TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 7

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____7💎



    Part d'in Ummi dady ya nufa ransa duk ab'ace, ya rasa wace irin rayuwace mom take son ake yi a cikin gidan sa, ita ko kad'an bata fahimtar me ake cewa kishi da kishiya ta yiwa kalmomin mummunar fahimta ta yanda ba zata tab'a barin a zauna lafiya ba a cikin gidan. Har ya iso cikin falon Ummi yana wannan tunanin, Bilal ne ya rugo da gudu yana fad'in, 


"Oyoyo dady" Cabesa dady yayi tare da kissing forehead d'insa shima yana cewa,


"Oyoyo my Bilal kana lpy?"


Kai ya d'aga masa yana wasa da buttle d'in jallabiyarsa. Ummi kuwa dake cikin bedroom fitowarta wanka kenan ta jiyo muryar dady, agurguje ta shirya sannan ta bud'e bedside fridge d'inta ta d'auko gorar ruwan faro mai sanyi tare da cup ta nufo parlon fuskarta d'auke da murmushi, Bilal na ganin Ummi ta shigo ya sauka daga jikin dady tare da barin parlon aguje yana k'walawa Billy kira.


"Aunty Billy, aunty Billy kizo ga daddy"


Wani irin lafiyayyen murmushi dady yayi ganin Ummi ta nufo inda yake fuskarta d'auke da murmushin da ako yaushe ke haskaka masa zuciya,


A hankali ya bud'e mata hannayensa ta yiwa kanta  mazauni bisa ki'rjinsa shi kuma ya zagaye hannayensa abayanta, a lokaci guda suka lumshe idanuwansu suna jin wani sanyi da natsuwa na saukar masu acikin zuciya, sun jima a haka kafin can suyi breaking hugging d'in da suka yiwa juna, ruwan Ummi ta tsiyaya masa a cup sannan ta mik'a masa cike da girmamawa, karb'a yayi tare da had'owa da hannunta ya kai ruwan abakinsa yana sha yana kallonta a hankali har ruwan ya k'are. Ajiye cup d'in tayi tare da cewa.


"Barka da rana dadyn su B, ya gajiyar hanya?"


"Yawwa Rabba'atul baiti, gajiya takau tunda gani ga iyalina, Abu mafi burgewa na same su cikin k'oshin lafiya sai dai kash...da alama ko tunanina basa yi tunda kowacensu hankalinsu kwance yake kunyi wani fresh daku..!"


Da sauri Ummi d'ora yatsansa akan lips d'inta tace,


"Babu bukatar canzawar zuciyar dake samun kyakkyawar kulawa ga wanda ya ajiyeta, jarumtar da kake da ita wajen bamu kula da cire mana kewar rashinka atare damu bazata tab'a barin tunani yayi tasiri akan mu ba balle har yasa mucanza daga yanayin da kake k'ok'arin son ganin mu akoda yaushe, Idan kuwa hakan tafaru to tabbas rashin adalci da godewa jaruminmu ya tabbata akan mu"


"Rabba'atul baiti kenan! Bakya gajiya da kiran jarumtaka ga jaruminnan da ya kasa daidaita gidansa, Shin bakya tsoron ace wata rana ya samu rauni agabanki!?"


"Ko kad'an bata haufi akan haka idan kuma har ta faru zanyiwa jarumin nan nawa uzuri, in d'auka cewa Allah ya jarabce sane ko kuwa nice nakasa wajen iya wasashi shi yasa hakan ta faru bawai don ya gaza ba"


Murmushin jin dad'i dady yayi tare da yiwa Allah godiya daya mallaka masa Aisha a matsayin matarsa


"Tsarki ya tabbata ga ubangijin daya mallaka mani ma'abocin fitar da kyakkyawan murmushi a fuskarsa, dukkanin murmushin da zaka yi yakan k'ara mini k'warin guiwa da kuma dalilan da zasu k'ara mani sonka da k'aunar ka tare da zama a cikin gidan ka cikin ko wane irin yanayi"


Yayi murmushi tare da cewa "Idan ko haka ne zan kasance mai k'ara yalwar murmushi na don intabbatar kin soni fiye da adadin numfashinki da nawa"


Sosai dady ya samu natsuwa da farin cikin da suka nemi kwace masa a part d'in mom, fira take yi masa wacce kesa idan har zai iya mantawa da kansa saboda tsananin dad'inta to tabbas zai manta dashi, 


Billy ce ta shigo bayan ta biye da Bilal aguje yana dariya ya yi saurin b'uya bayan dady, Billy naganin dady tayi tsaye cak had'e da duk'ar da kai k'asa,


"Dady ina wuni"


"Lpy klw Bilkisu ya aka yi naga kin biyo k'anin naki ko laifi yayi ne?" 


"Eh dady wai cemun yayi..." Bilal na dariya ya katseta yana fad'in.


"Dady wai don d'ai nace mata Billy Japanese yanda yaya mahmud kecewa shinefa take son dukana"


Gaba d'aya dady da Ummi sukasa dariya,


"Haba Bilkisu d'an wannan abun shine ya kai ayi duka akansa...Bilal yama ake cewa.. Billy Japanese  ko?" kukan shagwab'a ta fara yi tana bubbuga k'afa, A hankali ummi ta zagayo bayan dady ta damk'o hannun Bilal tana cewa.


"Zo gashi Bilkisu narik'e makishi tunda dadynku yayi siding d'insa"


"Wayyo ammi ki cikani da zafi zata yimun"


"Ban fad'a maka kadena cemata haka ba? Yau saika gane kuskurenka tunda bakaji"


"Ummi da wasa fa nake yi mata ko aunty Billy na?"


Saida ta hararesa sannan tace


"Eh Ummi, amma kice kar ya sake"


"Aww ni zaki bawa kunya? Shikenan zaki sameni ne"


Dariya suka yi harda daddy dake kallon su, abinda sam yaran Mom basa yi wato wasa da dariya ga junansu sai dai son girma kamar su suka yi kansu....



   *Assalamu alaikum 'yan uwa da abokan arziki, ina muku fatan alkairi a duk inda kuke. Ayi min afuwa na jina kwana biyu shiru da aka yi hakan ya samu asali ne daga wayar, yanzu ma zakuji ni shiru sai yadda hali yayi sabida taki yin dai-dai ko nayi typing dana bud'e data zai goge ayi min afuwa see you next insha Allah na gode....*😘




Post a Comment

0 Comments