TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Zazzafan so page 20

📄 *20*




*Washe gari* da asuba, abban ne da kanshi ya shigo ya tashe ta, kamar babu abinda ya faru..

A al,adarshi 'knocking' dama yake mata sai kuma ya tabbatar ta tashi ta bud'e kofa, sannan zai wuce masallaci.

Gabanta ya fad'i lokacin da taji shi yana kiranta, amma kuma hankalinta ya kwanta da taji yanayin kiran, dama baya d'aga muryarshi da asuba..

"Yaya,..Yaya, ki tashi kiyi sallah."

Ahankali ta mik'e ta bud'e kofar. 

Tun da yaga ta bud'e ya juya.

Tayi hamdala a zuciyarta bata son had'a ido da abban nata.

Akan darduma ta zauna bayan ta idar da sallah ta, tunano ta ina zata fara tun karar Yusuf da maganar abbah ta ke.

Gashi ya k'wace wayar bare ta kira shi. Ta mik'e ta bud'e wata jaka ta dakko zoben da Yusuf ya bata, ta dawo ta zauna.

'Tun ranar da aka koma makaranta ta karb'a a wajen Mama tace mata, zata mayarwa da Basma, shine ta boy'e shi.'

Ta kur'a wa zoben ido, tana tunano wanda ya mallaka mata shi, ahankali kwallah ta cika idanunta.

Allah ka taimakeni.. Allah kasa kada Abba ya rabani da farin ciki nah!!

'Idan na rabu da Yusuf na rasa komai.

Ta janyo Diary d'inta da yake akan 'Bed side drawer' (gefen Gado)

*'Together forever'*

_Our love is built up with scriface and devotion.._

_I will not let it be possible..!!_

_And.._

_I promise you to be

_with you forever no matter what difficult and challenges I'm_ _gonna face.._

" _I love you my_ _Yusuf!_


Ta rufe Diaryn ta ajye, sannan ta mik'e ta nufi kitchen wajen Mama, tasan ita ma babu dad'i ta kwana.

Maman tana kitchen d'in kuwa.

Tayi sallama tare da cewa,

"Mama,Gudmorning"Maman ta kalleta 

"An tashi lpia" 

"Lpia lau."

"Bari in fere miki dankalin."

"Ok kiyi sauri to, kinga kada ku makara a school."

"Ta k'ara kallonta.

Idan kin gama kije ki bawa abbanku hak'uri."

"To Mama"

Tana gamawa ta mik'e ta nufi d'akin Abban, gabanta na fad'uwa.

A tsaye ta tarar dashi a falon shi ya rataya jakarshi yana shirin fita.

Tayi saurin durk'usawa har k'asa. 

"Abba barka da safiya"

Ta fad'a kanta sunkuye.

"Barka, dai kun tashi lafiya?

Ya fad'a babu yabo babu fallasa.

"Lpia lau.

"To madallah"

ya fad'a yana shirin cigaba da tafiya.

Ahankali tace "Abba, don Allah kayi hak'uri kaji"

Ya d'anyi murmushi.

"Hmm, yaya kenan kinyi laifi ne?.. Ba kina ganin abinda kika yi dai dai ba ne koh?

Cikin raunin murya tace.

"Wallahi Abba ba haka bane, don Allah kayi hak'uri."

Ya juyo, ahankali ya kalleta sosai, sannan ya dawo ya zauna.

"To Me yasa kikayi haka? 

"Babu komai"

" Um, dama na nunawa mama fa wayar"

"Tambayar ki nayi me yasa kikayi haka?

"Um babu komai"

" To a ina kika sanshi?

Anan ta d'an fad'a mishi yadda suka had'u da Yusuf d'in.

Da yadda ya bata waya.

Amma bata fad'a mishi sun tab'a had'uwa a wani waje ba, sai ma ta nuna ranar da suka had'u gidan Hajiyah shine ganinta na biyu ita da shi.

Abban ya d'anyi shiru sannan, fara mata magana cikin nasiha, don ya fahimci ita take buk'ata.

"Hafsah ke har yanzu yarinya ce, baki san me duniya take ciki ba.

Ba wai ina hanaki yin wasu abubuwa bane da nufin k'untata miki..Kin manta ni mahaifinki ne?.. Ki daina tunanin zanyi wani abu da niyyar takura miki kinji?

Ta gyad'a kai kawai.

"Ya cigaba.

"Idan kina son abu ki dinga tambayata ko menene shi, kinji yaya? Da kin fad'a min kina son waya da tuni na sai miki..

"Ina son kiyi karatune kinji.. Ko kin fi son in miki aure yanzu?

Tayi saurin girgiza kai.

"To, ki maida hankali kan karatunki kawai, in sha Allah zaki sami mijin da zakiyi alfahari da shi.

Ya mik'a mata wayarshi.

"Ungo saka min number shi.

Hannunta na rawa ta karb'a. Ita dai tana tsoron kada Abba, ya kira Yusuf.

Ta rubuta, ta mik'a mishi.

"Yauwa, yaya."

"Allah yai miki albarka.

Ahankali ta amsa da "Amin"

Ya mik'e.

"Maza ta shi kije kiyi shirin makaranta,nima yau da wuri zan fita.

"Abba a dawo lafiya"

Allah yasa.

Ya fad'a yana fita daga cikin falon.

Daya zo fita ta babban palour, yaran nata hayaniyar shirin Makaranta.


Suna ganinshi suka hau gaidashi. Abba "Gud morning".. "Abba ina kwana?

Ya amsa cikin fara,a yana shafa kansu

Mama ta fito da d'an sauri, daga kitchen.

"Barka da asuba"

"Barka dai."

"Am fita zakayi ne?

"Eh sauri nakeyi"

Bataji dad'in hakan da yayi mata ba, amma sai ta hadi'ye har da yi mishi murmushi.

"Adawo lafiya, Allah ya tsare."

"Amin.

"Sai na dawo.

"Ok bye"

Ta koma kitchen.

Yaran ma suka fara, "Bye bye abba Adawo lafiya.

Shima bai ji dad'in hakan ba, amma kuma so yake ya nuna mata laifinta. Don ya fahimci hafsah bata da laifi tunda da saninta take komai, kuma akwai k'uruciya atattare da ita.

Hafsah bataji dad'i ba Basma bata zo makaranta ba, taso ta kira Yusuf, ta fad'a mishi yayi shirin amsa kiran Abba. Kuma tana son neman shawarar Basma akan al,amarin.

Da yamma bayan abba ya dawo gida. 

Mama ta ta tare shi. Babu laifi ya d'an saki jiki har yaci abinci.

Da daddare ne ta sameshi, yana d'akinshi yana wani aiki a computer.

Ta zauna kusa da shi.

"Abban Hafsah don Allah ka saurareni akan maganar nan.

Ya d'an tsaya da abinda ya ke ya kalleta.

Ina jinki.

Ta Kyautata muryarta.

Dama fa wallahi bada wani manufa na bata wayar nan ba, and wallahi na rantse bansan yarinyar nan tana zance ba."

Ya ajye Laptop d'in a gefe.

"Me kike son fad'amin, baki san tana zance ba, ya zanyi in yarda dake?

Bayan ke ta nunawa wayar?

"Eh ta nunamin"


_(kaji uwa😇👍🏼) love u mama nah_😘 #karima.

"So, sai na k'wace na kuma ce kada ta sake kulashi, yanzu lokacin yin karatu ne.

"Me yasa baki sanar mini ba.??

Kayi hak'uri bana son ina kawo maka damuwa ne, kuma lokacin ka dawo ne daga tafiyar dakayi, bana son ka damu kanka bayan kuma ga stress na office, then na zaci "I can handle it"

Amma ayi hak'uri.

"Hum! Yai ajiyar zuciya sanan ya d'anyi murmushi.

Mata kenan!! wato saboda ba,ason damuwata, sai akasa fad'amin matsalar da zata jawo babbar damuwa. #zancen zuci.



Afili kuwa ce mata yai. "Okey, ya akayi kuma kika bata wayar?

"Um, gani nayi ba babba bace wayar, kuma kada ta zaci ko ina zarginta ne, shine yasa na bata."

Ya d'an dara (dariya) kad'an. "Hmm Mrs habeeb kenan.

Sannan ya tausasa murya.

"Iya hangenki kenan, mata kuna da raina abu. Yanzu baki ga bata wayar da kikayi ya sa ta sami hanyar contacting d'in shi ba?

"Allah ya rufamin asiri iya gidan Hajiya appointment din nasu ya tsaya."

Ya fad'a yana 'yar dariya.

Baki san wani abu ba Ameenah, yanzu Hafsah gani take bata wayar nan da kikayi, kin bata damar contacting d'in yaron ne.

"Tayi shiru, yace 

Baki gane hakan bane Koh??

Tayi d'an murmushin jin kunya, ita ina tunanin ta yakai nan.!

Sai kawai tace,

"Wai kana nufin sai Hafsah ta iya zuwa wani waje da saurayi??

"Hm, kina mamaki koh? 

Ta gyad'a kai.

"Bana zaton zata iya yin haka"

"Hm, ki bar yaran yanzu Amina!

Ya saita muryarshi ta dawo 'Serious'

"Ni dai ina rok'onki da kuma baki umarnin, don Allah kada ki sake b'oyemin lamari makamancin wannan, domin idan matsala ta afku na rantse sai kinfi kowa shiga damuwa."

"In sha Allah zan kiyaye, ka k'ara hak'uri da ni"

"Idan kika yi hakan kin gama min komai."

Ya d'ora.

"Ina tsoron sha,anin samarin yanzu ne, akwai abinda nasani wanda ke baki sanshi ba, ki d'auka kula da kuma hak'k'ina ne dole in saukeshi, in sha Allah babu matsalar da zata gagareni kinji? 

Ya k'arashe maganar da d'an murmushi.

Tayi ajiyar zuciya

"In sha Allah baza,a sake ba."

"Nagode sosai zaujaty!!, wasu abubuwan bazaki fahimta ba sai nan gaba. Yanzu kiramin Hafsan kiga wani abu."

Tace "To" sannan ta mik'e ta fita.

Tare da Hafsan suka dawo, ta zauna kusa da Mama.

Abban ya kalleta cikin sakin fuska yace, 

"Hafsah kin fad'a mishi ina neman shi?

Ta girgiza kai ahankali.

Ya d'an had'e rai.

"To Meyasa?

"Abba babu waya,.. Kuma..

Sai tayi shiru.

"Hmm kuma me? 

Da ya ake kike had'uwa da shi wato don ba naki ba ne kiran koh"?

Kwallah ta taru a idonta.

"Allah abba ba haka bane bansan inda zan ganshi ba."

"Hmm, kije gidansu mana."

Ya fad'a fuskarshi babu wasa.

Kwallah ta fara bin kuncinta tana zarya.

'Menene abba ya ke nufi kenan?? 

Kada dai har ya fara zarginta da zuwa gidan su Yusuf. 

Sai yanzu ta yi nadamar k'in sanarwa ko da mamace tsakaninta da Yusuf, tasan zata fahimce ta.

Gashi yanzu hakan ya zame mata matsala cikin tarayyar su.

"Bazakiyi magana bane.?

Cikin kuka tace Allah Abba bansan gidansu ba."

Au,? Duk dad'ewar taku baki san gidansu ba.?

"To wacce unguwa yake?

Ta girgiza kai. 

Sai yanzu ta tuna basu tab'a maganar inda gidansu yake ba.

Abba wallahi bansani ba.

"Alright."

Ya fad'a yana mik'a mata wayar shi, daya danna kiran Yusuf.

"Ungo yi mishi magana ta nan."

Mama dai idone nata kawai.


Ta karb'a tasa a kunnenta, sam bata san me zata ce mishi ba ma.

"Hello" taji ance daga d'aya b'angaren.

Ta d'an daburce.

Um am, hell.. "Salamu alaykum"

"Wa Alaykumussalam."

"Am Hafsah ce"

Oh! My sweet baby, mene ya sami wayanki ne, kin barni ina missing naki." 

"Hmm, ta fad'a.

Sai wani rarraba ido take tana kallon abba da Mama.

"My baby inaso zanzo wajenki kawai ni dai yau"

Ta Kalli Abba wanda ya tsare gida.

Babu damar tace mishi kada ya zo, don bata son abba ya fahimci hirar da suke.

"Um, dama abbanmu nason ganinka"

"You say what?

Tayi shiru.

"Talk to me mana, Baby, mesa abbanki keson ganina?

Bata da mafita illa ta katse wayar, don haka tace "Okey, nagode, sai anjima."

A tare abba da Mama suka tambayeta "Meyace miki"?? 

Cikin in, ina tace,

"A wai yace in sha Allah zanzo."

Abba ya kalleta sosai.

'Ita Mama tuni ta yarda da zancen.

"Hum, shikenan tashi kije to"

Inji Abba.

Ta mik'e

"sai da safe.

Tana fita Abba ya kalli Mama, 

"Bafa zuwa zaiyi ba!

Mama ta kalle shi da son neman k'arin bayani.

Ya tari numfashinta.

"Ki zuba ido ke dai"

A can B'angaren Basma kuwa..

Tana kwance kan gadonta shiru, wani tunani take. Ko na meye oho!

Wayarta da ke gefenta tayi k'ara.

Taja tsaki tare da mik'a hannu ta jawo wayar.

Ta ware ido lokacin da taga sunan mai kiran nata, akan 'Screen' wayar.

"H. Hamid'slove"

Tayi murmushi har da yin gyaran murya.

"Hello"

"Basmah gud evening"

"Hw are you"

"Am fine, 

"Ok, please akwai magana da zamuyi dake, if you have time.

"Ok, no problem go ahead"

"Thank you.

"Am friend enki ne fa, she has a problem, bata saki jinkinta dani. I mean she always wants to make a difference between us, she always want to create a distance between us."

Basma tayi murmushi.

"Hmm, please be patient with her, I told you many times that Hafsah bata son kana mata abinda kake mata b'cause bata saba,ba..And yanayin naku ba d'aya ba.

"Nooo, I already know this, but why not if she loves me! ?

Basma tayi dariya.

Haha, no she loves you but she don't take care of you, as you want. And she will never do!!

Gaskiya na fad'a maka.

"Oh my gosh''.. Meyasa kka ce haka."? "Hmm k manta neh am her friend I know her more than you.."

Aransa yaji cewa gaskia ta fada.

"Kinaji nah,

Yanzu ma wani another problem enne, kinga fa yanxu munyi waya da ita, and she's telling me that daddy nata nason ganina!"

Cikin nuna mamaki sosai tace.

"To me yasa kun sami misunderstanding ne? 

"No, 

"Wllhi I don't know why yake son ganina."

"Hmm may be he wants to know Something about you, kasan ya hana ta kula samari, then itama naga bata son kana mata irin wannan abubuwan, so may be zaice ko kafito ne ayi muku aure"!!

Whatt??..are you telling me??..Hmm, impossible, I know I love her, but aure not yet gaskiya, barin fad'a miki bazan iya zuwa wajen abbanta ba"

Basma tayi wata irin dariya. 

"Why not. kafito kawai musha biki!

"Hmm am telling you as her friend, please ki nuna mata she have to change her attitude, cause am tired da abinda take min, kuma I don't think zan k'ara zuwa wajenta, sai dai tana meeting ena somewhere na gaji fa"!!

Basma ta kisma wasu abubuwa wanda nima ban san su ba. (Sanin gaibu sai Allah)

Amma afili naji tayi dariya sannan tace,

"Alright" wannan shine solutions" Amma Advicebly kada kaje gidansu couse nasan halin abbansu!!

Anya Basma!! 🤔🤔

Thank you alot bye bye.. I zanje club at 12:00am

"Ok, hope to meet you there one-day!!"

"Kina zuwa ne?

"Yeah, 

"Hafsah fa? 

"Hmm, kana da son jan zance, ya za,ayi kaga wannan a club??

"Oh shut!!

Basma ta Shek'e da wata dariya.

"Bye bye" 

"Ok, thank you u are important in my life."

"Hmm, kada ka damu"

Kawai tace.

Amma azuci cewa tayi.

"Sai ma na sami wata damar..

Ta ajye wayar tare dayin wani d'an ihu,

Sannan tace,

"Saura k'iris"

🤔🤔🤔

To me take nufi?? 




Post a Comment

0 Comments