TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 12

 👭❤ *'YAN UWA NA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____12💎



 Saida ta d'auke Bassam dake saman jikinsa yana duka kafin ta d'agosa yana kuka, lallashin tashiga yi had'e da kakka b'e masa jiki, a hankali tad'ago kanta tana kallon Bassam dake faman nishi sai kace wanda yayi wasan tsere,


"Bassam don me zaka yiwa d'an uwanka wannan duka, baka ganin kafishi girma, ko kana son kaga yaji ciwo ne, haba! Kudinga tausayin da k'asa gareku don Allah"


Hannunsa Basmah tazo taja tana qunquni k'asa k'asa ita marar kunya, girgiza kai Ummi tayi tare da cewa 


"Allah ya shirya manaku" hannu tasa ta d'auki Bilal dake kuka sannan tajuyo da niyar barin wajen, juyowar da zatayi taji Billy tasaki wata irin muguwar k'arar data sa both ya Mahmud da dady fitowa aguje saboda tashin hankali, kwance suka hango Billy a some kanta na zubar da jini a sanadiyar hankad'eta gefe da mom tayi lokacin da ta iskota bisa jikin Batool tana duka shine tafad'a akan d'aya daga cikin kujerun dake harabar gidan da yake irin na stones ne sai kanta ya bugu, speechless mom tazama  takasa karasawa wajen wasu zafafan hawaye na  zubo mata a idanu yayinda Mahmud ya d'auki Billy idanunsa ko gani basayi tsabar takaici shima hawayen ne ke zubar masa, bakin gate ya nufa da nufin samun abun hawa sai ga dady yafito da mota suka nufi asibiti, sosai jini ya zuba akan Billy don haka aka nemi a k'ara mata jini, nan take Mahmud yaje aka aunasa jininsu yazo d'aya, dafarko dady yaso a ibi jininsa kasan cewar Mahmud bai dad'e da tashi ciwo ba amma shi yak'i amincewa da haka, sai da likitoci suka tabbatarwa da dady babu wata matsala don and'ebi jininsa tunda ya samu sauk'i sannan hankalinsa ya kwanta, dady na ganin komai ya daidaita a asibiti ya d'auki motarsa ya kama hanyar gida, yana isa ko parking mai kyau bai yiba ya nufi part d'in mom, yana shiga ya taradda ita tana kallon wani season film (king of the heart) hankalinta kwance tamkar bata aikata komai ba, yaran tane kad'ai suka d'an shiga damuwar abun da yafaru don dukkanin su zaune suke kamar ruwa ya cisu, cikin kakkausar muryar da mom batasan dady da ita ba taji yace


"Enough hajia Hussaina, nace enough is enough, basai kin kashe mani 'yaba zan gane bakya son jinina, ba sai kin nuna cewa Bilkisu ba 'yarki bace zan gane bakya da asara idan tamutu, Allah yasani ina matuk'ar son 'ya'yana gabaki d'ayan su, bazan iya jurewa cutuwar d'aya daga cikin suba matuk'ar ina raye, nayita k'ok'arin tausar zuciyata wajen ganin banyi abunda zaisa yaranki suji ba dad'i aransu amma ke kin kasa fahimtar haka har saida kika kaini bango, saboda haka kitafi gidan ku bana buk'atar ganin ki agidan nan, kin fita raina tun lokacin da ida nuwana sukaga yanda kika illata mani yarinya, kika raba tsakanin d'aya da biyu don haka kibar gidan nan kafin indawo, sannan karki kuskura kibar gidan nan da yaro ko d'aya"


"Kasha k'arya, wlh tunda kakoreni cikin gidanka to kamar ka kori yaran kane, ai 'ya'ya nane ba ubanda ya haifa mani su don haka ba ubanda ya isa ya hanani tafiya da abuna da kuma ke cewa naraba d'aya biyu to ina naga d'ayan balle narabata biyu, babu wanda baisan cewa Aisha bata haihuwa ba , amma tsabar muna furci tunda taga inayi shine taje ta samo wud'ancan shegun aka k'ak'a ba maka, da yake kai kuma anriga an wanke an baka ka tara kai ka amsa shine kake nema ka mai dasu d'aya da 'ya'yanka to hakan bazata sab'uba wallahi"


"Tir Hussaina! tir da halinki, karki kuskura kisake sheganta mani yara, maza ki fice mun daga gida Allah ya shiryeki"


"Mtsss aikin banza, ance..." Kafin ta rufe baki dady ya shak'e mata wuya had'e da matseta ajikin bango idanunsa sunyi jawur tamkar garwashi,


"Ki maimata abunda kike son fad'a in kin cika, am tired of ur stupidity" da gudu yaran suka fito d'akunansu jin kakarin da mom d'insu keyi suna bawa dady hak'uri amma yak'i sakinta, ganin haka yasa Basmah tarik'e k'afafunsa tana kuka,



"Don Allah dady kayi hak'uri, ka saketa dady zafa ta mutu" sai da yaji gaba d'ayansu sun fashe da kuka sannan ya jefar da mom gefe yabar d'akin ransa a b'ace yana mai da na sanin aurenta, da sauri suka nufi kanta Batool ta d'ebo ruwa suka bata, dak'yar take shan ruwan sannan ta koma takwanta,


"Mom kitashi kitafi, wlh bakiga yanda fuskar dady tayi ba kada ya dawo ya iskoki, kitafi mu zamu biyoki daga baya" Basmah ce kefad'ar haka cikin kuka, saida mom tad'an dawo hayyacinta sannan tafara had'a kayanta tana jin wutar tsanar Aisha tare da yaranta na dad'a ruruwa acikin zuciyarta.



Ummi kuwa tunda abun yafaru tashige d'aki tana kuka, ko kad'an bata zaci tsanar da mom keyi mata ba takai ga har ta iya cutar mata da yara ta hanyar zubar masu da jini, ga Bilal a gefenta shima sai faman kuka yakeyi wai


"Ummi ina aunty Billy, meya faru da itane?, Ummi akaini wajen ta" Jawosa tayi ajikinta ta rungume hawayen ta na d'iga akan fuskarsa,


"Kayi hak'uri, auntynka na asibiti ba tada lafiya"


"Me yasameta Ummi? Itama 'YAN UWA NA NE suka yimata duka? Ummi ni basu jimin ciwo ba, sune suka jimata ko kuma mom ce? Ummi me yasa basa son mune?"


"Ya isa haka! nafad'a maka cewa ba tada lafiya ne, kayi hak'uri yanzu zamuje wajen ta kaji"


Mik'ewa Ummi tayi ta d'auko mayafinta, hannun Bilal ta rik'e suka nufi kofar fita saiga dady ya shigo, ganin yanayin da yake ciki yasa ta koma ta cire mayafinta, fridge ta bud'e ta d'auko ruwa masu sanyi a gora ta tsiyaya masa ga cup ta mik'a masa, kasa karb'a yayi yana kallon yanda idanunta suka rine saboda kukan da tayi, Bilal ta tura bedroom sannan takai ruwan abakinsa, a hankali yake shan ruwan yana kallon idanuwanta dake k'ok'arin sake kawo ruwa, bayan ta janye ruwan abakinsa, cikin sanyin murya yace



"Kiyi hak'uri rabba'atul bai..." Kafin ya iyar ta rufe masa baki, 


"Ba komai dama Allah ya tsaro yau jinin Bilkisu sai ya fita saboda haka muyi hak'uri mu rungumi wannan qaddara Allah ya tsare gaba, saidai naji ba dad'i naji zafi sosai araina" rungumeta yayi tana kuka yana cigaba da bata hak'uri


"Nayi kuskure sosai arayuwata rabba'atul baiti! Wannan duk ni najawo dana kasa tantance wace irin mata yakamata in d'auko gidana gashi yanzu..."



"Shhh...kadena fad'ar haka, ya jikin ita Bilkisu?" 


"Da sauk'i amma tarasa jini saida aka d'ibi na yayanta aka saka mata, yanzu haka bacci takeyi"


"Haba alhaji! Saboda me za'a d'ibar masa jini bacin kasan bashida lpy so kakeyi ayi biyu babu ne?" Muryar Mahmud tajiyo daga bakin k'ofa yana fad'in 


"Saboda ni yayan tane kuma au 'YAN UWA NA NE!...."




Post a Comment

0 Comments