TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Zazzafan so page 18

 📄 *18*





Ahankali yayi sallama, mama ta amsa tana shirin mik'ewa ta karb'i jakar shi, taga ya nufi hanyar d'akin shi, tayi mamakin hakan.

Baya shiga d'akin shi daga dawowarshi, sai dai idan suna fushi da juna..

Ta Kalli yaran hankalinsu na kan kallo. Ta mik'e a sanyaye ta bishi.

Da sallama ta shiga, yana zaune akan gadonshi ya zubawa carpet d'in d'akin ido.

Ahankali ta nemi guri kusa da shi ta zauna.

"Sannu da zuwa"

Bai mata magana ba kuma bai d'ago ba.

Ta d'an sha jinin jikinta.

Ta d'an yi shiru, Mintuna kamar biyu sai tayi tunanin ta kawo masa ruwa.

Ta mik'e kenan ta fara tafiya taji ya kirata a hankali.

"Amina!!

Ta juyo ta dawo ta zauna wajen da take da.

"Me yasa kakai min haka?

Mamaki ne ya cika ta har yasa ta bud'a baki tace 

"Menayi abban..

Ya tare ta cikin b'acin rai.

"Ok me kikayi kike tambayata koh? To 

zaki fahimta idan na d'auki mummunan mataki akanku!!

😳 

Subhaanallah ta fad'a a hankali.

Sannan ta kwantar da murya,

Haba Abban Hafsah, don Allah kayi hak'uri, Allah ya wuci zuciyarka."

"Hmm dole ki ce haka mana, amma fa kin bani mamaki wallahi.."

"Please kayi hak'uri don Allah, ka fad'amin Meyake faruwa?

"Hum"

Kawai yace.

Sai kuma yayi wani tunani.

'Ya lura ta kasa sanin meye laifinta, shi kuma ba shi da lokacin b'atawa wajen zaman fad'amata'

Don haka yace:

"Sai ki kirata tunda ai da sanin ki takeyin komai."

Ba zata ce bata fahimci da wa yake ba don tasan da 'Hafsah yake'

Ta mik'e cikin azama ta nufi d'akin Hafsah, abinda ya so firgita ta,

'waya ta ganta tana yi.

Ta Kai mata duka, ta sami wayar ta fad'i ak'asa.

Hafsah ta juyo a razane,

Maman ta watsa mata harara sannan tace,

"Sai ki taso abbanku na nemanki"

Hafsah ta razana da jin kiran.

Tuni ita maman ta fice.

Ko hijab bata sa ba itama ta nufi d'akin Abban.

Tayi sallama ta zauna.

Bata ga fuskar gaida shi ba.

"Ke waye ya baki waya??

Tambayar taso ta ruguza kanta kamar saukar aradu haka taji tambayar.

"Da ke nake"

Abban ya fad'a yana nuna ta da yatsanshi.

Hawaye ne ya fara biyo kankuncinta.

Shikenan yau ta kad'e. wacce k'addara ce ke neman afka mata Ayau.

"Zaki yi min magana ko kuwa sai nayi ball da ke a wajen nan."

Abban ya fad'a lokacin da yake kawo mata wani bahagon duka da hannunshi.

Mama tayi azamar tare hannun nashi. Abinda ya hana dukan sauka akan fuskar Hafsah kenan. Don la shakka daya sauka da babu abinda zai hana hak'oranta zubewa.😳😂

Abba ya juyo a fusace, yana huci b'acin ranshi ya nunku, ya kalleta fuskarshi cike da b'acin rai..

👏🏼👏🏼👏🏼

*Am sorry kuyi haquri da wannan*

[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥

*ZAZZAFAN SO*

(Guba ne)

*A broken* 

*heart story* 

  💔💔



Story and writing by:

*Karima Tijjani Mansur* 

*(Hajeeyah Kareemerh)*

*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.*

😘😘😘😘😘😘

*Kai jama,a, ni mai zance da masoya wannan novel ne??*🤔🤔

*Sai dai in gode muku kawai*👌🏻

*INA GODIYA DA ALFAHARI DAKU INA MUKU FATAN ALKHAIRI.*

*KARIMA NAJI DAKU😇*

*ZAZZAFAN So NOVEL GROUP:*

🌹 ummu al,amen, Adam's Fudiyya, Maman affan, Ramcy, Hajara ayuba, Sarauniya Bilkisu.👏🏼👏🏼👏🏼

*UNIQUE IN YOUR LOVE HEART GROUP:*

🌹 Zeena Khalid, pure baby and the whole members👏🏼

*JIDDA TIJJANI NOVEL GROUP:*

🌹Deejah, Lawisa tanaskha, Binta musa salisu (Mamana), Maman Hanan, Nana Hauwa,u, juwaira lukman. And also Aysha Tukur (Maman Teemah and Ahmad)👏🏼👏🏼

*RAYUWAR SUMAYYA NOVEL GROUP:*

🌹 ummu muhd, bintu muhd, Habiba abdul k'adir.

*SIRRIN MU:*

🌹 Ummu hibban 'yar baba, zaujatu muhibbuha, Mrs naseer.👏🏼

*NOVEL ZAFAFA:*

🌹Mr Otu, sumyhala2017.👏🏼

*MATAN AURE NOVELS:*

🌹SUA, Zeenah Khalid, pure baybee. 👏🏼

*NIDA K'AWATA FANS:*

🌹 Nadiya sadou, S ubanduma, maman umar, Aisha ya,u.👏🏼

*KUNDIN NOVEL GROUP:*

🌹Zulaihart, Maman Hafsah, Khadeejah.👏🏼

*TAURARUWAR MACE GROUP :*

🌹Sumayya hadi and Mami boy.👏🏼

💘💘💘💘💘💖💖💖💖💖

*Am totally in love with you.. Kun gane ai*😊👏🏼👏🏼👏🏼




Post a Comment

0 Comments