TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 21

👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_

 

_Gaisuwa mai tarin yawa tare da fatar alkhairi marar misaltuwa agareku 'yan group d'in *BILLY S FARI NVLS GROUP* u people are always made me happy especially you guyz AFRAH, MAMAN ABBULKHAIR, AISHA ABUBAKAR, SADIYA SANEE, MMN HANAN, MMN IHSAN dama sauran wud'an da ban ambata ba sincerely inajin dad'in yanda kuke zuba mun ruwan comment domin hakan na k'aramin k'warin guiwa sosai, ngd ubangiji Allah yabaku farinciki mai d'orewa duniya da lahira👏🏻 luv u more than how word can say❤stay bless🤝_


💎Page_____21💎


 Tun tana kukan a hankali har takoma yinsa sosai tana fad'in "yaya nak'oshi", ko kad'an kukanta bai dame saba balle ya saurari abunda take fad'a sai ma cigaba da dannar wayarsa da yakeyi, saida ta cinye abincin nan tas saiga kiran mom awaya ya shigo a wayarsa, murmushi yayi had'e da d'aga wayar,


"Mom bakiyi bacci bane?"


"Kaji shashanci! Taya zan iya bacci 'yatah najin yunwa bataci abinci komai ba, kasan Allah kashiga taitayinka don naga baka damu da 'yan uwan kaba" sai da ya harareta ta gefen ido sannan ya danna hands free d'in wayar yana dariyar k'eta,


"Tuba nakeyi mom, ki kwantar da hankalinki ganinan tare da 'yarki nabata abinci kuma saida na tabbatar taci ta k'oshi, yanzu haka bakiga yanda cikinta yayi ba sai nishin kwad'd'i takeyi, ki kwanta kiyi baccinki cikin farinciki mom zan kula da 'yan uwana yanda ya kamata"


"Katabbata?"


"Sosai kuwa mom, sufa 'YAN UWANA NE taya za'ayi inbari su tozarta hakan bazai tab'a yuyuwaba min sha Allah"


"Yawwa my son haka nake son ji Allah yayi maka albarka"


"Amin mom seda safe" ya kashe wayar had'e da kallon gefen da Basmah take zaune har lokacin hawaye na zubar mata a idanuwa, baran ma dataji muryar mom da tasan zai shafa mata lafiya wlh anan zata k'arya tashi kuma tafad'iwa mom muguntar da yayi mata nasata cinye cikin plate d'in abinci da sanyin sa, 


"Maza ki d'auke plate d'in kikai kitchen and make sure gobe da sassafe na iskoki kitchen kinfara had'a breakfast kafin Ummi tafito kuma idan kin isa kikira mom kifad'a mata wlh in tattakaki agidan nan wawiya kawai" yajuya yabar falon yana mai addu'ar Allah ya shirya masa 'yar uwarsa dake nema tazame masu trouble maker acikin gida, yana fita ta turo baki had'e dasa hannuwa tagoge hawayen da suka zubo mata tana fad'in


"Wlh Allah ya isana, mugu kawai kuma bazan d'auke plate d'inba" had'e da shuresa gefe, dariya Batool dake lab'e a k'ofar d'akinsu tana sauraren duk abunda ke faruwa tayi sannan ta gyara muryarta tayanda zatayi irin ta yaya Mahmud tace


"Eyye..Kikace me?" Da sauri Basmah ta d'auke plate d'in takai kitchen tafito tana waige waigen inda zata hangosa tunda tasan yafita, shin kodai yaya Mahmud na ajikin k'ofa  ya lab'e da gudu tanufi d'akinsu don kar inyana kusa ya shigo ya mammaketa garin haka tayi karo da kujera tafad'i twuiii kakeji kamar ba jikin mutumba, dariya Batool ta tintsire da ita had'e da fitowa daga mab'uyarta rik'e da ciki tana cewa


"Gwai Allah yayya Basmah, bake rashin kunya ba? ai maganinki kenan!" Ta k'arasa maganar tanaci gaba da dariyarta hadda hawaye, matse fuska Basmah tayi kamar bataji zafin fad'uwar ba wai ita aunty bata son rainin Batool tace


"O.o.o ki kwantar da hankalinki bazan fad'awa kowa ba babu wanda yaganeki sai ni hattafa yaya Mahmud baiga komai ba don yariga daya tafiyarsa, muryar sama da kikaji nice nan na kwaikwaya, ba waike irin big girl d'in nan ba hadda wani yimasa Allah ya isa kuma bazaki d'auke plate d'in ba?, shine nikuma nayi maki haka,kuma sai nafad'a masa abunda kikace, wato yayan ne mugu ko? Tabbas saina fad'a masa" cikin fushi da b'acin rai had'i da rad'ad'in da takeji tayo kan Batool, da gudu tashige d'aki tana biye da ita idan tayi nan tayi can tana dariya, kan gado ta haye ta b'uya a bayan Billy da hayaniyarsu ta tada ita zaune a tsakiyar gado tana murzar idanu, kan gadon tahau tare da ture Billy gefe tayi kanta da duka, pillow ta dinga karawa ga duk naushin da zata kawo mata tana dariya, acan cikin pillow tasake lank'washe muryarta zuwa ta yqyq Mahmud tace


"Shin wai ke bazaki natsu bane Basmah?" da sauri taja baya da kad'an tafad'o daga kan gadon saboda yanda take tsoronsa, ba Basmah kad'ai ba duk wanda zaiji muryar zai d'auki Mahmud ne dama can muryar batool nashige da tasa sosai banbancin kawai tata tafi tasa sirantaka saboda ita macece shi kuma namiji, to idan ta d'an kaurara muryarta sai kaji tafito sak irin tasa, yanda ta razana ya k'arasa Batool dariya ita kuma ta gano still itace ba yaya Mahmud d'inba nan ta d'auki pillow itama tanata dukanta dashi  tun tana dariya har sai da tafara kuka sannan ta k'yaleta, tana nishi d'aya bayan d'aya tace "gobema kya k'arya", Cikin kuka Batool tace


"Muguwa kawai, wlh Allah ya isana banyafe ba, matsoraciyar banza" sake buga mata pillow tayi


"Wa kike cewa muguwa Allah ya isa?"


"Dake nake ai kamatu dini tadana" Billy dake zaune a k'asan gado tana kallonsu cikin yanayin baccin da takeji ta d'anyi murmushi gefen baki had'e da cewa


"Wlh yayya Basmah kundai shiga hakk'ina.." Kafin tarufe baki Batool tace


"Kema Allah ya idan maki" wata irin muguwar harara Basmah ta watsa mata sannan tajuyo tana kallon Billy


"Mtsss yo ai sai kizo kidakeni" sannan ta wuce toilet tana d'ingisa k'afa, gyara gadon daya cukuikuye Batool ta sakeyi sannan ta maido hankalinta ga Billy dake zaune tana gyan gyad'i tayi murmushi


"Ina ruwan hajia kaka, wannan da nikeyi da nace nayo gado kam sosai, ke Billy we're sorry taso ki kwanta" ganin kamar baccin yaci k'arfinta yasa tarik'ota ta kwantar da ita a tsakiyar gadon sannan itama ta koma bayanta takwanta, saida ta watso ruwa sosai ajikinta sannan tafito ta canza rigar bacci itama tahaye gadon ta kwanta daidai filin dake akwai a gaba lokacin kusan k'arfe d'aya da kwata 1:15am na dare


Duk da kasancewar basu kwanta da wuri ba jakan baisa Basmah ta manta da gargad'in da yaya Mahmud yayi mata ba, tana ida sallar asuba tanufi kitchen ita kuwa Batool takoma kan gado abunta ta kwanta, Billy kuma tazauna tana karanta azkar d'in safiya tana idawa tahau gyaran d'akin, kan gadon tahau tana fad'in


"Yayya Batool kitashi in gyara gadon kinga garin yafara haske"


"Ehmmmm..don Allah Billy ki kwanta kihuta mana" ta k'arasa maganar had'e da jawo Billy ta kwantar da ita "yawwa Billy i baccinki" tafad'a cikin muryar dake nuna alamun bacci takeji sosai, cikin jin dad'i da farincikin yau gata ga 'yar uwarta tana nuna mata soyayya tace


"Yayya Basmah Ummi fa batason baccin nan na bayan sallar asuba, shiya bana komawa idan naga azkar sai in cigaba da 'yan gyare-gyare da d'ora breakfast har sai rana tafito,


"Karki damu yau yayya basmah zata had'a mana breakfast"


"To bari naje nayi share-share da mopping idan yaso inkin tashi kya gyara gadon" k'ok'arin saukowa tayi daga gadon ta rik'e mata hannu "help me Billy in tashi in rik'a maki aikin" murmushi tayi had'e da jawo hannunta ita kuma ta biyota a hankali ta d'ora kanta akafad'arta, 


"Oh my God! Wake up yayya Batool kafin Ummi tashigo ta haumu da fad'a" d'ago fuskarta tayi tana kallon tata tace


"Billy am so sorry da yanda nayi treating d'inku a baya, na matuk'ar gano hakan ba daidai bane, nafahimci ku 'YAN UWANA NE kuma ina matuk'ar sonku" yatsanta tad'ora akan lab'b'anta


"Shiiiii...Yayya Batool! Babu komai a tsakaninmu yanzu, Allah ya gafarta mana zunubbanmu, dama kullum fatana shine naga 'yan uwana na sona kamar yanda nake sonsu" rungumeta tayi had'e da cewa


"Nagode sosai, amma zakiyi hak'uri da halin yayya Basmah ko? Bazaki d'auki fushi da itaba akan abubuwan da takeyi ko? Na d'aukar maki alk'awarin cewa da sannu itama zata gyara halinta in Allah ya yarda, zamu zamo kamar yanda yaya Mahmud keso muzama wato tsintsiya mad'aurinki d'aya"


"Sosai kuwa, Allah ya yadda" breaking hug d'in sukayi sannan suka hau gyara gadon, bayan sun ida suka cigaba da sauran gyare-gyaren gidan. 


Koda Basmah tashiga kitchen tsaye tayi takasa gano abinda ya kamata tad'ora kamar ance ta juya gefen fridge d'in dake bakin k'ofar shigowa kitchen d'in ta hango wata takarda mak'ale ajikin bango wacce ko baka tambaya ba kasan time table d'in abunda yakamata adinga cine kullum ajikinta saboda komai na Ummi a tsare yake kuma tana aiki da planning, mere baki tayi had'e da duba takardar taga yau Wednesday za'aci yam balls da kunun gyad'a da kuma farfesun kifi, rik'e k'ugu tayi had'e da cewa "Tab wlh akwai aiki kuwa breakfast d'in har sai anyi kusan girki kala uku sai kace restaurant" itakam gaskiya bata iya komai daga cikin su ba, kuma bazata iya tambayar Billy ba tare nata, don haka tanemi tukwanenta guda uku duk ta cikasu da ruwa ta d'ora akan gas tasamu wuri abunta tazauna, k'arfe shidda da rabi sai ga yaya Mahmud ya shigo, kitchen d'in yafara lek'awa ya hango Basmah zaune ta k'urawa tukanen ido kai kace wani abun kirki ta d'ora take jiran ya nina, gyaran murya yayi da sauri tamik'e tsaye,


"Morning yaya Mahmud" k'ura mata idanu yayi yana son gano wani abu ganin yanda tayi fik'i-fik'i da idanuwa tana wani nonnoce kai k'asa yace


"Lpy klw ai nazata zan iskoki kina vaccine"


"A'a gashima har na d'ora"


"Gud girl" yafad'a sannan yabar wajen, murmushi tayi had'e da cewa


"Hmmm gud girl ko? zako kuga gud girl wlh donni ba abunda na iya acikin abunda za'ayi breakfast dashi yau"


Ummice tsaye agaban wardrobe d'in dake lak'e ajikin bangon d'akin dady tana gyara masa kayansa bacin sun gamo sallar asuba shikuma yana cikeciken wasu document a laptop d'insa, gyaran murya tayi lokacin da take ninke wata T-shirt tace


"Dadyn yara ina son muyi wata magana idan har ba damuwa"


"To madam ina saurarenki," yafad'a har lokacin hankalinsa na akan aikin da yakeyi


"Da zaka bani aron wasu mintoto daga cikin lokacinka da zaifi, amma idan aikin da kakeyi urgent ne sai inbari sai wani lokacin" saida yayi saving rubutun da yakeyi a laptop d'in sannan ya rufe yajuyo yana kallonta,


"Gani ranki shidad'e ba lokacina kad'ai ba har ni kaina gashi kinsamu, kiyi maganar ki ina sauraren ki natabbata zanyi maki kyakkyawar fahimta aciki"


"Godiya nakeyi, Allah yak'ara d'aukaka mana kai" shiru tad'anyi sannan tace dama akan maganar hajia Hussaina ne, duk daba hurumina bane ina so inbaka hak'uri da kaje kayo bikon matarka don Allah, ka tausayawa yarannan ko donsu kaje kadawo da ita, bai kamata ace cikakken magidanci irinkaba ace yasamu tauyuwar ladarsa tahanyar rashin d'ayar matarsa akusa dashi ba, kayi hak'uri shi Allah yana son mutane masu hak'uri da kuma kyautatawa" cike da mamakin kyakkyawar zuciya irin ta Aisha da kuma yanda ta iya sarrafa harshenta wajen furta kyakkyawan kalaman da zasu lank'wasa zuciyar mutum tayi sanyi yace


"Aisha me yarannan suka rasa da bakya yimasu"


"Soyayya mana irin ta uwa da d'a wacce duk abunda zanci basu duniya bazan iya basu itaba" yasan halinta sosai idan yabiye mata yanzune zata sanyawa zuciyarsa raunin k'wak'k'waran adadin hukuncin data d'ibarwa mom don haka yace


"Shikenan zanyi tunani insha Allah"


"A'a dadyn...."


"Shiiiii....no more word again, kibarshi ahakan tunda ni nace zanyi tunani to zanyin kinji ko?"


Da haka tabaro part d'in nasa zuciyarta cike da fatar Allah yasa yahakura kenan...



_Tofah!🤔 koya za'a kwashe da Basmah dake kitchen tana had'a breakfast😋😋 aunty maijidda da aunty fareeda m Abbas ina gayyatarku wajen cin breakfast d'in Basmah's delicious💃🏻💃🏻💃🏻😃_


 

Post a Comment

0 Comments