TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 13

 👭❤ *'YAN UWA NA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____13💎



  Da sauri dady ya nufi inda yake


"My son ya akayi kabaro asibitin? Bilkisun ta farfad'o ne?"


"A'a dady har yanzu, bacci nabaro tanayi shine nadawo in karb'i kayayyakin da za'a iya buk'ata don gaskiya dr kamal yace sai ta kwana biyu anga yada jikin nata yayi kafin su bata sallama saboda da alamu tana d'an jin jiki"


"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiun, Allah yasa bawani abunne ya faru da ita ba" Ummi ce tafad'i haka tana mai dafe hannun kujerar dake gefenta saboda jirin da taji yana shirin d'ibarta"


"Ki kwantar da hankalinki Ummi babu abunda zai sami lil sis in sha Allah, suna so ne sai an yimata scanning d'in k'wak'walwar ta anga buguwar da tayi bata haifar mata da wata matsala ba shiyasa zasu d'an rik'emu na kwana biyu"


"Shi kenan kaje ka watsa ruwa kafin nan ta shish shirya kayan"


"A'a dady babu buk'atar hakan yanzu nasan gab take data tashi, Ummi kije ki had'a mani kayan bari inje indawo"


"To Babanah sannu kaji, Allah yayi maka albarka"


"Amin Ummi"


Nan yafita yabar dady zaune akan kujera ya dafe da kansa da alamu har yanzu yana cikin b'acin ran abunda ya faru.


Part d'in mom ya nufa yaci karo dasu Basmah abakin k'ofa d'auke da akwatuna guda biyu biye a bayan mom, wani irin kallo mai d'auke da alamar tambaya ya watsa masu da sauri suka ja baya tare da sakin akwatunan, kai mom ta d'ago cikin b'acin rai tana kallonsa tun daga sama har k'asa


"Dallah matsa kabani wuri in wuce, lpy zaka shigo ka tsoratamun yara haka"


"Yi hak'uri mom amma ina zaki jene?" Ba tare data kallesa ba tace


"Kaje katambayi mahaifinka" sannan taci gaba da tafiyarta, da sauri yasha gabanta


"Don Allah karki tafi mom, ya kike so muyi idan kin tafi, ko kina so ne murasa gatar da muke da ita agareki, ko kad'an bazamu juri rashin kiba, don Allah mom kiyi hak'uri" cigaba da tafiyarta tayi tana fad'in


"Ai sai kaje ita waccan daka fifita akaina ta maye maka gurbina, tabaka gatar da duk kake buk'ata, ammafa ina so kasani yazama dole ka kula da k'annenka kuma kayi masu duk abunda suke so tamkar inanan" cikin muryar kuka yake binta yana cewa


"Kiyi hakuri mom, babu wanda zai iya bamu gatar da takai taki, kefa uwace ita kuma uwa tanada matuk'ar karamci da tausayawa ga 'ya'yanta, inada tabbaci akan babu wacce takaiki ko tafiki awurinmu, don..." Da sauri ta katsesa had'e da d'aga masa hannu


"Ya isa haka..ka kula da 'yan uwanka shine kad'ai abunda zan fad'a maka idan kuma suma kazab'i wasu 'yan uwan akansu basai kayi hakan ba" saurin tarar gabanta ya sakeyi yana hawaye tare da rik'o Bassam dake gefensa


"Mom ki dubesa ki gani yana matuk'ar buk'atar ki a kusa da shi ko ba don muba kiyi hak'uri ki koma don sa, bana son kina fad'in wud'annan maganganun domin babu wanda zai iya maye mana gurbinki aduniya" sosai mom kejin tausayinsa azuciyarta, har ga Allah tana matuk'ar son sa fiye da sauran 'ya'yanta shiyasa duk lokacin da taga hankalinsa ya karkata a wajen Ummi da yaranta takeji tamkar anrabata dashi kallonsa tayi cike da kulawa


"My son!, ai shi mahaifinku bai san da haka ba saboda haka kamar yanda ya buk'aci in tafi  in bar masa gidansa, to zan tafi in yaso ita wacce ya zab'a yasa tamaye maku gurbina" Runtse idanuwansa yayi, sauran hawayen dake lak'e a idanuwansa suna bin layi a fuskarsa, duk daya san cewa komai yafaru laifin mom d'in sane hakan bai hanasa jin d'aci acikin zuciyar saba, sosai yakejin ba dad'i akan hukuncin da mahaifin nasa yayi, hannayensa yasa ya goge hawayen dake kwance akan fuskarsa tare da kallon mom, kafin yace wani abun yaji muryar batool data hango dady na fitowa daga part d'in Ummi shida ita nacewa 


"Ya..ya. Yaya don Allah kabar mom ta tafi ga dady can yafito karya sameta anan, zai iya yimata fiye da abunda yayi mata d'azun" akwatunan hannuwansu ya karb'a yana fad'in


"Shikenan maza ku shiga daga ciki, mom zo mutafi ko?" Gaba d'ayansu suka rungumeta yayinda itako hankalinta nakan dady da Ummi dake tsaye wajen motar da dady ke hawa aranta tana ayyana irin ja'izar (musibar) da zata saka Ummi da duk wani nata aciki, muryar Mahmud ta katse mata tunani dataji yana fad'in "mom mutafi"


Bud'e mata d'aya daga cikin motocin da key d'inta ke hannunsa yayi ta shiga sannan ya zuba akwatunan a bayan boot, wajen su dady ya nufa batare da ya kalli inda yake ba yace 


"Ummi don Allah kuwuce keda dady ya ajiyeki asibitin akwai inda zanje yanzun amma idan nadawo zan sameku acan"


"Shikenan Babanah amma ina mom d'inka zata jene?" Murmushin karfin hali yayi yana kallon yanda dady ya juya bayan sa jin abunda Ummi tafad'a, tabbas yau mom takaisa bango, cikin sanyin murya yace


"Kayi hak'uri" sannan ya nufi motar da mom keciki ya tayar suka fita"


A gaban dady Ummi takoma tana kallon fuskarsa, hannunta tasa ta d'ago fuskar had'e da cewa


"Dadyn yara meka aikata" batare da amsa mata ba ya bud'e gaban gambun motarsa yace


"Shiga muje"


"Ka am samun tambayata mana, ashe bazamu kasan ce masu yadda da k'addara ba, Allah yariga daya tsaro hakan tafaru don me zakayi hakan, kenan idan nima da nake mahaifiyarta tsotsayi yasa hakan tafaru sai kace sai ka hukun tani"


"Ba haka bane, ki kwantar da hankalinki kinsan kowaye ni, bazanyi abunda ba daidai ba, kawai kishiga mota kinji rabba'atul bait?" ya k'arasa maganar yana k'ok'arin dafa kafad'arta, cikin rashin jin dad'i ta d'aga masa hannu.


"Shikenan ya isa, amma kadubi yanayin da Babanah ya shiga, ashe bai cancanci yasamu farinciki daga gareka ba, ita uwa fa uwa ce duk yanda take d'anta bazai tab'a jurewa ganin ta cikin b'acin rai ba, don Allah kasake tunani"


"Rabba'atul bait kenan! Ai kema uwace ya akeyi kike jurewa damuwar da akae saka yaranki dake kanki aciki, ya kamata ak'alla ko sau d'ayane innuna mata kuskuren da take aikatawa, ina so mugudu tare kuma mutsira tare don haka dole tasan tayi kuskure beside wlh ba abunda ya faru akan Bilkisu yasa nace ta tafi ba, ta matuk'ar yin gangancine cikin kalaman da tayi mani wannan dalilin yasa nayi mata wannan hukunci" jin yanda yayi rantsuwa yasa jikinta yayi sanyi, tashiga cikin motar had'e da cewa 


"Allah ya sawak'e" 


A b'angaren mom kuwa ta madibi Mahmud ke kallonta kafin yace


"Mom ina zan kaiki?"


"Gidan mahaifina mana"


"A'a mom kituna koma da daraja irin ta papi, anya kina ganin zuwanki bazai tab'a masa kima ba, yakamata ace izuwa yanzu kinfitar da duk wani abu da kikeji aranki gameda Ummi, yanzu meye dad'in wannan abu da yafaru tsakaninki da dady agaban yara? Abunda tun kuna da k'uruciya bai tab'a faruwa ba sai yanzu da kuka manyanta" 


"Tabbas kuma wannan abun ba abunda ya k'ara mani illa tsana da k'iyayyar matar ubanka, saboda adalilinta komai ya faru, wlh wlh matuk'ar inada rayuwa saina salwantar da rayuwar Aisha zuriarta" da k'arfi ya taka burki yana fad'in


"Wa'iya zubillahi meye haka kike fad'a mom?"




Post a Comment

0 Comments