INNA SAFIYYA? Wadda ta ci layar ko dan shugaban kasa bazata bawa auren miskiniyar ‘yar ta ba don kada a tozarta mata ita sabida nakasarta?

     Ko kuwa ta bangaren mahaifin sa ABBA PROF.? Wanda tun asali alamu sun nuna ko zancen su baya so? Koko ta bangaren MAMANSA Mai Shari’ah Haj. Maimunatu???

     Kowanne daya daga cikin wandannan bangarorin ya dosa da hukuncin da ya yanke, ya san babu sauki wai ciwon arne. 

    Dr. Sarham ya aje numfashi, ya muskuta ya gyara kwanciyar sa ya koma rigingine, daga kwancen da yake yana hararo jan aikin dake gabansa. Ya san da gaske ya daukowa kansa DUTSEN DALA da na GWAURON DUTSE kai har ma da duka KOFOFIN KANO da BADALOLINTA bakidaya ya kinkima ya dora a kan sa. 

    Shin ko wa zai taya Dr. Sarham saukewa kansa nauyin wannan kuduri da ya dauka? Ni dai na san mutum mai kyakkyawar zuciya da kyakkyawar manufa a kullum mai nasara ne akan duk abinda yasa gaba. Kuma kamar yadda Hauwa tace ne shi din mutum ne mai ‘abstract reasoning’ komai cudewar lamari baya kasa warware abinsa. Don haka ina yiwa Dr. sarham fatan nasara da fatan alkhairi da taya shi fafutukar kaiwa ga cikar kudirinsa na alkhairi.

    

    

    

    MURFIN LITTAFI NA BIYU

    

    Mu biyo “HAUWA KULU-AKA- (‘YAR CIKIN BADALA)” a littafi na uku, Ubangiji dai yayi alkawarin cewa “cikin dukkan tsanani akwai sauki”. Sannan a cikin biyayyar iyaye akwai babbar NASARA. Hauwa kuma tuntuni tayi aniyar yiwa Inna biyayya ta danne kwadayinta na dukkan dan adam, wato ta hakura da rayuwar ‘marital life’ da ‘motherhood’ daga yau har karshen rayuwarta domin yin biyayya ga Inna.

    

    Shin kwadayin Hauwa na can karkashin zuciya zai tabbata? (Hauwa za ta samu damar yin marital life da motherhood kamar kowacce diya macen data kai munzali duk da lalurar makantarta? Ko kuwa zata dauwama ne a gaban Innarta tana kaf-kaf da abarta yadda Innar ta zabar mata tayi rayuwa???

     Shin HAUWA-KULU zata yi rayuwar aure da tara iyali a yadda Ubangiji ke son ganin ta ko kuwa zata dauwama bisa tsarin Innarta?  

    

Ina labarin Malam Bilyaminu har yanzu ne? A mace yake ko a raye?

Amsoshin duka wadannan tambayoyin in sha Allahu suna cikin littafin HAUWA-KULU kashi na uku. 

    

    

            

    

          Taku har abada;

     Sumayyah Abdulkadir (Takori).

            2/09/2023 

07030137870

(WHTSAPP ONLY)





Post a Comment

0 Comments