TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 20

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____20💎



 Saida suka gyara kitchen d'in sannan suka kwashe kayan abincin suka jerikke akan dining table suka dawo falon suka tada Bassam da Bilal dake bacci suka wanko masu bakinsu sannan suka dawo falo suka zauna suna jiran fitowar Ummi, dady suka gani ya turo k'ofar falon bakinsa d'auke da sallama, da gudu su Bilal sukaje wurin sa suna oyoyo dady, ciki hanzari Mahmud ya tashi ya karb'i jakar hannunsa yana fad'in


"Sannu da dawowa dady"

 

"Yawwa Mahmud kun dawo?"


"Eh dady su papi na gaishesheka sosai" k'arasowa daga cikin falon yayi d'auke da Bilal d'ayan hannunsa kuma rik'e da hannun Bassam, kamar 'yan matan sun had'a baki gaba d'ayansu suka yimasa sannu da zuwa atare cikin girmamawa, cikin zolaya da barkwanci dady yace


"Yawwa 'yan matana, Basmah shin ko kin gano min Batool da Bilkisu" gaba d'ayansu sukayi dariya Mahmud na fad'in


"To gadai Batool nan a zaune dady amma Billy ina tunanin munbarota asibiti.." Kafin yarufe  baki cikin shagwab'a Billy tace


"Ehnm..ehnm kai yaya bagani anan zaune ba, ni kadena yimun fatan zaman asibiti banaso" dariya dady yayi had'e da k'ok'arin wucewa bedroom d'in Ummi sai gashi tafito cikin riga da plane zane na atamfa super England ash and maroon colour tayi matuk'ar kyau sosai sai k'amshi takeyi, sannu da zuwa tayi masa sannan takarbi Bilal dake hannunsa cikin lowering voice tace


"Yallab'ai ko zaka fara da abinci kafin wanka naga kamar yaranka yunwa sukeji" batare daya tanka mataba ya kashe mata idonsa d'aya sannan ya nufi gefen da dining table yake, murmushi tayi don tafahimci abunda yake nufi sannan ta juya tana kallonsu 


"Babanah kutaso kuyi dinner ko?"


"To Ummi sannu da k'ok'ari"


"Yaukam ai k'ok'arin na k'annen kane saboda haka kataso ka kwashi Batool delicious ko Batool?" Sosai suka shiga yin dariya har da dady dake can zaune shida su Bassam inbanda Basmah da ta kalli Ummi da gefen ijiya sannan ta mere baki, Mahmud ne ya tsaida dariyarsa yana fad'in


"Kai Ummi wannan irin kambamawa haka wai Batool delicious inama laifin kice Billy delicious don indai batool ce nasan bata iya komai ba"


"Lallai yaya aikuwa yau zakasha mamaki domin d'and'anon girkin natane," Billy ce tafad'i haka tare da rik'o hannun Batool data turo baki jin abunda yafad'a, murmushi Ummi tayi ta rungumota ajiki suka nufi dining table yana biye dasu Ummi tace


"Fita batun yaya ko yayi aure bazakije gidan saba balle yasa ran zakiyi masu girki" 


Bayan kowa ya zauna Mahmud ya juyo yana kallon Basmah dake kwancenta a inda take ko motsawa batayi ba yace


"Ke bazaki taso kici abincin bane?"


Juyowa tayi takallesa sannan ta sake maida idanuwanta tarufe, zuciyarta na rad'ad'i, muryar dady tajiyo again yana fad'in 


"Basmah meke faruwane da bazaki taso kici abinci ba?" 


"Dady tun d'azufa nakejin yunwa aka hanani" juyowa dady yayi yana kallon Ummi da itama ta d'ago kanta da k'arfi tana kallon Basmah cike da mamakin abunda tafad'a, shiru dady yayi tare da ajiye cokalin abincin dake hannunsa, Batool da tun d'azu maida hankalinta ga cin abinci da takeyi ta d'ago kanta ahankali tana kallon Dady da Ummi tacire hannunta daga abincin da yake ita batason cin abinci da spoon tace


"Dady Ummi, kufita batun yayya Basmah kuci abincinku, nice nan na hana Billy ta zuba mata abinci lokacin bamu ida kammalawa ba tazo tayi mana tsaye wai yunwa takeji, bacin tana zaune Ummi tashiga kitchen amma ta kasa tashi tarik'a mata aikin sedai mu damuke k'annenta mukaje, don haka idan zata taso taci abincin ta taso idan kuma bazata tasoba ita yunwa zata wahalar" tana gama maganar ta maida hankalinta ga cin abin cinta haka shima dady ya d'auki chokalinsa yaci gaba da cin abinci, Ummi ma haka, d'agowa Mahmud yayi saboda jin dad'in amsar da Batool tabaiwa dady bayan yakai lomar spoon abakinsa ya had'e 'yan yatsunsa biyu ya d'agawa Batool alamun girkin is so test sannan ya k'ara d'aga mata babban yatsansa alamar jinjina tayi daidai, wani irin takaicinsu ya rufe Basmah ta tashi da gudu tabar fallon tana kuka, kamar dady da mom sun had'a baki atare sukace


"Allah ya shirya" gaba d'ayansu suka amsa da amin.


Kwance mom take tana juye juye akan gado tarasa meke yimata dad'i a rayuwarta, ba abunda take da buk'ata aduniya irin kota halin k'ak'a taga ta salwanta rayuwar Aisha data zuriarta, wayar tace tayi k'ara tajawo had'e da karawa akunne, hello suka fad'a atare ita da wacce takirata,


"Hello, hajiya kilishi"


"Na'am mutuniyata kar dai ince har kingane muryata"


"Sosai kuwa bagashi kin gani ba, ya ake cikine"


"Daidai wlh..alhajinki yazo biko kuwa?"


"Hmm bari kawai hajia kilishi ina cikin matsala wlh har yanzu banga k'afarsa ba, ke inma tak'aice maki koga waya bai nemeni ba"


"Tafd'i jam shine kuma kike zaune abunki hankali kwance!? Yo ai bakiga tazama ba don anriga ankautar masa da hankali akanki bakya gabansa"


"Nasani hajia kilishi yanzu haka tunanin da nakeyi kenan akan yanda zanb'ullowa al-amarin, ina mafita yanzu?" Wani irin shu'umin murmushi tayi aranta tana fad'in anzo wajen!!!


"To kibari har insamu dama zan shigo sai muyi magana, ya papi da hajia kaka lpy suke? Saboda nakwan biyu ban kirasu awaya ba"


"Eh lpynsu klw wlh"


"Kigaishe dasu kafin inzo"


"Zasuji insha Allah" daga haka suka d'an tab'a hira sannan sukayi saida safe, tana gama waya da hajiya kilishi saiga kiran Basmah yashigo awayarta, dasauri ta d'aga wayar had'e da cewa "hello Basmah" cikin muryar kuka ta amsa da "hello mom, don Allah kibawa dady hak'uri kidawo, ni bazan iya zama gidannan ba idan bakya nan" 


"Me akayi ne Basmah, kiyimun bayani duk kintayar mani da hankali" nan tafad'a mata k'arya da gaskiya tak'ara da cewa hatta Batool yanzu anhure mata kunnuwa rashin kunya take yimata, iya k'ololuwar b'acin rai mom takai tace 


"Shikenan kyalesu duk saina ganar dasu kurensu, yanzu inashi yayan naki?"


"Yana d'akinsa"


"OK inazuwa" katse wayar tayi takira lambarsa lokacin yana k'ok'arin kwantawa, cikin girmamawa ya d'aga wayar


"Assalamu alaikum, mom..."


"Maza karufemun baki, wato don kana samna za'a tozarta 'yar uwarka agaban idanuwanka kayi shiru, to yanzu da aka hanata abinci da yunwa kake so takwana?"


"Mom metace maki anyi mata?, ya za'ayi a hanata abinci haba mom meyasa bazaki fahimci matsalolin Basmah ba"


"Ni bana son jin komai daga gareka maza kaje ka d'ibi abinci ka kaimata idan kuma babu kafita kayo mata take away"


"Haba mom dubafa kigani pass 11:00 yanzu ina zanje in nemo mata abinci" cikin b'acin rai tafara yimasa fad'a


"To idan bazakaje ba, bari ni infita insiyo mata sai kazo bakin gate ka karb'a ka bata tunda ni ban isa gareka ba"


"A'a mom kiyi hakuri zanje Allah ya huci zuciyarki" suna gama wayar yaciro doguwar jalabiyarsa dake sagale a jikin hanger, d'akin yarufe ya nufi part d'in Ummi, yana shiga ya k'wallawa Batool kira, cikin gigin baccin daya soma d'au karta tafito tana fad'in


"Yaya lpy?"


"Lpy klw akwai sauran abinci"


"Eh amma Ummi ta sakasa a fridge don karya lalace"


"OK shikenan zaki iya tafiya ki kirawomun Basmah"


Kai tsaye yanufi wajen fridge ya d'oko abincin sannan ya shiga kitchen ya d'oko plate ya yad'ibi abincin har saida plate d'in yayi soro yazuba stew asama sannan ya maida kingin acikin fridge, fitowa tayi da rigar bacci ajikinta earpiece lak'e akunnuwanta tace


"Yaya gani" kallonta yayi daga sama har k'asa kasancewar rigar nada d'an kabri kuma ta gota guiwowinta shiyasa bai yimata fad'a ba


"Zauna ga abinci kici" kasancewar tanajin yunwa girman kai yahanata zuwa tad'iba taci yasa tazauna batare data yimasa musu ba tafara cin abincin shikuma yadawo agabanta ya zauna kai hannunta keda wuya taji abincin da mugun sanyi ai kuwa tab'ata fuska tare da cire hannu tana kallonsa


"Ni bazanci wannan abincin ba yayi sanyi da yawa" wata irin muguwar harara ya jefamata had'e da cewa


"Ai wlh sai kin cinyesa tas, ba yunwa kike jiba, yau senayi maganinki intak'amarki rashin kunya" adole yatasa ta agaba tanaci tana kuka gashi babu damar d'aga waya balle takira mom......



Post a Comment

0 Comments