TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 19

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_


_A rayuwar kowane mutum yanada wahala yamanta da mutane masu tarin d'inbin alkhairi acikin ta da kuma alamurransa😍 to nima kamar hakane awurina, dukkanin mataki da cigaban da zan samu arayuwata bazan tab'a mantawa da irin k'warin guiwar da akoda yaushe nake samu daga wajen ki ba *AUNTY MAIJIDDA MUSA* fatana Allah ya dawwamar da amincinsa acikin rayuwar aurenki, yaraya maki zuriarki ya albarkaceta sannan yayi maku kyakkyawan sakamako da aljannah fiddausi bi gairi hisabin wala ik'abin👏🏻ina mik'o gaisuwa mai tarin yawa da kuma jinjinata agareki Allah yabar tare🤝 much luv aunty mj😍_


💎Page_____19💎



 Shikenan Ummi bari nafara harhad'a kayanmu kafin su dawo, sister faraaha ce tashigo cikin d'akin fuskarta ba yabo ba fallasa cikin sauri Billy ta ajiye blanket d'in dake hannunta tana ninkewa ta rungume faraaha


"Congratulate me sis anbamu sallama yau zanje gida, missing home  sosai wlh" murmushi tayi had'e da rik'o hannunta suka dawo inda Ummi take "Ummi kinga lil sis d'in Yaya Mahmud sai farinciki takeyi tunda tayi nasarar tirsasani anbata sallama" tana kallon Billy take maganar, zaro ido Ummi tayi


"Faraaha dama had'a baki kukayi aka sallameta lokaci beyi"


"A'a naga mutuniyar tawa tagaji da zaman kuma gashi result ne kad'ai zai zaunar daku na tsawon kwana biyu shiyasa kawai naga bari ayi hakan, inyaso bayan kwana biyun idan yafito saiku dawo saboda ina tsoron tayi mana absconding" tak'arasa maganar tana dariya, girgiza kai Ummi tayi tana murmushin irin wayon yaran zamani shine Bilkisu tayi mata kamar batasan da maganar ba hartana tambayar ko anbasu sallama, kai yara Allah dai ya shirya mana tafad'a cikin zuciya, kallon Billy faraaha tayi cikin damuwa tace


"Sisto bakida kirki k'irik'iri kike nunamun farincikin ki zaki tafi gida abunki batare da ko irin zakiyi missing d'ina ba" 


"Kai aunty faraaha zaman asibitinne babu dad'i ko kad'an kinga kuwa dole inyi farinciki da samun sallama kuma kema kinsan ko ban fad'a ba zanyi kewarki sosai"


"Hmmm kamar da gaske"


"Aikuwa dagaske nakeyi, Ummi aramun wayarki na copy number ta aciki don ta tabbatar" mik'amata wayar Ummi tayi tana fad'in


"Maza ki kwafa kibani ink'arasa azkar d'in kafin magrib tayi na manto da hisnil Muslim d'ina agida" da sauri ta fad'a mata digit d'in tayi copy akan wayar sannan tafita d'akin saboda akwai statement d'in da take son cikawa ita kuma tamik'awa Ummi wayar sannan taci gaba da shirya masu kayansu.


Cikin b'acin rai mom ta sauko k'asa tare da nufar d'akin papi saida tayi knocking sau uku sannan aka bata izinin shigowa, yanayin da sukaga tashigo ya tabbatar masu da akwai abunda yafaru, d'aure fuska sosai papi yayi sannan yayi mata nuni da tazauna akan kujerar dake acan gefen wardrobe, anyi kusan mintuna biyar yana kallonta kafin can yace da ita


"Lafiya kuwa"


"A'a papi maganar gaskiya da akwai matsala" tashi Mahmud dake zaune agefen hajiya kaka yayi daniyar fita papi dake k'ok'arin gyara zamansa akan gado don sauraren abunda tazo dashi yace masa ya koma ya zauna,


"Inajinki meke faruwa ne?"


"Papi nidai so nake kayiwa dadyn yarannan magana ya maido mani da yarana hannuna bana buk'atar suzauna tare dashi ab'ata masu tarbiya" ba papi ba hatta hajia kaka da Mahmud saida suka zaro idanu had'e da bud'e baki suna mamakin kalaman dake fita abakin mom, kallonta papi yayi yana dariyar Ikon Allah sannan yace


"Meye dalilinki da kuma hujjarki akan abunda kika fad'a" aikuwa kamar jira mom keyi tabud'e baki bakunya ta zayyane masu duk abunda Basmah tafad'a mata k'arya da gaskiya kumafa papi inba son ab'ata yara ba har rungume rungume sukeyi agaban yaran, ni dai..." Katseta yayi cikin b'acin rai "ubangiji Allah ya rabaki da wahala Hussaina, yanzu meye amfanin wud'annan maganganu da kike fad'a agaban yaronki?,"


"Saboda suma hujja papi.."


"Rufamun bakinki, tir da yawanki ai wannan ba hujja bace shirmene, atafi suna aikata hakan shin haramunne? Sannan wayakai idanun yaran harsukai ga gano abunda bai shafesu ba"


"Papi kafahimta mana, agaban su akeyi"


"Mtsssss..wannan shi ake kira da bakin wahala, duk da banda tabbas akan abunda kefa ruwa yallab'ai natabbata wlh k'aryane hakan bai faruba don yanda nalura da halin hajia Aisha da shikansa maigidan nasu bazasu tab'a aikata hakan ba wlh, wannan duk k'ullalliyar yaran tane da gurb'atawa tunani ta b'ata masu tarbiya" hajia kakace ke fad'ar wannan maganar cikin fushi tare da b'acin rai, Mahmud dake zaune ya sadda kansa k'asa tunda mom tafara magana yace


"Mom wlh kiyarda dani wannan magana ba haka takeba, taya Ummi tasamu aikata duk wud'annan abubuwa ita da kullum cikin aikin kulamaki da yaranki take itada ko yaushe tana hanyar zuwa asibiti wurin jinyar 'yarta, na tabbata wannan matsalar Basmah ce tahaifar da ita, to bari kiji gaskiya mom ita kanta Basmah a asibiti take kwana, saida safe idan naje ita kuma saita jegida tayi wanka taci abinci lokacin Ummi tagama gyara komai sai sudawo tare kuma lokacin dady baya gida shin taya za'ayi tasan abunda yake faruwa, kiyi tunanin wannan maganar mom"


"Rufamun bakinka dama nasan kai bazaka yadda ba tunda ko yaushe bayanta kakebi tariga ta gama da kai da mahaifin naka" murmushin takaici papi yayi yana kallonta yace


"Tabbas muma d'in bamu yadda ba sannan kafin inrufe idona in bud'e inaso kibar d'akin nan shashashar banza da batasan ciwon kanta ba, inyaso muma d'in kice tagama damu kinji ko?"


Sumui sumui mom tabar falon zuciyarta na zafi da k'una akan rashin samun goyon bayan iyayenta aranta takai k'arshe akan cewa daga wannan karon bazata koma k'unsar bak'in cikin Aisha ba dolene bak'in yanayi ya juya akanta.


Tana fita papi ya kalli Mahmud dake kuka yace


"Kayi hak'uri kaima jarabawa ce Allah yayi maka da mahaifiya mai murd'ad'd'en hali kamar yanda muma ya jarabcemu da ita amatsayin 'ya" shafa kansa yayi tare da cigaba da lallashinsa har saida yaga yayi shiru sannan ya cigaba da cewa


"Dama Bilkisu bata da lafiya shine baka sanar damu ba kuma shima dadyn naku koda mukeyi magana dashi bai fad'a manaba abu har ankai ga kwanci asibiti gaskiya duk kanku baku kyautaba"


"Papi ni nazata tunda kunyi magana dashi yafad'a maku abunda kefaruwa" nan Mahmud ya zayyane masu duk abunda yafaru ranar da silar kwanciyar Bilkisu a asibiti, "Allah sarki Mahmud mahaifinka mutumne nagari, wlh gaba d'aya bai fad'a mana wannan maganarba amatsayin abunda yasa yace ummanka tayo gida, sab'anin da ya had'asu har takai ga sheganta masa 'ya'ya don banata bane shi kad'ai yafad'a mana, ya Allah kishirya mana wannan yarinya, gaskiya bata kyautaba ko kad'an kuma tayi kuskure sosai"


Shiru Mahmud yayi yana mamakin hali irin na mahaifinsa, tabbas duk hak'urinsa dole ya hukunta mom akan wannan abunda tayi masa,


Sunjima suna tattaunawa akan matsalolin mom tare da baiwa Mahmud shawarwarin yanda zai dinga lurar da ita, daga k'arshe papi ya tabbatarwa da Mahmud insha Allah gobe zasuzo suduba Bilkisu da jiki kuma yabawa dady hak'uri kafin suzo yafad'a masa basusun cewa Bilkisu batada lpy ba sai yau daya fad'a masu, sannan kafin sutafi ya kira Basmah da Batool yayi masu fad'a sosai tare da nuna masu suso 'yan uwansu domin ita duniya batada tabbas, babu yanda mom batayi ba don tasake keb'ewa da Basmah amma da hajia kaka talura da haka ta kasa ta tsare afalo har saida taga sunbar gidan sannan itama tanufi hanyar bedroom d'in papi ta d'ibo masa ruwa abuta saboda sallar magrib data gabato kuma dama shi bayason yin arwala a toilet yafiso yayi ta awaje hakan yafi sama masa natsuwa,


Ana kiraye kirayen sallar magrib suka isa asibiti don haka Ummi tace yaje yayo sallah kafin nan suma sunyi sannan sai suwuce, 


Bayan sun iso gida yana yin parking da mota Billy tafito aguje tana fad'in.


"Home sweet home, missing u so much" tana maganar tana bud'e hannayenta asama tare da shak'ar iskan dake kad'awa, hasken fitillun dake zagaye da bangon gidan su suka taimakawa Mahmud wajen hango farincikin dake shimfid'e a fuskarta, dariya yayi tare da fad'in


"She's always different, dt's my lil sister" 


Gaba d'ayansu part d'in Ummi suka nufa agajiye kowanensu yazube akan kujera ita kuma direct d'akinta ta nufa cikin zumud'i tana shiga taci karo da manyan akwatuna guda biyu wanda kemata nuni da anan 'yan uwanta suke zaune, ko kad'an ranta bai b'aciba ta wuce toilet ta watso ruwa, wardrobe d'in kayanta tabud'a suna nan kamar yanda tabarsu agyare, taciro wata doguwar riga ta material amma cotton anyi mata d'inkin nan da ake kira A-shape ko kad'an yadin bayada nauyi kalar baby pink da touch d'in royal blue ta saka ajikinta sannan takoma falo anan inda tabarsu suna nan zaune abunsu kowa na harkar gabanshi, ita kuma Ummi tana kitchen tana tanadar masu abunda zasuci marar nauyi, Bilal da bassam kuwa tuni har sunyi bacci,


Kitchen d'in itama tanufa ta samu Ummi tasa dafuwar macaroni tana hik'ar arish, hannu ta mik'a da niyar karb'a Ummi tace


"A'a Bilkisu jeki kihuta"


"Kai Ummi wane irin hutu zanyi tunda nasamu sauki" 


"Allah dai yak'ara sauk'i, ungo to bari nad'ora dafuwar k'wai kafin ki k'arasa fek'ewar"


Billy bata jima da wucewa kitchen ba itama Batool tabi bayanta, tana shiga tace 


"Ummi sannu da aiki, me za'a rik'a?" Saida Ummi tayi murmushin jin dad'i sannan tace


"Ai da kinbarshi batool kije kihuta, kuda kukasha tafiya"


"Lahhh bakomai wlh idan har Billy da batada lafiya zata iya aiki to mezai hana nima inyi Ummi?"


"Kai yayya Batool nifa na warke don bana tunanin zaki fini lafiya yanzu" dariya Ummi tayi


"To nidai bana son musu ungo nan kihad'a waccan stew d'in dana d'ora yanzu ga mai nan da nik'akkin kayan miya bari ni naje nawatso ruwa 'ya'yan albarka" har Ummi takusan fita Batool ta Sosa k'eyar kanta had'e da d'an yatsina fuska tace


"Ummi a gaskiya ban iyaba" shiru ummi tayi fad'an lokaci tana mamakin yanda kamar Batool ace bata iya had'a stew ba, murmushi tayi sannan tadawo cikin natsuwa ta dinga nunawa Batool yanda ake had'awa har suka kammala cike da jin kunya tayiwa Ummi godiya, shafa kanta tayi tace ba damuwa kijira ta ida nina sai ki kwashe a cikin waccan warmer d'in ke kuma Bilkisu kitsane macaronin da arish shikuma kwan kiyankashi shape d'in ball kamar yanda kika yiwa arish d'in saiki saka a wannan bowl d'in ku gyara kitchen d'in kafin nafito,


Kallon Basmah dake latsar waya Mahmud yayi sannan yace


"Ke bazaki tashi kije kuyi aikin ba"


"Bacci nakeji" 


"Ohh! Bacci kikeji amma kike latsar waya, zaki tashi kitafine kosai na mammakeki awurin?" Cikin b'acin rai ta tashi tanufi kitchen d'in har lokacin tana latsar wayarta wanda hakan yasa da kad'an ta bangaje Ummi dake k'ok'arin fitowa, jabaya tayi Ummi ta wuce abunta batare da ko kallonta tayi ba, mere baki tayi sannan ta lek'a kitchen d'in 


"Hi gusz abincin ya nina ne?" Kad'a mata kai Billy tayi tana murmushin da baikai ciki ba tace "eh yayya Basmah" ita kuwa Batool ko kallonta batayi ba taci gaba da aikin gabanta,


"Ke Billy ki kawomun nawa afalo don yunwa nakeji" tana gama fad'a tawuce abinta


To Billy tace tare da d'aukar d'aya daga cikin plates d'in dake sagale ajikin kitchenware Batool tayi saurin rik'e mata hannu


"Stop it Billy wlh Allah baza'a zuba matashi ba sai Ummi tafito, wannan ai rainin hankali ne..



Post a Comment

0 Comments