TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 8

 👭❤ *'YAN UWA NANE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_


_*Gisuwa mai yawa tare da fatar alkhairi ga d'aukacin masoya wannan littafi, ngd bisa jajircewarku da k'aunar da kuka nuna agareni da kuma wannan lbri mai suna 'YAN UWA NANE! kuma ina yiwa kowa barka da sallah tare da fatar kowa yayi sallah lpy, in sha Allah zaku cigaba da jini akai akai*_


💎Page_____8💎



   Da sauri billy tanufi wajen Ummi rik'e da kunnuwa har lokacin tana dariya


"Sorry ummina nice fa, Bilkisunki ta annabi mai gadon zinari" Cikin soyayya Ummi ta d'aga hannunta kamar zata doketa dady yayi saurin jawota har lokacin shima yana dariya


"Haba madan ayimata hak'uri kar asa jinin dady ya hau" kafin ummi ta amsa har dady ya maido kallonsa ga Billy fuskarnan tasa ad'aure kamar bashine yagama dariya yanzu ba, cikin natsuwa yake tambayarta 


"Bilkisu me yafaru tsakaninki da auntynki basmah" shiru billy tayi kanta sunkuye ak'asa kafin tajiyo muryar dady yana sake jefo mata tambayar da k'arfi, nan take tayi masa bayanin duk abunda yafaru batare da tayi k'ari ko ragi ba, hannunta dady ya saki had'e da jawo hannun bilal dake rungume ajikin Ummi


"Bilal! Shin gaskiya ne auntynka ta fad'a?"


"Eh dady, amma mun bata hak'uri ko aunty billy" ya k'arasa maganar yana kallon 'yar uwarsa da nan take ta gyad'a masa kai.


Murmushi dady yayi had'e da cewa


"Very good! Amma ina so daga yau Bilkisu dake da bilal karku sake musayar magana da 'yan uwanku hakan d'abiace Marar kyau kunji ko?Ke Bilkisu Basmah Auntyn kuce bakyau ace kina mayar mata da magana akan zata yiwa qanenta hukunci, amma duk lokacin da kikaga tayi abunda ya cutar daku to kifad'amun kinji ko?


"Eh dady, kayi hak'uri bazan k'araba in sha Allah"


"That's my dota, haka nake so, Allah yayi maku albarka"


"Amin dady"


"Oya  jeki kishiryawa bilal kema kishirya kafin ingama magana da umminku zamu fita" tsalle Bilkisu tayi tare da cewa dady hadda Yaya Mahmud zamuje?


"Eh idan kunshirya kije kifad'a masa duk da nasan dak'yar inzai iya tunda jikin nasa ba mafita" da gudu billy taja hannun bilal suka nufi bedroom d'in Ummi shi kuma dady ya dawo sit d'in da take zaune kanta ak'asa tana tunanin matsalolin da suke fuskanta agidan na rashin zama lafiya, hannu yasa akan hab'arta tare da d'ago fuskarta tana kallon tasa, lumshe idanunsa yayi ya rufesu tare da bud'esu ya d'age mata gira yana murmushi yace



"Me uwar gidana ke tunani ne?" Murmushin itama tayi sannan tace


"Abunda zai faranta farincikin mai gidanta" 


Dariya dady yayi tare da d'ora yatsansa akan lab'b'anta ganin tana k'ok'arin yimasa bayani akan maganar da yagamayi da yaransa


"A'a Aisha kibar maganar a haka, nadad'e da fahimtar komai, nasan bazaki tab'ayin abunda zai raba kan 'ya'ya naba indai ba sharrin shayd'an ya gitta ba"


"Nagode da fahimtata da dyn Mahmud"


Tana rufe baki sai ga Mahmud yashigo falon, ganin yanda suke zaune so close ya sashi saurin juyawa da sauri


"Come in my son" dady yafad'a da k'arfi had'e da mik'ewa tsaye yana mai farincikin ganin d'an nasa da yake matuk'ar k'auna da kuma alfahari a zuciyarsa, kansa duk'e a k'asa ya k'araso d'akin had'e da gaida Ummi


"Ummi ina wuni?"


"Lafiya k'alau yayan B, ya karfin jikin naka?"


"Alhmdulillah Ummi naji sauk'i ya k'ok'ari?"


"Allah ya k'ara lafiya"


"Amin Ummi, inasu lil sis ne naji gidan shiru" yana rufe baki sai gasu billy sun fito cikin shirinsu suna k'amshi, da gudu bilal ya rugo Mahmud ya cab'esa sama yana fad'in


"Eyyee yaron Ummi, wannan gayu sai ina haka?"


Hannu dady yasa a kafad'ar Mahmud dake k'ok'arin sauke bilal ya lak'amo Mahmud yana fad'in...



Post a Comment

0 Comments