TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Zazzafan so page 22

 πŸŒΏπŸŒΏπŸŒΏπŸŒΏπŸŒΏπŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

*My Family My Pride!!*

*GAISUWA, JINJINA HADE DA* *GIRMAMAWA GA DUK WANI MEMBER NA 'WAZIRI AHMADU MAI* *SHAHADA FAMILY'*

*Aduk inda kuke,* *Allah ya k'aramarku had'e k'anmu..Amiin ya jik'an iyaye da kakanni!!* πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ


FANS AYI HAKURI DA TYPING ERROR BANA EDITING πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ


πŸ“„ *22*



*Data* koma gida Abba ya kirata. Cikin taushin murya yake cewa.

"Hafsah, kinga abinda nake nuna miki koh? Kin ga yak'i yazo koh?

"Abba zaizo fa"

"Hmm, yaushe? Fiye da sati da mishi maganar.

"Wallahi yace zaizo ne"

"Yaushe ya fad'a miki haka?

"Uhm.. 

Abba ya d'anyi murmushi, shikenan ina zuba ido"

Ya sauya zancen zuwa wani.

"Ya shirin jarabawa?.. Ki k'ara karatu kinji,?" 

Ta gyad'a kai "To abbah" 

"Yawwa Allah ya miki albarka."

"Amin Abbah"

"Ki turomin Bashir," 

To Abba.

Aranar bikin Auncle Abdallah, sun shirya duka 'yan gidan don zuwa wajen bikin.

Tayi kwalliya sosai tayi kyau cikin ankon bikin, tana cikin 'yan matan familynsu 'ya'yan yayyen abbanta mata, suna ta shan hira, ba,a cika ba lokacin. Ita dai gabad'aya tunaninta yana ga ina zata sami waya ta kira Yusuf'?

Gasu 'yan matan dai yawancinsu suna da wayoyi.

Hirar makaranta suke sai kuma hirar

samari. 'Nasreen ce tace mata Kefa Hafsah baki da saurayi koh?

'Hmm, anta'bo mata inda yake mata k'aik'ayi.

Ta Kalli Nasreen d'in tace " kin tuna mini wallahi yau mukayi zamu had'u." 

"Allah?

Hafsah tayi murmushi.

Nasreen tace 

"So ki kirashi mana.. Oh ashefa baki da waya, ungo nawa kirashi."

Ta Karb'a "Thank you sisterrrh"

'Hello"

My Baby how are you?

"Am fine.

Nace, "Ka tawo ne?

"Yeah give me just a five minutes"

"Ok".

Sannan Yai k'asa da murya, cikin sanyi yace.

"My Baby"

"Yes..

"Please..

What? Inji Hafsah.

Ya d'an ja numfashi, 

"Forget it.

Sai ta d'an rud'e.

"Please tell me"

"No,ki barshi kawai.

"A,a nidai.."

Yai ajiyar zuciya.

Hum, Ok"

"Ina nufin kin shirya zuwana.?

"Hmm, dear sosai ma"

"Hmm, to me zaki bani please I need some thing special,.. Because kawai ni dai bani son nazo kina min wani abu!

"Dear menayi kuma? 

"Hmm nothing, saina zo."

"Ok"

Ta ajye wayar a sanyaye. Sauran sukayi shewa "Hahh Hafsah ana zuba love".

"Bari yazo muganshi ko ya had'u."

Tayi murmushi "Hmm, Zaku ganshi ne, but my Yusuf is a king dole ku gaidashi then kada wadda ta kalleshi fiye da sau d'aya"...

Ta fad'a har cikin ranta, amma su azatonsu wasa take. Don haka suka Shek'e da dariya.

Hah kajita tab' k'anin namu zamu gaida?..lallai kina da tsaurin ido, Hafsah mun girme ki fa dukan mu"..

Haka suka cigaba da hirar su har lokacin da Yusuf, ya kirata a wayar Nasreen cewa gashi nan'.

Ta mik'e harda k'ara murza powder..

Ya had'u sosai cikin irin shigar daya saba, na k'ananan kaya.

Yau Motar daya d'akko fara ce ta had'u.

Ya bud'e k'ofar motar, kallon ta yake cike da wani shauk'i yana mata murmushin shi dake k'ara adadadin sonshi a zuciyarta.

Ahankali ta k'arasa wajen shi. Ta sakar masa murmushi, 

"Hi my dear!

Yai murmushi.. har da lumshe ido"

"You're welcome Baby" 

Ta shiga cikin motar ta zauna.

Wani k'amshi na musamman, ne ya ziyarci hancinta.

Yanayin taji ya mata dad'i fiye da koyaushe. 'Wato duk sanda take tare da Yusuf, tanajin wani abu na musammaman a tare dashi.. Bare kuma na yau ya nunka koyaushe. Bakinta taji yayi nauyi wajen kasa furta koda kalma 'You're welcome dear ' ne kamar yadda ta saba.

Ahankali ya juyo da kallonshi zuwa gareta, ya k'ura mata ido shima, yana karanta mata wani abu dake cikin zuciyarshi..

Taji wani nauyinshi.. Sannan kuma ta gaji da 'Silent' d'in da sukayi..

Ahankali ta kai hannunta saitin idanunshi ta yarfe su, kamar zata, tsone mishi idon..

Tad'anyi kamar ya furgita.

Yai mata wani 'Sudden smile' daya rikita mata 'yar nutsuwar tata, da k'yar ta samu tace, "Dear wannan kallon fa?

Ya lumshe ido sannan ya bud'e ya kuma zuba su akanta. 

"Always beautiful to me"..

I.. love..you!!

Ya fad'a, wanda motsin leb'enshi kawai ta gani ta gane me yake fad'a..

"Hum, tayi ajiyar zuciya, Ahankali ya mik'o hannunshi babu zato taji ya tab'a mata leb'enta na k'asa da d'an yatsanshi.. "I love your lips..!

Gabanta ya fad'i tsoro ya d'an kamata. Wurin, wuri ne na zirga zirgar jama,ah sannan kuma glass d'in motar ba bak'i bane '(Tinted')

Yaso ya karanci sauyin yanayinta cikin idanunta, amma ta d'an dake har da k'ak'alo mishi sassanyan murmushi, wanda iyakacinshi kan leb'enta..

Wai duk a k'ok'arinta na gudun b'ata mishi rai..πŸ€”


Shikuma yak'i cire hannunshi sai tafiyar tsutsa yake mata a kan leb'e.πŸ˜…

K'asa k'asa take jiyo hayaniyar su Nasreen suna neman su, tayi saurin juyawa d'aya gefen ta wayance, ta kira 'Nasreen d'in.

"Sister Nassy"

Cikin hayaniya Nasreen tace,

"Oh, kun gansu ashe" 

Su hud'u ne suka k'araso suka gaisa da Yusuf,

"Yakake, 

"Am fine,"

"Ya gajiyan biki?

Na'ima tace,

"No I yanzu aka fara.

"Hmm Gud" 

Hafsah taji dad'in yadda ya musu sai wani arahan murmushi yake musu.

Sautin kid'an da aka fara ne yasa suka, gudu.

"Hafsah sai kin taho kinga amfara".

"Okay sai na taho,"

'Nasreen ta lek'a kanta ta cikin glass d'in ta yi wa Hafsah rad'a a kunnenta.

"Ke irin wannan azababben guy haka??..Kin kwaso babban kai fa.

'Suka tafa'

Hafsah taji dad'i an yabi 'Sahibul Khalbi'🀣

Yusuf ya zaro wrapper na dollars ya mik'a ma Na'ima dake ita ce ab'arin da yake take' 

"Take this kunyi lik'i dashi."

"Ta karb'a thank you."

'Suka ce suka tafi suna murna, suna jinjina had'uwarshi.

Acikin hall ana ta shagali,yayin da Hafsah da Yusuf, suke ta tsinkar fure...

Hira tayi hira, Yusuf ya kalleta yace.

Baby, jiya munyi waya da friend enki Basma, and ta fad'amin a week en da zakiyi graduation zatayi birthday, so she asked me to attend."

Taji wani kishi ya toshe mata hanyar numfashinta,.. 

Basma kuma? Awanne dalili??.

"What's wrong with you Baby? Ya fad'a cikin kulawa.

"Hum.. Nothing"!

'Ta fad'a a share'

"Please tell me" ya d'an nuna damuwa.

"Hmm, haba dear, 'mene ya had'aka yin waya da ita..

"Hmm, oh sorry, she just called me, mun gaisa ne fa"..

Ran Hafsah ya k'ara b'aci jin wai Basma ce da kanta ta kirashi..

Ta juya kanta d'aya gefen..

Cikin taushin murya da k'aramin sauti yake mata magana. 

"Please Baby calm down, just forget it.. Babu komai ne fa, I respect her because she is your friend, and she care about me!!..

Tayi saurin juyawa da mamaki afuskarta. 

Cikin b'acin rai ta maimaita.

"Becouse she care about you.. Ok.. Ta fad'a tana girgiza kai.

"Am sorry dear I don't mean it, i mean she care about us"

"Hmm ta fad'a tana shirin bude ficewa daga motar.

Yayi saurin jawota ta dawo ta zauna babu shiri.

Ta juyo tana kallonshi, sai kuma tayi k'asa da ido, da suka had'a ido.

Ya girgiza mata Kai kanshi,

"Please baby.. 

Ahankali taga yasawa motar key, ya ja ta da gudu suka fice.

Zuciyar Mama ta buga dam, ankira ta ne a waya bataji, cikin shine ta fito waje don amsa wayar. Kwatsam kuma sai ta ga mota ta fita da wata mai irin ankon bikin a gaban motar.. Haka kawai zuciyarta ta raya mata kada ace dai Hafsah, ce.

Da k'arfin muryarta ta furta innalillahi,!

Sannan ta kashe wayar.

Cikin rashin sanin abin yi ta koma cikin Hall d'in.

Acan tsakiyar filin rawa ta hango Nasreen tayi gurinta da sauri, ta jawota, har Nasreen d'in ta tsorata.

"Ina Hafsah,?

Tambayar da ta k'wallah mata a kunnenta kenan, wacce tasa hantar cikinta kad'awa,..

Tama rasa k'aryar da zatayi tasan da 'Wijdaan ce (Yayarta) da tuni ta ninke mama a baibai..

Innalillahi, Hafsah ba bata zance koh? 

Ta fad'a a zuciyarta. To me zata cewa Mama,??.. Tana wajen wani suna zance ko kuwa??




Post a Comment

0 Comments