TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 25

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_


_Ina kuke 'yan group d'in *HOME OF NOVELS* gaisuwa ta musamman zuwa agareku saboda muhimmancin da kuke dashi agareni bazan tab'a iya misaltashiba, tabbas kuna sakani nishad'i tare da k'aramun k'warin guiwa aduk lokacin da naga kuna comment idan nayi update, wannan dalilin ne yasa bazan iya wuce wannan page d'in ba har sai na isar da jinjina had'e da fatar alkhairi agareku, especially you people UMMIE, ZULAIHA SAMINU ELJIBRIL, MALKALFRED966 da kuma OUM RUQAYYAT, nagode nagode sosai Allah ya faranta maku zuciyoyinku fduniya da kuma lahira, *luv you all to the square of infinity*💋❤_



💎Page_____25💎



  Daga nan fa Bab's da suby suka dinga mik'awa Basmah kayayyakin dake sa maye kala kala tana sha wai don duk su sama mata farincikin da take tsammanin tarasa acikin agidansu,


Tunda ummi tagama waya da ita tafad'a akan kujera zaune hannunta na rik'e da wayar yayin da idanuwanta suka kasa dena zubar da k'wallan bak'inciki da takaicin rashin sanin halin da Basmah tajefa kanta aciki, haka Mahmud ya gaji da yawace yawacen nemanta ya dawo gida ya tarar da ita cikin wannan halin, har ya k'araso gabanta ya duk'a had'e dasa hannayensa akan hannunta dake rik'e da wayar bata san yana wajen ba sai lokacin da taji ya rumk'e hannun nata sosai sannan ta farga dashi awajen, hannunta d'aya ta d'aura akan hannayensa dake kan nasa had'e da kallonsa cikin muryar kuka tace


"Basmah..!" da sauri ya lumshe idanuwansa yace "ki k'yaleta Ummi, duniyace ta isheta wando da riga hadda mayafi, rayuwar da tazab'awa kanta kenan babu yanda zamuyi da ita sai addua, babu inda banjeba cikin gidajen 'yan uwa da wasu k'awayenta dana sani amma ban sameta ba, abun takaicima ko wayata tak'i ta d'aga saboda d'ai tasan mezai faru idan ta d'aga" yak'arasa maganar shima hawaye nafita daga idonsa.


"Bazai yuyu a k'yale taba, itafa 'ya macece dake buk'atar killacewa, wallahi zaifi ace aure aka yimata da a k'yaleta cikin wannan rayuwar sam hakan bai dace ba Babanah kayi tunani mana"


"To Ummi yanzu me za'ayi?, tunda bamu ganeta ba"


"Sake komawa zakayi ko Allah zaisa ka ganta"


"A ina kuma awane wajen, natabbata bata area nan, amma bari na sake komawa" tashi yayi yafita yana gogur idanuwansa da sukayi masa jawur saboda tsananin b'acin rai da yake ciki, har yakai bakin k'ofar fita Ummi takira sunansa,


"Babanah ka kula da kanka sosai" gyad'a mata kai kad'ai ya iyayi sannan yafita,


Tunda hajia kilishi ta d'ora mom akan hanyar salo da yaudarar da zata bijirowa dady da ita don ya maisheta d'akinta tafara shire shiren yanda zatayi yanzu haka kusan minti biyar kenan tana kiran wayarsa amma yak'i d'agawa, hakan ba k'aramin b'ata mata rai yayiba cikin takaici tajefar da wayar tana maseefa


"Lalle mutumennan yamatuk'ar walak'antani, yanzu nike kiransa yak'i d'agamun waya, wlh duk randa yashigo hannuna sai nasa yayi nadamar wannan abun da yayimun" dariya hajia kilishi dake zaune a gefen gado tana buga game da wayarta tayi ba tare da tad'ago kan taba tace


"Saifa kin kai zuciyarki nesa yanzu don da alama uwar gidansa ta cikashe masa duk wani gurbi da kika kasa cikashewa acikin gidansa, mezai hana ki gwada tura masa text message, natabbata zai gani kuma zai karanta, ki kula banda rawar kai ko kuma kushe  masa mata acikin alamurranki ai kingane ko?" Sai da mom tad'an bata rai tare da gallawa kilishi harara sannan tajawo wayar, message tafara rubuta masa kamar haka cikin zafi da k'unar zuciya


_Alhaji natabbata kana ganin kirana ka kak'i ka d'auka saboda yanzu banice agaban kaba, to koma dai meye yakamata kasaurareni kona minti d'aya ne saboda kasan ko meye dalilin da yasa nakiraka, alhaji kenan inaso kasani fa har abada babu wacce zata iya maye maka gurbina matuk'ar ina raye saboda nice uwar 'ya'yanka wacce tafara baka farincikin da aka kasa baka na tsawon shekaru don haka kuwa kasan ban cancanci walak'antawa daga gareka ba, idan kayi tunani ina jiran kiranka domin mu magantu_ tana gama rubutawa ta tura masa had'e da jefar da wayar ta dafe kanta da duka hannayenta.


"Wlh alhaji na neman sa in zubar da matsayina agunsa" kallonta hajia kilishi tayi sannan tasake maida hankalinta ga game d'in da takeyi tana fad'in


"Abune da yazame maki dole kiyi inhar kina so kikoma d'akinki don cikar burinki to dole kisauke wannan girman kan da jijji dakan da kike yimasa",


"Shikenan! He most to pay fo all this wlh" k'arar shigowar message a wayarta taji da saurin ta d'auko wayar tana duba amsar da dady yaturo mata,


" _Hmmm kice har yanzu da sauran zama kenan!_" 


Da k'arfi mom tace "what?", kingani ko ai duk ke kika jamun wannan rainin, anfad'a masa cewa gidan namu isata yayi ne?"


"Cool k'awata" hajia kilishi tafad'a


"Mik'omun wayar naga mekika rubuta kuma wacce amsa kika samu da kika buga man wannan uwar tsawar acikin kunne"


Duk jahilcin hajia kilishi saida ta bud'e baki cike da mamakin kalaman da taga mom ta turawa dady, dafe goshinta tayi da tafin hannunta tana kallonta


"Ai kuwa da gaskiyarsa baki gaji da zaman gida ba, taya zaki tura masa wannan sak'o mai cike da isa da kuma izgilanci kuma kiyi tsammanin zai tsaya ya saurareki? Kash wlh so kike kib'ata mana tsari gaba d'aya, keda zaki yita lallashinsa da kalamai tausasa masu dad'i har kisamu ya saurareki amma shine zaki tura masa wannan shirmen? Cab...to wlh da sake indai baso kikeyi ki ida tsofewa agidan nan ba sukuma suna can suna bugun ingantacciyar rayuwarsu cikin soyayya ba"


"To yanzu ya kikeso nayi? nifa gaskiya bazan juri wannan sabon walak'anci nasa ba"


"Ai kuwa yazama dole kijure don cikar burinki idan kuma kin safe tun yanzu kin barwa Aisha shi sai intattara inawa inawa gobe inbar garin nan" da sauri takame hannunta


"Haba k'awata karki yimun haka, yanzu me kikeso ayi ko nace masa kuma?" shiru tayi ta kalleta ta kalli wayar sannan ta jefa mata ita ajiki,


"Maza kisake tura masa wani kuma kibasa hak'uri" jiki na rawa ta d'auki wayar don tana matuk'ar buk'atarta atare da ita domin batada wata madafa idan ba itaba, wani message d'in tafara rubutawa cikin jin haushin k'awar tata.


" _pls kayi hak'uri bahaka nake nufi ba, gaba d'aya narasa natsuwatace atare dani saboda rashinka akusa dani, nayi kewarka don Allah kayafe mani nayi nadamar abunda nayi kuma ashirye nake nagyara kuskurena_


 Tana gama rubutawa ta mik'awa hajia kilishi wayar tana tuk'uburi domin taduba tagani idan yayi, murmushi tayi tana kallonta bayan tagama karan ce message d'in had'e da rubuta _I LUV YOU SO MUCH & AM MADLY MISSING YOU_ ak'asan rubutun sannan tayi sending message d'in wa dady tare da mik'a mata wayarta tace 


"Shak'iyiya ana so ana kai kasuwa, to sai kijira amsa kigani yanzu"


A wannan karon kam dady dake zaune akan kujerar office d'insa yana duba wasu takardu tashi tsaye yayi cikin sauri kamar wanda aka tsikara da allura, lokacin daya gama karanta sak'onta, domin a iya saninsa tunda suke bata tab'a bashi hak'uri ba idan tayi masa laifi ba saidai yagaji da fushinsa sudawo su daidaita, amma sai gashi da kanta take basa hak'uri had'e da dad'ad'an kalamai, Allah sarki miji da mata sai Allah ko yanzu dady baisan badon karan kanta tayi hakan ba sai don ta cimma mummunan manufarta tare da taimakon k'awarta hajia kilishi" wani irin farinciki ya tsinci kansa aciki wanda ya haifar masa da nan take ya manta da kaidi da kuma makirci irin na mom, har zai kiranta sai kuma yafasa shima ya sake rubuta mayar mata da sak'on a takaice


_Da gaske kikeyi hajia Hussaina_


Tana karantawa tayi dariya tana cema hajia kilishi 


"Kinga sokon har ya yadda, bari zakayi idan kazo hannu, dama indai wajen sanyin zuciya ne nasan babu kamar alhajina kuma ai inada tabbacin yana matuk'ar sona ransa ne yab'aci har yayimun haka" wani sak'on tasake tura masa


_Sosai kuwa alhajinah don Allah kasake bani dama zaka fahimci rashinka yasa na canza dukkanin halayyata nidai fatana kayafe mani kai da Auntynah_


A wannan karon cikin zumud'i dady yakira wayarta tana d'agawa tafashe da kukan makirci


"Kayafemun alhaji wlh nayi nadamar duk abunda nayi, nayi maka alk'awari zanbika zanbi aunty Aisha bazan sake yin abunda zai haifar da damuwa acikin gidan kaba" wani lumshe idanuwa dady yayi yanajin kukan nata har cikin ransa.


"Karki damu komai ya wuce, kiyi shiru bana son jin kukan nan naki yana azabtar da zuciyata" mom najin haka tasake fashewa da wani kukan dak'arfi har tanayi kamar tana sharar majina


"Kabarni inyi kuka mana, na zalinceka da yawa don Allah kayafeni" haka dady yayita rarrashin mom yana fad'a mata dad'ad'an kalamai har saida yaji muryarta ta daidaita sannan sukayi sallama


Kallon hajia kilishi data saki baki tana kallon ta cike da mamaki tayi ta sakar mata murmushi had'e da ajiye wayar akan gado tashige toilet abunta, saida tafito hajia kilishi ta iyayi mata magana,



"Hussaina dama shak'iyancinki da makircinki yakai haka shine har kike neman taimakona kina yimani kamar bakisan mekike yiba, to plan A yak'are tunda kun daidaita da mijinki nima gobe komawa zanyi yarage naki ki aikata plan B yanda yakamata inyaso idan kingama dashi saiki nemeni musan yanda zamu b'ullowa plan C.


Dariya mom tayi tana goge jikinta da towel tace


"kad'an kika gani, dama can fashiyar bak'i ke wahalsheni amma ana nunamun hanya shikenan anwuce wurin"


"Eh naga alama kuwa irin wannan makirci haka!"


Muryar hajia kaka suka jiyo tana doka sallama abakin k'ofar d'akin, bayan sun amsa mata ta shigo cikin shigarta irinta nagartaccin tsofaffi dake nuna shirin fitane tayi tace


"Muzamu fita nida papinku don Allah kuje kud'ora dinner kafin mudawo" da yake ba'a jima dayi sallar la'asar ba a lokacin,


Atare suka amsa da "adawo lpy hajia"



Post a Comment

0 Comments